Showing 75001 words to 78000 words out of 557259 words
koresu?......yace bashi dashi?.....yace bazaya bada ba?......wannan mashkur din yau shike bada damar a nemi ko nawa ne zai iya mallaka mata bisa rashin sanin WACECE ITA?.
Hakan tamkar wata dama ce a gareta kenan da zata samu dukka kudaden da takeso......amma bisa sharadin sadaukar da abinda yafi komai mutunci a tare da ita?.
Koda ta saba ko tana da damar accepting masa abinda yazo dashi.......tabbas ba zata lamunce ba......tanaso ta debi kudadensa ta hanyar data saba azabtar da sauran.......tanaso ta debesu ta hanyar da zaiji ciwon da bazai kankaru ba a zuciyarsa.......tanaso ta debi kudin da zai tsaye masa a rai......yayi masa ciwo fiye da yadda rayuwa da zukatan matan da ya fadawa mutuncinsu sukayi musu ciwo......tanason bashi darasi me girma a rayuwa.......tanason shima ya girgiza girgizar da zata tsaida masa komai na rayuwarsa cakkkkk koda ba tsaiwa bace ta har abada......to amma kuma ta sani.......babban plan da yake buqatar nutsuwa da tsare tsare masu yawa. Don haka da safiyar washegari ta tura JIB wani saqon da sunan mutum biyu.
Tana tsaye tana shan ruwan dumin da takesha duk safiya kafin shigarta wanka saqo ya shigo wayarta. Sanda ta duba sai ta samu alert na kudi daga wajen ya'aqoub. Five hundred thousand ce,sai ta gyada kai a hankali tana sakin murmushin takaici. Don kyauta yana da kyauta ya'aqoub ba daga baya ba......abinda bata da yaqini shine haka yake a cikin gidansa?,ko shima fankan fayau ne?.
Saqon godiya ta tura masa a gajarce,ta aje wayar tana shirin wucewa wanka wani saqon ya sake shigowa
"Patiently waiting for you" Share saqon tayi hade da sauran. Tasan me saqonsa ke nufi a gajarce. Kowacce safiya izina ce a gareta,kowacce rana kowanne sati da kuma kowanne wata cikin rayuwarta yana bude mata babi na abubuwa da yawa cikin rayuwarta. Waishin akwai ragowar NAGARTATTUN MAZA kuwa?,tambayar da kullum idan ta yiwa kanta ita take bawa kanta da kanta amsa da BABU.
Kanta tsaye take takawa cikin tsakar gidan nasu ba tare data daga kai ba bare ta lura da waye a hagunta ko damanta?. Ba tare data damu da kallon nan nasu data tabbatar a safiyar yau zai ninka ko ma ya canza salo saboda abinda ya faru a jiya.
Dab da zata sanya qafarta a qofar toilet din nasu dake da sassa biyu bathroom da toilet ta jiyo muryarsa yana koda sallama. Sallamar da muddin ya yita duk wani dake da hadin kai dashi take masa dadi......duk wani wanda yake da qulli dashi Kuma yake neman yin ta kansa,mutane kuma kamar ita sukejin kamar su turashi ya koma muhallin da ya fito.
Koda taso tayi shigewarta toilet din ta tabbatar sai ya ganta don ya iso dab da wajen. Don haka ta tsaya a nutse tana bude toilet din ta hanyar murza handle,abinda ya bashi damar qarasa shigowa farfajiyar tsakar gidan.
Da ita ya fara hada idanu kamar yadda nata idanun suka zube a fuskarsa. Kamanni dai da mahaifinta har kullum sune,bata kuma fasa ganinsu shimfide a fuskarsa,saidai nisan tazarar halayya da dabi'un sun kai girman tazarar dake tsakanin sama da qasa.
"Yauwa alhamdulillah......ai gwara dana sameki cikin gidan.....zuwan dama naki ne" Kallonsa kawai tayi ba tare da wani mamaki ba,dama wanne zuwa ne zaiyi gidan ba nata ba?,koda yayi zuwan daba nata ba to lallai daga qarshe sai ya zama nata ko kuma ya hado da ita a abinda bai zama damuwarta bama bare y shafeta. Amma tun a jiya tasan tabbas dama zayazo,shi yasa taso su fice kitso da wuri yazo ya taras da sararinsu kawai.
"Ina kwana kawu?" Ta fada cikin girman nan da bata fasa bashi shi kaman yadda kowa cikin gidan ke bashi duk kuwa da farin sanin da tayi na waye shi?,sanin da kaf gidan tayi yaqinin ba wanda ya masa shi......sanin da a qa'ida ya cancanci ta rainashi......amma sai kuma batayi hakan ba.......sanin da ko yaushe ta tunashi dashi take jin kaico da bacin rai da rashin sanin son ganin gilmawarsa.
"Lafiya qalau......idan kin baro bandakin ki sameni a dakin bibo" Ya fada yana saba babbar rigarsa yana wucewa ciki tare da jaddada sallamarsa.
Da kallon takaici ta bishi,tasan dama zaa rina,ba wani abu da zai fari cikin gidan ya kwana ya hhantse baije kunnuwansa ba.......yana kuma zuwa kunnuwan nasa ne ta hanya guda daya rak wato BIBO. Idanma akwai ta biyunta to bata bayyana ba tukunna. Cikin rashin damuwa da lamuransu gaba dayansu ta kada kanta ta wuce bandakin.
Babu wani abu da zai sanyata gaggawa a zuwa kiran data tabbatar babu alkhairi sam sam a tare dashi. Wannan ya sanya ta kammala wankanta a nutse,takuma tsaya gaban madubi ta shirya tsaf kamar yadda ta saba. Tun bata kammala ba ya aiko kiranta ya kusa sau biyar. Ana shidan ta tsaida nadra da taji tana gaya musu cewan kaya take sanyawa
"Kace gani nan zuwa" Ta fadima usman daya aiko. Rigar lace tayi niyyar sakawa,don haka ta fara sanya 'yar cikin rigar ta yane kanta da mayafi ta zura slippers dinta tana cewa
"Ku kammala shiryawa ina dawowa zamu wuce" Ta qarasa fada tana sanya qafafunta a waje,huda kuma ta bita da kallo. Sam bataso ace sabreen din taje da kanta kamar yadda kawu ya buqata ba,ta tabbatar da cewa ba wai wani abun arziqi zai aiwatar ba face tsantsar son zuciya da son rai kamar yadda suka saba. Ba wani lokaci da abu irin haka zai taso cikin gidan ya zamana anyi hukunci cikin adalci da sanin ya kamata.
Hankali kwance ta daga labulen dakin bibo gami da sallama. Su uku ne cikin falon,kawu bibo sai hadiyya dake zaune saman daya daga cikin kujerun. Qafarta daya saman daya tana kadata a hankali. Tako ina tana jin kishin wanzuwar komai dake tattare da sabreen din. Kowanne abu tana yinsa ne don kawai ta samu daqile sabreen din. Ba haka takeso ta bude idanuwa ta ganta ba. Wani qaqqarfan abu ya dasu a ranta game da sabreen din.
A haka mutane ke raina matakin da take kai.....suke mata kallon wadda ke tafiya bisa baragurbin bigire......amma ita a nata idanun ta sani cewa sabreen din tayi mata wani irin nisan tazara me tarin yawa. Bataso ta ganta a haka.....ba'a haka take da muradin ganinta ba,tana son ta sauya daga matsayin da take kai a yanzun,shine abu daya da zai gamsar da ita.....
*SU SAKE DAWO MUKU DA WASU SABBIN LABARAI*
*_BAYAN WASAN DA AKA BUGA GA WANI SABON WASAN_*
*_MIQAQQIYAR TAFIYAR NISHADI_*
*_KAFATAWA DA ZAFAFAN MUHAWARA_*
*_LABARAI MASU DAURE KAI DA SANYA NISHADI A CIKIN ZUKATAN MASU KARATU_*
*ZAFAFA BIYAR*
*_MASUBURBUDAR LABARAI MASU CIKE DA HIKIMA DA DEBE KEWA DA WASA TUNANI TARE DA TSUMA ME KARATU DA TSUMAMMIYA KUMA TSAFTATACCIYAR SOYAYYA_*
*Hanzarta shiga ayarin ZAFAFA FAMILY(WATO IYALAN ZAFAFA DA BASA GAJIYA DA KASANCEWA DA SU*
_TA HANYAR SHIGA RUKUNIN MASU SIYAN LITATTAFANSU KAMAR HAKA_
_QIRJIN ME HANKALI Miss xoxo_
_K'ALBIM Mamuhghee_
_AJIYA A DUHU Billynabdul_
_DUNIYATA Huguma_
_Dukka qunshin litattafan daga farko har qarshensu_
*hudu 2k*
*uku 1500*
*Biyu 1k*
*Daya 500*
_YADDA ZAKU BIYA IDAN KATI NE:_
*09032345899 KATIN MTN, IDAN AN TURA SHEDAR MA NUMBER ZAA TURAWA*
*IDAN BANKI NE A TURA SHEDA ZUWA GA*
*09033181070*
*BANK NAME/SUNAN BANKI: ACCESS BANK*
*ACCOUNT NUMBER/LAMBAR ASUSUN BANKI: 0022419171*
*ACOUNT NAME/SUNAN DA KE ASUSUN BANKI:MARYAM SANI GUMMI*
*AL'UMMAR MAQWAFCIYAR QASATA NIJER KUWA*π³πͺπ³πͺ
89825722
Nousaiba lawali maradi
1000cf
*_Madalla da masoyan ZAFAFA BIYAR_*
*_MADALLA DA KASANCEWARKU TARE DASU_*π₯°π₯°
*D U N I Y A T A*
*_H U G U M A_*
*_Arewabooks:@Huguma_*
https://www.arewabooks.com/book?id=675041625c3130f457519997
________________________
PAGE 42
Janye dubanta tayi daga kan hadiyya,sai ta nemi hannun kujerar dake daga bakin qofa ta zauna akai,wayarta a hannunta tana qoqarin sakata a silent. Ta manta yaushe ne lokaci na qarshe data shigo wannan dakin,bama shi ba,dukkan wani daki dake cikin gidan ba muhallin shigarta bane.
"To da kika shigo kikayi mana derere saman kujera ai sai ki sauko ko?" Muryar bibo ta rasa kunnenta. Dauke dubanta tayi daga saman wayar ta aza a fuskarta. Abubuwanta sun fara mata nauyi akai,tanason ta fara shige huruminta. Tana ganin kima da martabarta a matsayinta na macen data taba kasancewa mata a wajen mahaifinta,amma ta lura da sam sam bata kula da wannan.
Dauke idanunta tayi daga kan bibo din,tana ji a ranta lokaci ya kusa da zata sassauta wannan girma da martabar da take bata,tunda har ita din ta gaza riqo dasu yadda ya kamata
"Gani" Ta fadi kai tsaye tana duban kawun. Zamansa ya gyara yana wani hakimcewa. Jira yake su kammala da maganar da aka tattagoshi a kanta ya gabatar da nasa batun wanda shine yafi damunsa
"Yanzu ke......wani irin baqin hali gareki ne?.....kin fita ZAKKA ke kadai?,kin addabi kowa kin damu kowa?,a gidan nan kaf babu wanda yake da matsala sai ke?" Duk da tasan qarshen zancan,ta kuma san abinda ya sanyashi debo dogon zance har haka amma sai maganganun nasa suka bata mamaki. Banda tsabar rashin son zaman lafiya na mutanen gidan......a yanayin yadda ta tsara rayuwarta dana 'yan uwanta,ya kamata ace tana cikin sahun jerin mutanen da za'a mance da wanzuwarsu cikin gidan. Zaka jima baka ga gilmawarta ba,zaka jima baka ganta zaune a farfajiya ko filin tsakar gidansu ba.....zaka jima baka ganta a tsaye tana magana da kowa ba,to wai shin me ta tsarewa bibo da ire irenta cikin gidan?.
"Wani abu akace maka ya faru?" Tayi tambayar tana tsareshi da idanu. Fada yakeso rufeta dashi kamar yadda bibo ke buqata.....amma kuma yana duba da tunanin kada hakan ya sarayar da samuwar tashi buqatar.
"Yo har sai ance miki ma wani abu ya faru cikin gidan nan banda raini?.....me ya kaiku shiga hurumin yarinyar nan banda neman tada zaune tsaye?,yarinyar da babu abinda ta sanya a gaba banda karatunta?,inajin kaf cikin yaran marigayi babu kamarta ko akwai?" Ya qarashe tambayar yana maida dubansa kan bibo da taketa cika tana batsewa. Dukka salon fadan daya dauko babu wanda yayi mata
"Ina fa?.....mu irin karatu ne,kuma karatu shine a gabanmu" Ta fada tana gyara daurin dankwalinta.
Da idanu kawai take binsu tamkar bata fahimtar koda kalma daya daga cikin maganganunsa,har zuwa sanda yakai qarshe ya kuma jona da tambayar bayyana fifiko me yawa tsakaninsu da hadiyya.
Tsam ta miqe tana duban kawun
"An gama?,inaso na fita ne" Ta fadi kai tsaye ba tare da tayi duba ga sashen da bibo ke zaune ba. Dukkaninsu idanu suka zuba mata su ukun,yayin data juya a hankali tana nufar qofa ganin kawun bai iya cewa komai da ita ba.
Cikin tsananin jin zafi gami da yunqurowar wani boyayyen zazzafan kishinta a kanta ta sauke qafafunta tana aje wayar hannunta gefe
"Kin gani ko bibo?,ai dama na gaya miki......wallahi bata kunya ko shakkar kowa......ni nasan kawu ba matakin da zai iya dauka a kai....."
"Ke!.....yimin shuru,rashin kunya zakiyimin?" Ya fada cikin fadan nan nasa yana rarraba idanu. A duniya idan akwai abinda ya tsana itace kalmar YA KASA KO YA GAZA
"Aah dakata sule......" Bibo ta fada tana daga masa hannunta daidai sanda kunnuwan sabreen sukayi nisa daga jin cecekucensu.
"rashin kunya har takai wadda waccen figaggiyar gantalalliyar yarinyar tayi maka.....tambadaddiya da ka kasa saitota cikin yaran dan uwanka......kaf dinsu yara mata goma sha tara amma ita daya ta fita ZAKKA?,to kada kazo kace zaka zaqemin akan yarinya......me laifi daban wanda za'a huce a kansa daban?". Ransa ya baci sosai,don shi din irin mutanen nan ne da basa son raini ko wargi ko qanqani. Banda ma bibo din da taga wallensa......kaf yaran gidan tsoro da shakkarsa suke idan ka cire SABREEN din
"Ke hajara......dakata,hawainiyarki ta kiyayi ramata......kibar ganin ina daka ta taki.....wallahi ina nan yadda kika sanni......kawai ina duba wasu abubuwa ne nake rama miki halacci da halacci......amma tunda iskancin naki a kaina zai sauka a gaban qaramar yarinya irin wannan......to shikenan......ni na zare hannuna daga sha'aninki cikin gidan nan......" Ya fada yana miqewa cikin hargagi gami da kakkabe babbar rigarsa.
"Haba sule.....zauna mana kaji......ba haka nake nufi ba.....ni dadina dakai wannan masifar taka da jarabar". Tsaiwa yayi yana hade rai gami da dubanta
"Ba haka kike nufi ba hajara gayamin abinda kike nufi". Sai kuma ya waiwaya sashen da hadiyya ke zaune
"Tashi ki bawa mutane guri kin zauna kina raba idanu a gabansu" Ya fadi mata cikin tsawa kamar zaibi ta kanta. Wayarta ta dauka sumi sumi tana yin hanyar shigewa bedroom din bibo din,qasan ranta cunkushe fal da baqinciki. Baiyi mata yadda takeso ba,ba kuma haka takeso ya yiwa SABREEN ba. Batasan dame sabreen din ta fisu ba da har tauraruwarta tafi tasu haske cikin gidan,duk da tayi yaqinin ko meye sabreen din zata juya ta kuma nunawa duniya shi to ba shakka ya samu ne daga dattin ZINA da kuma dattin BARIKI. Ba abu mafi daure kai irin mazan dake karakaina a kanta tamkar su sadaukar mata da rayukansu......amma ta gaza cafke koda guda daya ta maisheshi mijin aure?.
"Mazan bariki dama suna auren macen da suka hadu da ita a bariki?,ai saidai su tsotseta tas.....su musaya wannan zaqin da gardin da suka samu daga gareta da 'yan kudaden da zasuyita mata barinsa......daga sanda buqata kuma ta biya su tattarata su watsar su qara gaba zu zabi wata". Sai ta tuna maganar da sukayi taba yi da bibo wadda ke kamaceceniya da kalmomin maleeka roommate dinta. Juyi tayi kadan saman gadon,tana da burika masu tarin yawa akan karatunta,wannan ya sanya ta sadaukar da rayuwarka akanshi. Tana so ta ganta tana fantamawa,tanason ta ganta tana haskawa tamkar sabreen da dukkan wani alatu da jin dadi......tanaso taga maza suna mutuwa a kanta sama da sabreen......amma dukka ta hanyar karatunta da kyawun sura da Allah ya bata. Tana cikin sahun jerin farko farko da 'ya'ya masu kyau a gidan......ta tabbata ko wannan ya isheta jari wajen zaben kalar mijin da take buri da muradi idan aka qara da karatunta da takesa ran kammalashi ta kuma riqi kyakkyawan certificate mafi girman daraja a idanun mutane.
Ta samesu a zaune sun gama shiryawa sanda ta koma dakin. Kai tsaye ta wuce can ciki ta jawo rigarta ta sama ta zura,ta hada igiyoyin ta daureta ta zauna dai dai jikinta,abinda ya bawa rigar daman fidda kyakkyawan shape din nan nata da ba kasafai ya fiya bayyana ba saboda ita din ba ma'abociyar sanya damammun kaya bace. Sai data sake goge jikinta da sassanyan oil perfume dinta sannan ta fara rolling dan kwalinta saman kanta idanunta akan fuskarta data bayyana tarwai ta cikin madubin.
Maganganunsu taketa tattaunawa ita da zuciyarta. Dabiar kawun dama bibo gaba daya. Yadda tsahon lokaci da zamani bai sanya kowannensu ya sauya ba. Ranta da zuciyarta duka ba dadi. Ta iya rigima tuburan idan taso......ta iya surutu har kayi zaton ma ba ita bace......hakanan ta iya fada musu da kuma taurin kai......amma daga sanda rayuwa ta soma Karantar da ita wasu darussa sai ta gane basu take buqata ba,don haka ta tattarasu ta aje a gefe.
Jakar da zata dace da shigar da kuma yanayin ta dauko. Kaman yadda ta saba duba jaka kafin takai ga fita da ita haka ma wanna,a nan taci karo da kudaden da mashkur ya bata. Maidasu jakar tayi da zummar damqawa suraj su,daidai lokacin haneefa ta shigo tana kiranta
"Kizo inji kawu sule"
"Kawu kuma?" Ta tambayi haneefan tana duban idanunta
"Eh" Kamar ba zata mata komai ba,sai ta fesar da iska daga bakinta. Tasan dukkan abinda zai sanyashi shigowa wajenta baya taba zame mata abun alkhairi face tarin matsaloli fadace fadace da fadin maganganu barkatai da zasu yamutsa DUNIYARTA tana zaune salin alin
"Kice masa gani nan" Ta bata amsa tana juyawa sashen ajiye takalmanta ta fara dubawa. Takalma ne kala kala masu mabanbantan shape kudi da kuma kaloli. Wani adadi ne me yawa ma'ajiyar takalman taci,wanda dukkansu idan ka kalla babu takalmin qasa sa dubu goma.
A duk sanda ta kalli sashen suturar data mallaka a yanzu,a karan kanta mamakinta yana sake ninkuwa ne. Suturu na alfarmar da yaran masu hannu da shuni ke taqamar mallaka ko jin isar cewa sun kai. Daya daga ciki ta zaro,ta aje a qasa ta zura a qafafunta sannan ta debi wayoyinta ta jefa a jaka tayi hanyar fita tana ji a ranta ko sisi a yau din bazai samu daga wajenta ba muddin abinda ya shigo dashi kenan.
*SU SAKE DAWO MUKU DA WASU SABBIN LABARAI*
*_BAYAN WASAN DA AKA BUGA GA WANI SABON WASAN_*
*_MIQAQQIYAR TAFIYAR NISHADI_*
*_KAFATAWA DA ZAFAFAN MUHAWARA_*
*_LABARAI MASU DAURE KAI DA SANYA NISHADI A CIKIN ZUKATAN MASU KARATU_*
*ZAFAFA BIYAR*
*_MASUBURBUDAR LABARAI MASU CIKE DA HIKIMA DA DEBE KEWA DA WASA TUNANI TARE DA TSUMA ME KARATU DA TSUMAMMIYA KUMA TSAFTATACCIYAR SOYAYYA_*
*Hanzarta shiga ayarin ZAFAFA FAMILY(WATO IYALAN ZAFAFA DA BASA GAJIYA DA KASANCEWA DA SU*
_TA HANYAR SHIGA RUKUNIN MASU SIYAN LITATTAFANSU KAMAR HAKA_
_QIRJIN ME HANKALI Miss xoxo_
_K'ALBIM Mamuhghee_
_AJIYA A DUHU Billynabdul_
_DUNIYATA Huguma_
_Dukka qunshin litattafan daga farko har qarshensu_
*hudu 2k*
*uku 1500*
*Biyu 1k*
*Daya 500*
_YADDA ZAKU BIYA IDAN KATI NE:_
*09032345899 KATIN MTN, IDAN AN TURA SHEDAR MA NUMBER