Showing 420001 words to 423000 words out of 557259 words

Chapter 141 - πƒπ”ππˆπ˜ATA BOOK1 AND 2 HAUSA NOVEL

HUGUMA   

03 Nov 2025

3488

tabbatar bashi da wani gata daya rage masa saishi daya......ashe akwai wata halitta daban a gefe dake tsananin kulawa da rayuka har guda uku a matsayinta na diya mace?.

Daya bayan daya suka sauke board din,su dinne.....huda nadra da haneefa......sune amma fuskokinsu sun canza daga su hudan data sani watannin baya sun koma wasu mutane na daban da kamanninsu ke nuna zallar jin dadi nutsuwa da kwanciyar hankali.

Jikinta duka ya dauki rawa,fuskarta ta gauraya da kalolin emotions har guda biyu,dariya da kuma kuka,ta soma qoqarin kwasa da gudu don ta cimmasu,tana ganin kamar tafiya tayi kadan ta kaita garesu. Caraf yayi ya riqe hannunta.

"Bi a hankali......mrs muhammad jadda......bani da tabbacin babu baby ne a jikin ki,still baki da cikakken lafiya......muje na rakaki.....su dinne,zaki cimmasu cikin salama da nutsuwa".

" Kai....kain...." Bakinta yana rawa tanason tambaya da samun tabbaci.

"Shshssh..... Muje" Ya fada yana mata nuni da lumsassun idanunsa.


_Allah sarki....dan uwa rabin jiki_πŸ₯Ή



*_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_*
08187255862


𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀
_Zafafabiyar_

ΜΆBΜΆOΜΆOΜΆK ΜΆ2

β±§Ι„β‚²Ι„β‚₯β‚³

π™‹π˜Όπ™‚π™€ 111



111


Tun kafin ta qarasa garesu hawaye sun gama wanke mata fuskarta,taqi dauke idanunta daga kansu koda na second guda,tana ganin kamar idan tayi hakan zasu bace mata kafin ta sake bude idanun nata.

Suma basu iya jira ta qaraso garesu ba,da wani irin sauri suka tunkarota kowa yana qoqarin fara isa wajenta. Gudun nan daya hanata batasan ta yishi ba sai da ta jita cikin jikinsu,dukkaninsu su ukun qoqari take a lokaci guda ta samu damar rungume kowa. Bata fahimci kuka sukeyi ba sai da suka zube duka a jikinta suka sulale qasa duka har ita din. Sheshsheqa sosai sukeyi kowanne da sunanta a bakinsa. Wani irin sautin kuka ne me taba zukata,kukan dake cike da kewa da qaunar juna irin wadda asalin soyayyar 'yan uwantaka take bayarwa. Ko fu'ad a wannan karon baya yaja ya tsaya yana rungume da hannayensa,kallonsu kawai yakeyi baiyi yunqurin yi ko cewa komai ba,saboda yasan wanne irin ciwo ne zukata sukeji a irin wannan lokacin.

Ta rasa sunan wa zata fara ambata?,sai kuma ta saka hannu ta fara dago haneefa auta.

Fuskar autan ta sake cika sosai,duk wani kamanninta da ita sun sake bayyana,tayi wani irin haske wanda da alama shine asalin color din fatarta.

"Auta......auta kece?" Ta fada wani kukan farinciki yana sake tsinke mata. Kai haneefa ta gyada tana dariya da maqalallun hawaye akan fuskarta.

"Nice adda......adda kin qara girma.....adda kin zama balarabiya" Haneefa ta fadi tana shafa hannun sabreen dake riqe da nata hannun. Qaramin dariya daya taho da hawaye ta saki tana maida kallonta ga huda.

Hudanta ta sake zama budurwa sosai,abun abun mamaki kaman wadanda aka saka famfo ake hurasu. Kamarsu itama ya sake fita,duk da baikai kamannin dake fuskar haneefa ba.

"Adda......ban zaci zamu sake ganinki da wuri ba"

"Nima haka adda......" Muryar nadra ta sanyata waiwayawa. Itama nadra din kaman sauran,saidai nata kamannin da ummenta ne suka fito sak kaman an tsaga kara,abinda ya raunata zuciyar sabreen sosai ta miqawa nadra hannu. Ba musu ta dora nata hannun akan na sabreen din suna duban juna.

"Nadra?....ya akayi kukayi irin wannan girman?,me kuke ci?"

"Komai me kyau adda.....komai mai dadi hamma ya tanadar mana,komai da zamuyi amfani dashi muci ko musha yasha banban dana dubban mutane adda"

"Hamma?" Ta tambaya a mamakance,sai huda ta gyada mata kai tana duban fu'ad dake nesa kadan dasu. Kanta ta daga ta waiwaya zuwa inda yake tsayen,zuwa sannan tare da saddiq suke tsaye,batasan maganar da sukeyi ba amma taga yana miqawa saddiq din wani card.

"Hammanki adda" Haneefa ta bata tabbaci. Maganan data sanyata dauke dubanta daga kanshi zuwa kansu. Kai huda ta gyada mata still tana qara tabbatar mata.

"Ya Allahu ya salamu.....when......and how?" Ta tambayi kanta. Duka yaushe yayi hakan?,duka yaushe yasan da yaran?,yaushe yasan inda suke?,yaushe ya shirya komai?. Ko yawan using da wannan na'urar da yake sanda suna muraaka suit yana da alaqa da shirinsa akan haka?,take taji amsar tambayar tazo mata.

Wani kakkaifan abu a kansa taji ya huda zuciyarta,ta lumshe idanunta tana jin yadda yake kwarara cikin kowanne sashe na zuciyarta dama gangar jikinta.

"Muhammad fu'ad jadda" Sunansa kadai ya dinga amsa kuwa cikin kunnuwanta.

"Amma kun saba alqawari.....kun karya yarjejeniya sister" Muryar nan tasa dake cike da tarin nutsuwa ta ratsa rufaffun idanunta,sanda ta budesu sautin murmushin huda ya sauka a kunnenta.

"Wallahi hamma itace.....adda ne ta fara sakamu kuka" Ta amsa masa tana miqewa gami da riqe dariyarta. Idanunta ta bude fes saita samu tattausan tafin hannunsa gaban fuskarta yana miqo mata shi.

"Next time sai naci tararku idan kuka sake sanyamin mata kuka......get up my world" Ya fada yana duqawa kadan yasa hannuwansa yana daga kafadarta.

Wani sanyi taji yana ratsa sannan jikinta,ta ware idonta a kansa sanda yake miqar da ita tsaye. Fuskarsa fresh kuma normal kaman baiyi wani abu ba,ta laluba labbanta zuciyarta dama kwanyarta gaba daya,tanason zaqulo kalaman da suka dace tace dashi wani abu amma ta rasa.

Gyara mata veil dinta yakeyi yana sake rufe mata jikinta gami da jan hannun abayarnata

"Wannan kallon.......bakison zuciyata ta huta hala?" Ya tambayeta yana balle mata button guda daya daya zame na abayarta. Idanunta sunyi raurau sosai sun cika da hawaye,ko sau daya so take ya kalleta......koda na second daya ne wataqila zaifi fahimtar girma da martabar abinda yayi mata,don ta tabbatar kalaman baki sunyi qanqanta su isar da abinda takeson isarwar,saidai yaqi ya kalletan har sai daya gama sannan ya zube mata fararen idanunsa. Wani abune da yake yawan bata mamaki,a iya mazan data taba kallon idanunsu ba zata iya tuna mutum daya da idanunshi suke da haske haka ba......koda kwatankwacin nasa kuwa.

"Akwai wani abun?" Ya sake tambayarta yana kallonta. Labbanta ta motsa amma sai ya saka yatsunsa biyu ya b'ame mata su.

"No need......bana son godiyarki ko kadan......it's my duty......aikina ne na baki duk wani abu da zai baki farinciki......haqqina ne samar miki da duk wani abu da zai baki nutsuwar zuciya data gangar jiki......aikina ne.....dole na ne na matso miki da dukka farincikinki kusa dake.....har yanzu jikinki da dumi,mu qarasa" Ya fadi yana riqe hannunta cikin nasa sannan ya kira haneefa ya saka mata ita a gefenta,ya kira huda ya sakata a daya gefen,yaja nadra baya sukabisu a baya yana mata magana qasa qasa wadda sabreen batasan me yake tambayarta ba.

Tuni ta kame a owners corner,tanason ta sake tabbatar da duk wani motsi da xai gayawa kowa ita din isashiya ce. A bude tasa abar mata qofofin lafiyayyar motar,tana shaqar iska d'ai d'ai tana ratsata,tana jin qofofin abubuwan daya kamata ta aiwatar kaman suna bude mata.

Tana jin tsaiwar anni a daura da ita,ita da amna da musaddiq da take jira su samu xama sosai tayi masa iyakoki da lamuran annin. Batason duk wani abu da zai ci gaba da sanya kusanci tsakaninsa da yarinyar can me kama da uwarta,zata iya kowanne kalar hauka xata kuma iya cinye komai ta daure har ta gama da matsalar amma banda alaqa tsakaninsa da amna din,don yanzun haka sautin dariyarsa da yarinyar tana jinsa har tsakiyar kanta.

"Musaddiq" Ta kirayeshi tana leqo fuskarta daga motar. Sam yana mancewa da wani warning na maamah din,kiranta ya dawo dashi cikin hayyacinsa,ya amsa mata a nutse sannan ya dubi anni. Da ido ta masa alaman yaje ya amsa kiran mamarshi

"Ina zuwa" Ya fadi qasa qasa yana takawa zuwa inda take.

Kallo take qare masa tun daga sama har qasa,ta kowanne fanni abun babu sauqi ne wai?,wai me yasa sabbin matsaloli suke sake kunno mata kai?.

"Anya ka samu isashen ilimin sanin darajar uwa kuwa?.....a ina ka taba ganin mutum yabar wajibinsa ya dauki mustahabbi?" Kasa cewa komai yayi,bayason ya fadi wani abu da zata tunzura taci gaba da zazzago maganganun da ya tabbatar anni tana ji,don muryarta a bude take magana ko wanda ke nesa zai iya jin sautinta,kasancewar garin gari ne maras hayaniya sam sam,albarkacin wanda yake kwance cikinta.

"To tunda nayi maka a daki bakaji ba......bari nayi maka a gaban kowa da kowa......ni mariya ahmad.......indai nice nayi cikinka watanni tara na haifeka.....na haramta maka zuri'ar hamza kibiya da ameenatu haramci na har abada.....idan ka sake nuna wani abu makamancin haka kuma ban yafe maka ba".

Idanu fu'ad dake qarasowa wajen ya runtse maganar tana hudashi,duk wani motsi nata qara bashi yaqini yake a kanta,tana sake haska mishi kanta da kanta tana fadada zargin da xai iya cewa qiris ya kusa zama tabbaci.

".......kaji na gay......" Ta dora da maganar da takeyi saidai kuma kasa qarasawa tayi sakamakon qwarewa da tayi da yawun bakinta.

Bawai tayi qwarewar Allah da annabi bane.....ba kuma ta qware bane haka siddan,abinda idanunta suka hasko mata shi ya janyo mata qwarewar ya kuma zarce mata da wani matsanancin tari daya sanya idanunta firfitowa waje.

Fu'ad yana takewa sabreen da qannenta baya kaman wani dan aikinsu......mutumin da shi kansa garada ne masu yawa suke gadinsa....... Saukar idanunta akansu huda ya qarasa dauke duk wata wuta ta jikinta na wasu sakanni. Ta ina yaran suka bullo?,daga wacce shiyya ko jaha?,ko duk cikin zallar iya barikinne na yarinyar?. To waima da kudin ubanwa sukazo madeena?,waye ya dauki nauyinsu?. Indai amsar dukanta FU'AD ne to lallai ta zaunar dashi ta karanta masa komai kenan a kanta?. Indai haka ne ai la shakka zataga wani sauyi ko alamu saman fuskarsa,to amma bataga komai ba.....wai ya abun yake?.

Tarin tulin tambayoyin da suka hana tarin lafawa da wuri,har sai da taji maqogoronta ya fara zafi,ta karbi ruwan da musaddiq yake bata ta kurba still idanunta akan yaran. A yadda suka rabu dasu rabuwar qarshe......bata nuna musu duk wani plan nata ba,tayi qoqarim basu gata da kulawa,a yanzun tana zaton zasu iso gurinta cikin fara'a da girmamawa ne kaman yadda yake a baya,saidai yanzun ga tarin mamakinta sun gaidata ne a tare......irin gaisuwar da zaka yiwa baquwar fuskar da baka taba ganinta ba. Bata iya amsa musu ba saboda mamakin da ya ciyota,ta bisu da idanu sanda suke motsawa gaba wajen anni suna gaidata.

"Ma sha Allah......aah 'yammata,lafiya alhmdlh,da alama kun rigamu sauke taku umrar.....nasan halin saddiqu da kyau,bazai bari ku zauna ba dama.......ga photocopy din takwara ameenatu......ma sha Allah,Allah ya yiwa rayuwa albarka" Dukka muryoyin anni suka dinga dukan kunnenta sanda suke haraman barin wajen bayan rarraba motar da kowa zai hau.

Madeena kusan ta zame masa muhalli,don haka yana da gidaje nasa na qashin kansa kyawawa har guda biyu. Ba wani gari a duniya da yake jin nutsuwar da ko jaririn dake cikin mahaifiyarsa baikaishi samunta ba irin madeena,ta biyunta makka,to amma yanzun saboda yana buqatar sabreen din ta huta sosai,sai yasa aka kama musu amenities a intercontinental Darr alhijra,saboda yafi kusa da masjid annabawi.

Duk yadda yaso ya kasance a motarsu sabreen din amma sai ya dage mata qafa,don wataqila akwai maganganu da suka shafesu da zasuyi a tsakaninsu daya kasance sirrinsu ne,don haka ya tura saddiq motar maamah su tafi tare,amna da anni,shi kuma ya karbi key da kansa ya kira musaddiq

"Shiga muje" Ya fada yana shiga mazaunin driver ya tayar da motar suna fita a nutse. Bayajin xai iya barin wadannan sakannin su wuce maganan dake ransa yana cizonsa,shi yasa da zafi zafi ya nemi kebewa da musaddiq din.

Shuru ya ratsa tsakaninsu har zuwa sanda suka dauki hanyar intercontinental,muryar hamman nasa ta masa saukar ba zata.

"Musaddiq"

"Na'am hamma" Ya amsa a sanyaye har yanzu muryar maamah tana bugun tunaninsa.

"Kanason amna?" Tambayar da bai bata tsammani ba ta fita daga bakin hamman nasa. Har wani firgicewa yaji yayi,yaji kaman baiji abinda fu'ad ya fada daidai ba.

"Nn...na'am hamma?"

"Nace kana son amna?" Ya sake tambayarsa idanunsa nakan titi yana sauraren amsarsa.

"Hamma.....amma hamma"

"Ba sunana na tambayeka ko nace ka maimaita ba......kanason amna?,eh ko a'ah?,banason wani sharhi"

"Ina sonta hamma" Ya amsa masa yana yin qasa da kansa a sanyaye. Kai kawai fu'ad ya jijjiga,bai kuma sake cewa dashi komai ba,yayin da yabar musaddiq din da saqe saqe a ransa masu yawa,ya matsu yaji hamman nasa ya sake cewa wani abu amma bai sake fadi ba,kuma tunda har mintuna sukayi nisa yasan ba lallai ya furta komai din,don haka yayi qarfin hali ya motsa.

"Hamma.....maamah ta fadi cewa bataso ta kuma r......." Wani kallo ya waiwaya ya watso masa duk da tuqi yakeyi sannan ya maida dubansa ga titi.

"Kayi magana akan abinda kowa yakeso da wanda bayaso amma banda maamah......bana buqatar komai nata ciki harda ra'ayinta da meye bataso da wanda takeso......abinda na sani kawai shine na sauke haqqinta na ci sha sutura muhalli da lafiyarta......sai biyayya akan abubuwan da basu sabawa mahalicci da kuma addini na ba.....baya ga wadannan komai a kanmu nata ba dole bane". Yadda hammansa yayi magana ya sanyayar masa da jiki,ya sani gaskiya ya fada....kuma koshi yana yaba masa yadda yake qoqarin bata girmanta.

Sun rigasu isa intercontinental din,don sanda fu'ad ke parking a parking lot na gurin ga motocinsu nan ajjiye,ya tsaida motar yace da musaddiq.





*_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_*
08187255862



𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀
_Zafafabiyar_

ΜΆBΜΆOΜΆOΜΆK ΜΆ2

β±§Ι„β‚²Ι„β‚₯β‚³

π™‹π˜Όπ™‚π™€ 112




112



"Ka shiga ciki ina zuwa......ka fada mata zan shigo yanzu.....but idan naga tana kuka zan nesantata da kowa har sai ta daina". Har zuciyarsa abun ya qawatar da musaddiq,ya amsa masa a girmame yana bude motar sannan ya fice.

Da kallo fu'ad ya bishi har ya bacewa ganinsa,iska me zafi ya furzar daga bakinsa,ya sake yarda har yanzun shine garkuwar musaddiq,zai kuma ci gaba da zame masa garkuwa har sai ya tabbatar da cikar kamalar farincikinsa.

Hannu ya dora saman center console na motar ya dauki wayarsa,ya gyara zaman kujerarsa sosai yayi relaxing sannan ya soma lalubar number wayar abbansu wato alhj hamza kibiya.

Bisa jagorancin saddiq suka wuce amenity din,sannan ya nunawa kowa dakinsa. Amna dai da anni,nashi dakin shida musaddiq.....dakinsu huda suma su uku,sai dakin boss din nasu da duniyarshi......farouq ne ya zama shi kadai daban. Sabreen murmushi ta saki sanda suke bude dakinsu huda da sukace tazo taga wani abu,tana jin farouq yana balbalin masifa.

"Shi tuzuru dama abun rainawa ne......shi yasa aka wareni kaman wani barawo......duk wanda yayimin abu saina rama.....Allah ya kaimu lokaci,sati ukun ai kamar yau ne".

Idanu sabreen ta firfitar waje tana kallon matar dake zaune saman abun sallah.....momma bahijja ce cikin kamilalliyar shiga. Idonta ta murxa tana jin mafarki takeyi da gaske

"Qaraso sabreena.....mommmanki ce". Da gudu ta qarasa jikinta ta zube tana sakin wani irin hautsinannen kuka

"Momma duk kun gama birkitani.....kun gama bani mamaki,momma dama zakuzo?".

"Ko niyya babu me ita,duka aikin mijinki ne". Kalmar ta sauka sosai a zuciyarta,ta ruqunqume momma sosai tana hangen kamilar fuskar nan tasa. Wanne irin mutum ne shi me abun mamaki haka?,wanne irin mutum ne shi wanda ya iya nemowa abokin rayuwarsa maqurar farinciki?.

"Zazzabi kike haka sabreena?" Momma ta fada tana dagata a jikinta.

"Shine momma.....zai sauka,don Allah kada ki bari hamman nan yaji,tsaf zai sakani kwanciya asibiti"

"Kinsha magani?" Ta tambayeta cikin kulawa,kai ta gyada mata,duk da tasan ba wani magani da tasha tun a dubai,ta maida kanta ta kwantar saman qafafunta tana cewa.

"Ya akayi komai ya faru momma?,bani labari?" Ta furta tana riqr hannun haneefa da kyau cikin nata.

Doguwar waya ce da sai da suka shafe aqalla awa biyu ba kadan suna tattaunawa da alhaj hamza din,daga qarshe abban yayi shuru kafin ya sake magana.

"Na fahimceka muhammadu.......kuma na gamsu da bayananka da hujjojinka........amma me zai hana ka jira na qaraso nan din ko ku ku dawo gida?". Kai ya girgiza


" Kayi haquri abba.....bawai inason inyita musu dakai bane.... Amma karka manta annabi ya fada mana,ba'a jinkirta aikin alkhairi gaggauta yinsa ake"

"Na sani muhammadu banaso ka kirawa kanka matsala ne gaka kai daya" Murmushi ya sake saki yana yin gefe da kansa.

"Abba...ka manta muhammadu nake?....ka manta wannan me babban sunan?" Qaramin murmushi ya qwacewa Alhaji hamzan

"Ban manta ba kam.....jarumin gold daga qasar yarbawa da inyamurai" Wannan karon shi kansa fu'ad saida murmushinsa ya fadada

"Ka samu alhaj muhyidden,yana alranuna unguwar da gidanka yake......Allah yasa haka shi yafi alkhairi......amma kabi komai a hankali,idan akazo batun iyaye bin komai ake a sannu"

"In sha Allah abba.....na gode" Ya amsa masa yana jin wani farinciki yana ratsashi sukayi sallama.

Zaune kawai abban yayi da waya a hannunsa. Wanne

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login