Showing 111001 words to 114000 words out of 557259 words

Chapter 38 - πƒπ”ππˆπ˜ATA BOOK1 AND 2 HAUSA NOVEL

HUGUMA   

03 Nov 2025

528

bada alamar yana ciki ba,sai ya wuce a hankali kamar kazar da qwai ya fashewa a ciki zuwa study room dinsa,ya tura qofar ya shiga ya maida ya rufe.

Zaune kawai yayi saman sofa idanunshi a kulle,yayi nisan nazarin da shi kansa baisan wane zare a tunanikansa zai kama ba. Abu daya ne da yafi daure masa kai da dagula masa lissafi,qoqarin da takeyi da gaske na sai ta raba tsakaninsu,indai haka ne wannan fitar tasu tana da alaqa da qudurinta.....indai haka ne kudin da take nema lallai yana da alaqa da qudurinta......indai kuma haka ne tabbas wannan BAQUWAR FUSKAR akwai tata rawar cikin mission din......duk da yasan wannan din tsohon quduri ne dake ranta.....amma dukkan alamu sun nuna ta samu MAKAMASHI.


*D U N I Y A T A*

*_H U G U M A_*

PAGE 59


Shuru ne ya biyo baya tsakaninsu,babu wanda yace da dan uwansa komai tsakanin ita da anni din. Daga yanayin tsaiwarta da yadda take bin komai da wani irin kallo ta tabbatar ba alkhairi bane ya kawota,don haka taci gaba da abinda takeyi din ba tare data ce komai da ita ba.

Baifi minti biyu ba kacal sai ga amna ta dawo

"Yace gashi nan...." Ta bata amsa tana sake binta da kallo tamkar a tsorace,sannan ta qarasa ta dauki plate dinta ta koma kusa da annin ta naniqe ta zauna tana ci gaba da satar kallon maamah din.

Da sallama ya shigo falon cike da kamalar nan tasa dake shimfide saman fuskarsa,sanye yake da jallabiyya ruwan qasa,kansa sanye da qaramar hula tashi ka fiya naci.

Amna da anni ne suka amsa sallamar tashi,yayin da maamah ta dubeshi kadan kafin ta dauke kanta

"Mariya ce?,....bismillah......zauna mana" Ya fada yana zama kujerar dake daura data anni. Kamar tace ba zata zauna ba,to amma kuma zaman yafi kamata tayin,don tanason daga qarshe ta gasa masa maganganun da indai ya haifu zai fara janye jikinsa daga dukkan wata mu'amala ta fu'ad dama rayuwarsa gaba daya,yabar mata 'ya'yanta kamar yadda kowacce uwa keda iko da nata yaran.

"Muna lafiya.....ina fata kuma lafiyar ko?" Gyara zamanta tayi sosai tana dora qafarta daya kan daya,sannan ta saka idanunta sosai cikin nasa

"Wajenka nazo hamza" Ta fadi kanta tsaye,abinda yaja hankalin anni kenan tadan daga kai ta dubeta,sai kuma ta saukar tana son kwashe hankalinta sam sam daga kansu.

"To ai gani.....Allah yasa lafiya" Fuska ta qanqance tana dubansa idanunta a ciki.

"Al'amarinku yana bani mamaki hamza yana kuma dauremin kai.........duk duniya ban taba ganin inda ake irin haka ba sai a kanku,hankaka mai da dan wani naka?......amma mu ajjiye wannan batun......tunda kun zab lallai sai na zama maqasqanciya a gabanku akan 'ya'yana?......ba laifi don komai da ka gani a rayuwa lokaci ne.....kuma iyaka gareshi......" Ta furta qasan ranta tana hangen iya adadin lokacin da ya rage musu wanda alaqar uwa da uba zata wanzu a tsakaninsu.....da tazarar lokacin da alaqar zata juye zuwa alaqar gagarumin abokin adawar da duk duniya fuad din zai wayi gari bashi da abokin adawa irinsa. Burinta shine ta bude idanu taba tsabtsar gaba da adawa mai qarfin gaske ta qullu tsakaninsu......irin adawar da zata bawa kowa mamaki ta kuma shiga sahun tarihi......tabbas saita fanshe dukkan wani baqinciki da suma cusa mata......hakanan ba zata qyale ba sai sunyi aman duk wani da sukaci daga cikin arziqin fuad......koda kuwa wannan gidan da suke ciki yana cikin jerin sahun mallakar fu'ad din.

"Wai nikam hamza.......ban sani ba ko cikin duhu ne a sannan?......hadaka da kuma gamayya kukayi da ubansu fu'ad yayin samuwar cikinsu?,ma'ana tare kukamin cikinsu ko kuwa?" Ba alhaji hamza kibiya kadai ba,hatta anni dake zaune daga gefe ba tare da shiga shirginsu ba sai data cira kanta da sauri maganar tana dukanta

"Subhanallahi.......innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Alhj hamza ya fada zallan mamaki yana saukar masa,idanunsa akan fuskar amna wadda ta yunqura tana miqewa ba tare data tsaya daukan plate din abincin ba saboda yadda maganar ta girmimi kunnuwanta.

"Mamaki kukayi?,to ai ba abun mamaki bane duba da yadda kuka qanqame min rayuwar 'ya'ya hamza" Ta kuma fadi cikin izza ba shakka ko d'ar a cikin idanunta.

"Mariya cikin hankalinki kike kuwa?" Anni ta gaza jurewa ta fada tana kafeta da idanunta. Wurga kallonta tayi zuwa ga annin

"Kinga ina iface iface ne ko yage yage da zakiyimin wannan tambayar?"

"Shin mene marabar dambe da fada mariya?,ai hauka nau'i nau'i ne.....nakin ina kyautata zaton ta wannan fuskar yazo"

"Kamar yadda cutarwarku tazo da sigar yaudara da damfara ba.......na rantse da Allah a yau inda fu'ad yana a faqirinsa bashi da komai da tuni kun watsashi shi da dan uwansa........."

"Kaman yadda zamantowarsu halittar da zaki iya mora ta sanya kika dawo cikin rayuwarsu ba?....bayan kin watsar dasu a sannan kina zaton su din ba masu amfani bane,nauyi ne kawai a wuyanki?". Anni ta maida mata amsa ta hanyar katse numfashinta bacin rai yana fara nuna alamun tasiri cikin muryarta

"Ya isa aminatu......ban yarda ki sake cewa wani abu ba" Alhaji hamza ya fada yana daga mata hannu. Ya gama karantar akwai abubuwa masu tarin yawa a bunne cikin zuciyar maamah din,biye matan da annin zatayi shi xai bata damar furzar da maganganun da idan suka qyaleta basu tanka mata ba har ta mutu saidai ta mutu dasu a cikinta.

Dole ta ninke dubban maganganun da suke tsinkulinta a rai kawai don ta bawa abban girmansa,amma bawai don abinda take da shirin furtawa itama ya qare ba,ta kauda kai tana hadiye fushinta ba tare data sake jefa baki a maganarsu ba

"Ka gaya masa ya bini.....domin kuwa duk duniya ba wanda akace aljannarsa tana qarqashin qafarta face ni.....komin lalacewata......ka taimaka ka sakar masa mara ya rabu dani lafiya kaman yadda na tabbatar ka rabu da naka lafiya......ka shaida masa yazo ya bani kudin dana buqata a hannunsa.......bawai alfarma nake nema ba......ka gaya masa dole ne yayimin...." Tana kaiwa nan ta miqe tsam,idanunta akan anni da tayi kaman batasan da wanzuwarta a wajen ba. Taso ace annin taci gaba da ja,don tana da tarin maganganun da takeso ta amayar mata

"Wallahi duk d'an da ya hana uwarsa bacci.......shima bazai huta ba" Ta furta tana juya hankali kwance tana barin falon.

Shuru ne ya biyo baya,duk kuwa da cewa ta gama ta kuma fita daga gidan ma gaba daya

"Hasbunallahu wani'imal wakil" Alhaji hamza ya furta gauraye da wata ajiyar numfashi me nauyi idanunsa na kallon waje daya.

Baisan wanne irin abune yake dawainiya da mariya ba......baisan kuma wanne girman laifi sukayiwa rayuwarta haka da take musu kallon wasu manya manyan abokan adawarta ba. Anni batace komai ba kaman yadda shima bai buqaci tace ba,tanata qoqarin sarrafa bacin ranta da ganin ta hadiyeshi ba tare data barshi ya mata tasiri ba

"Ina muhammadu?" Alhaji hamza yayi tambayar yana duban annin

"Bansan ina yayi ba.....mun rabu dashi a dazu kan zai shiga wajenta" Ta amsa masa a taqaice. Karkacewa yayi ya ciro wayarsa daga aljihun jallabiyyarsa ya soma trying number din fuad din.

Sosai yayi nisa cikin tunani,a haka idan ka ganshi zaka dauka bacci yakeyi,saidai ba ko guda daya. Wasu mintina ne daketa wulga masa tsakanin bacci da ido biyu wanda a ciki baisan ainihin abinda yakeyi ba

A silent wayar take,amma hasken da take fitarwa ya ratsa rufaffun idanunsa a cikin duhun dakin.

Kamar bazai bude idanun nasa ba amma sai ya budesun a hankali yana saukesu akan wayar. Yayi tsammanin ya kashe duka layukan,sai a sannan ya lura guda daya ya kashe. Sunan daya gani saman wayar ya sanyashi sauke qafafunsa a hankali yana maida hankalinsa a kanta,ya miqa hannu ya daukota daga inda take ajiye yana qoqarin dagawa.

Sallama yayi amma muryarshi ta maqale,yadanyi gyaran murya sanda yajiyo muryar abban yana masa sallama

"Ina ka shiga ne?" Alhaji hamza ya tambayeshi

"Ina cikin gida abba"

"To fito......inason ganinka.....ka sameni falon anninka"

"To abba" Ya amsa masa a ladabce. Remote ya laluba ya dauko ba tare daya tashi a gun ba ya maida hasken dakin. Take yayi tarwai da haske kaman yadda ainihin dakin yake

"Allahumma la sahla illa ma ja'altahu sahla.....wa'anta taj'alil hazna iza shi'ita sahla" Ya furta muryarsa can qasa,yana jinsa gaba daya ba kuzari,tun daga zuciyarsa har zuwa gangar jikinsa.

Bai wani bata lokaci ba ya sauya kayan jikinsa sannan ya wuce sassan annin. Sallama yayi hankalinsa na kaiwa fuskar anni. Tun bai zauna ba jikinsa ya bashi akwai wani abu,don ba kasafai kake ganin fuskar annin a haka ba. A nutse ya qarasa shiga ciki,kai tsaye kuma ya nufi inda Alhaji hamza yake,wanda bai motsa ba daga wajen tunda maamah din ta fita ta barsu.

"Bismillah.....zauna" Alhaji hamza din ya masa nuni da kujerar dake kusa dashi. Sanda ya zauna din ita kuma anni ta miqe da zummar barin wajen,abban ya maida dubanshi kanta

"Zama kema zakiyi......ina zakije?" Duban abban tayi,kaman zatayi magana sai kuma ta fasa,ta koma ta zauna ba tare data sake cewa komai ba.

"Muhammadu" Abba ya kira sunanshi kai tsaye,abinda ba kasafai hakan ke kasancewa ba. Mamakin ya hanashi amsawa saidai ya daga kai kawai yana duban abban.

"Muhammadu ya ina yabonka sallah zaka kasa alwala?" Abban ya sake fada idanunsa still akan fu'ad din,tausayinsa kuma yana ratsa zuciyar abban.

"Abba....." Fu'ad ya motsa labbansa a hankali da zummar yin magana

"Me dame mariya tace maka tana da buqata wanda bakayi mata ba?" Ya masa tambayar Kai tsaye don sauqaqe masa wahalar tunani.

"Abba.....ba wani nauyi ko haqqi daya kamata na bawa maamah wanda bana bata shi......bana tunanin akwai wani abu da ya zama nauyi ko haqqi da ubangiji ya doramin wanda na gaza dauke mata shi". Har cikin zuciyarsa abban ya gamsu da wannan,saboda shi kansa ganau ne bawai jiyau ba akan hakan

"Na sani Muhammadu......amma don me yasa idan tana da buqatar kudi daga hannunka kake hana mata?". Sam baima kawo wannan zancan bane,sai ya sauke boyayyar ajiyar zuciya yana sauke kanshi qasa.

Rashin amsawarsa ya bawa abba amsar tambayarshi

"Me yasa kusan ko yaushe matsalarka da ita akan tana neman kudi ne ka hanata?,bayan Allah yayi maka wadatar da zaka iya bata ko nawa ne Muhammadu?" Ya qarashe maganar ta sigar tambaya idanunsa a kanshi,can qasan ransa yana mamakin abinda ke kawo musu matsala akan abinda yasan ya jima da fin qarfinsa. Km

*D U N I Y A T A*

*_H U G U M A_*

PAGE 60



"Ka sani cewa......duk d'a aljannarsa tana qarqashin qafar iyayensa?,kuma haramunne jayayya dasu bare su buqaci abu aqi ayi musu?"

"Na sani abba.......amma bazan iya bawa maamah ko sisi ba". Sosai maganar ta bawa abban mamaki,har anni dake zaune daga gefe itama ta daga kai tana kalleshi

"Akwai abubuwa masu yawan da baka gama saninsu ba abba akan maamah......akwai boyayyun sirrikan dana ajewa cikina abba.......akwai wasu abubuwa masu yawa wadanda ba zasu fadu ba......amma koma meye cinta shanta lafiyarta dama suturarta wani abu ne da bazan taba iya hana mata su ba ko don albarkacin haihuwa da Allah ya bata........amma batun kudi abba........bazan iya bata ba"

"Dalili?,dalili nakeso naji Muhammadu" Abba ya sake tambaya cikin tsananin mamaki. Bai taba umartarsa da abu ba ya saba.....sai gashi s yau yana qoqarin bijire masa.......tabbacin akwai wani qaqqarfan dalili da kuma hujja kenan

"Abba...." Ya kirayi sunansa yana jin nauyin abinda zai furta din. Shurunsa ba abinda zai harfa tsakaninsa dashi sai gurguwar fahimta,bayaninsa din kuma bawai abu bane me dadin ji ko sauraro ba.

"Kasani Muhammadu.....koda baka bayar ba ni zan dauka na bata da kaina"

"Zan bayar abba.....zan bata amma bawai don zuciyata tana so ba......"

"Zuwa yaushe kenan?" Ya sake tambayar sa

"Zan yiwa sadiq magana,zai saka mata"

"Kirashi yanzu yanzu" Ya sake bashi umarni kai tsaye. Dole ya fidda waya ya turawa sadiq din saqon umarnin fidda kudaden,sannan ya aje wayar yana duban abban

"Zai sanya mata in sha Allahu". Ajiyar zuciya abban ya sauke. Shi kansa yasan akwai qalubale masu tarin yawa cikin rayuwarsa,to amma ko meye zaiyi yana yine saboda kyautatuwar rayuwa da kuma gobensu.

Kamar yadda ya saba lokaci bayan lokaci baya gajiya da yi musu nasiha dukkaninsu,yanzunma nasihar ce dai yayi masa.

Haka kawai sanda yake barin falon yaji hankalinsa bai kwanta ba. Muddin maamah tazo gidan to ya tabbatar akwai wani abu maras dadi daya biyo baya. Ko mene kuma ya farun yasan babu me gaya masa cikin gidan,daga amna sai musaddiq wanda baya gidan.

Yana takawa a farfajiyar gidan yana lalubar number amna din. Bugu daya ta daga tana amsa sallama a nutse

"Fito waje inason magana dake"

"To hamma" Ta amsa masa tana sauke plate din hannunta data gagara cin abincin ciki. Wayar tabi da kallo har yanzu muryar matar tana amsa kuwwa a kunnenta. Maganganunta sun girmi kunnuwanta,batasan komai a kanta ba amma tana ganin rashin kirki qarara daga dukkan wani motsi nata.

A tsaye ta sameshi idanunsa saman qananun shukokin dake bawa wajen iska me kyau da yanayi me dadi

"Zauna" Yace da ita yana nuna mata kujerar dake gabansa tare da qoqarin karantar fuskarta. Ba musu din ta zauna tana jin jikinta yana qara sanyaya daga kallon da taga yana yi mata

"Akwai baquwar da tazo gidan nan dazun?" Ya tambayeta yana kallon tsakiyar idanunta. Kallonsa itama tayi sai tayi qasa da kanta tana tuna gargadin da anni tayi mata

"Ba ruwanki da abinda tazo ta fadi,wannan ba abinda ya shafeki bane.....ba'a gaban kowa kuma akayi ba saike kadai...... Kada na soma jin zancan nan ya fita" Gargadin annin kenan bayan ta bar falon ta isketa a kitchen.

"Ehnnnn......kina nan sanda ta shigo na tabbatar......akwai wasu abubuwa data cewa anni da abba?" Ya sake tambayarta yana kallon fuskarta. Ba zata iya kallonsa kuma tayi masa qarya ba......hakanan ba zata iya saba maganar anni ba,don haka ta zabi sunkuyar da kanta ta kuma girgiza masa kai. Qaramin murmushi ne ya subuce masa wanda ba komai cikinsa sai bacin rai

"When kika fara yiwa hamma qarya amna?" Tambayar tasa saita rudata gaba daya,taji bata da sauran zabi illa ta shaida masa gaskiya.

Tambayar farkon data jefawa abban ita ta sanya fuad jan kujera shima ya zauna wani nauyi yana saukar masa. Ya ilahi.....wannan wacce irin jarabawa ce?,me yasa UWA take jin tasu jarabawar rayuwar?.

"Tashi kije" Ya bata umarnin daya sanyata miqewa da sauri tana barin wajen.

Tafin hannunsa ya sanya yadan daki goshinsa yana lumshe ido. A mizanin hankali da tunani da sanin ya kamata......yayi zaton maamah zata kasance ne cikin sahun farko na mutanen da ko kansu sukan sanya a gaba suka yanka ba zata ce komai ba.

****A hankali take takawa cikin layin zuciyarta na bugawa a hankali a hankali. Bugun zuciyartata ne batasan meye ainihin dalilin faruwarsa ba. Tsoron ganinsa takeyi ko kuma shauqin ganin nasa?.

Tun daga wancan ranar daya aike mata wasiqa ta qarshe bata sake jinsa ko kuma ganin motsinsa ba,har kawo yau da suke shirin cinye satin gab daya a kuma shiga sabon sati.

"Assalamu alaikum" Sautin sallamar daya sanya zuciyarta wani irinn bugawa ta ba zata,mamaki kuma da tsoro suka hanata amsawa saboda yadda taji alamun muryarta a shaqe take. Kasa waiwayawa tayi har zuwa sanda ya tako yana cimmata a inda take,ya zagaya kuma yana yiwa kansa matsaya a gabanta dab da ita. Yanayin kallon daya rutsata dashi ya hanata janyewa baya kaman yadda takeyi a duk sanda ya tsaya kusa da ita kamar haka

"Banga alamar kinyi kewata ba......inacan soyayyarki zata kasheni?" Ya furta yana karyar da wuya tare da komawa kalar tausayi ainun.

Idanunta ta fiddo waje tana dubansa

"Me ya sameka?" Ta samu bakinta da subucewa gami da tambayarsa kai tsaye.

"Ciwon sonki" Ya fada wani mayaudarin murmushi yana subuce masa. Nasararsa yake hange muraran daga idanun yarinyar,ya tabbatar yana dab da cika burinsa......yana kuma gab da daukan fansa.

Wata ajiyar zuciya taja tana sauke numfashi

"Bakiyi kewata ba huda sam sam" Ya sake fadi yana kalmashe wuya idanunsa cikin nata,yanason ya sake dasa mata dafin da zaiyi wahalar gogewa daga ranta. Yanason ya cimmata sosai,ya kuma nutsar da ita cikin tafkin qaunarsa fiye da yadda yayarta ta jefa masa qugiyar da har yanzu ya gaza zameta daga ruhinsa. Baya jin akwai wata mace da zata iya kashe masa qishirwarta. A kanta yakejin komai kuma ita kadai zata iya sama masa da wannan nutsuwar.

Saidai kuma ya karanci hakan wani abu ne da bazai taba samunsa ba.....don haka gwara yayi daukan fansan da zata gwammace bashi rayuwarta yayi yadda yaga dama da ita.

"Don Allah me kyau kice wani abu mana" Ya fada yana marairaice mata

"Nayi kewarka mana....." Ta samu kanta da furtawa. Yadda ya fidda idanu yana gwada mata mamakinsa ya sanyata jin kunya gami da mamakin kanta. Wani abu ne da yake faruwa da ita karo na farko a rayuwarta da bata taba tunanin zuwansa a nan kusa ba

"Da gaske kike?" Ya fadi har yanzu idanunsa a waje,sai tasa hannunta kawai ta lullube fuskarta dasu tana sakin qaramin murmushi,abinda ya sake fidda

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login