Showing 486001 words to 489000 words out of 557259 words

Chapter 163 - πƒπ”ππˆπ˜ATA BOOK1 AND 2 HAUSA NOVEL

HUGUMA   

03 Nov 2025

531

Da sauri ta damqe hannunsa tana duban tsakiyar idonsa,sai ya dage mata dukka girarsa yana tambayarta why?,da wannan kallon nasa.

"Ba bra a jikina".

" Good" Ya fada da hanzari yana daukanta cak ya azata saman drawer din,sannan yasa hannunsa ya dage rigar har zuwa inda yakeso.

Da cikin nata ya fara wanda ya fara turo kansa,ya aza dukkanin hannuwansa akai.

"Good morning my Angel's" Dubansa tayi.

"What?" Yatsansa ya dora saman lips dinsa

"Shshshsh" Ya fadi sannan ya maida hankalinsa kan cikin.

"Eheeennnnn......hope you're doing well......am eager to meet you my life.......have a nice and great day" Sai ya sunkuya yayi kissing na cikin. Sama ya komar da fuskarsa tsakanin ababen dake matuqar janye hankalinsa,qanqameshi tayi sanda yake cusa kansa a tsakiyar su,sannan ya sakar mata wani kiss din me sanyi kafin ya janye fuskarsa da idanunsa suka fara canza launi.

"Mun gama gaisawa.....me kike cewa?. Fuska ta bata.

"Son kai hamma.....son kai"

"Name?" Ya tambaya yana ware hannayensa.

"Angels hamma?......ni nafison baby boys.....masu kama da kai.....masu quality dinka". Ta fada tana tura baki gaba. Kyau sosai lips dinta sukayi masa,yasa hannu yana taba lips din murmushi na qwace masa,ya motsa bakinsa cikin nutsuwa.

"Nafison baby girls masu tausayi irin naki......masu tsananin zumunci irin na ummansu......masu qaunar 'yan uwansu.....kinsan ma haihuwar diya mace falala gareta me girma fiye dana d'a namiji?" Kai ta girgiza

"Na sani,idan aka haifi uku aka musu tarbiyya aka aurar dasu zasu zama sanadin shigar mahaifansu aljanna,sannan haihuwar d'iya mace tamkar shigowar haske biyu ne cikin gida,saboda zata jawo wani namijin shima ya zama naku". Tafi sosai ya sakar mata yana murmushi

"Bravo alaiki...." Ya furta yana kissing tafin hannunsa ya aike mata dashi.

"Duk da wannan?,duk da wannan my world kikeson boys?" Kai ta gyada.

"Na rigaka addu'a fa hamma......inaji a jikina Allah ya amsamin.......ina buqatar photocopies din muffin dina" Ta fada tana tsiyaya masa ruwan gwadar ta miqa masa.

Karba yayi yana dubansa,sai daya qare masa kallo sannan ya kalleta da lallausan murmushi

"Ya akayi kikasan ina sonsa?". Dukka girarta ta dage masa tana nade hannayenta a qirji,hakan ya qara mata kyau sosai.

"Kana tunanin idan nace inasonka ina sonka ne da wasa?......duk wanda nace ina sonsa......ina sonsa da gaske.....ballantana kai...." Ta qarasa fadi tana nunashi da yatsa daidai sanda kira ya shigo masa.

"Farouq?" Ya fada a mamakance,farouq dinne da kira haka da sassafe?,cikin jikinsa yaji tabbas akwai wani abu daya faru,ya miqa hannu yana daga kiran



*_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_*
08187255862



𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀
_Zafafabiyar_

ΜΆBΜΆOΜΆOΜΆK ΜΆ2

β±§Ι„β‚²Ι„β‚₯β‚³

π™‹π˜Όπ™‚π™€ 144


*_NACE BA......._*🧏🏽🧏🏽

*_Hajjaju a ina kike siyan turare?....._*

*_NACE A INA KIKE SIYAN TURARE?_*

*_Ga wani fa........TASTED AND TRUSTED ne.......mun gwada munga ingancinsa_*

*_Da yardar Allah saikin godemin_*

*_KUNSAN DUK INDA QAMSHI YAKE ZAKA SAMENI A GURIN,MAGANAR GASKIYA KENAN AHTO_*πŸ˜‚πŸ˜‚

Golden oud
Hawi
Sandal balls
Sandal flakes
Cotton bakhoor
Kabbasine mix
Khumra(alba,alsuma,ebony,monarch,musk)
Deep crush (luxury khumra).
Signature oil
Kuleccham
Kabbasine spray

*_YA SUBHANALLAH.....hajiyata dukka wadannan zaki samesu a_*

*_PRIME SCENTS(the scents of royalty_*

*KE DAGA JIN SUNAN KINSAN ZA'A ZUBDA QAMSHI ME AJI DA DAUKAN HANKALI*

*SUNA NAN A*

*_No 3,kabiru sani lawan street,farawa layout,Maiduguri road kano_*

*BA'A KANO KIKE BA?*

*_karki damu,tuntubeta ta nan,TABBAS kayanki zasu iskeki a duk inda kike cikin aminci da yardar Allah,NA BAKI TABBACIN HAKA_*

*DANNA RUBUTUNNAN DON YIN MAGANA DA ITA KAI TSAYE*πŸ‘‡πŸΎπŸ‘‡πŸΎ
wa.me/+2348103155915

KO KI KIRATA TA NAN

08103155915



144


Shuru kawai yayi yana sauraren farouq har ya gama gaya masa abinda zai fada din. Satar kallonta yayi sanda take qoqarin zuba masa wani tea din.

"Ka kula please dude.....banaso adda taji maganar nan ko don lafiyarta.....itama fanna din ban gaya mata ba,zan wuce gidan yanzu"

"In sha Allah" Ya fada yana sauke wayar daga kunnensa.

"Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un" Shine abinda yaketa maimaitawa can qasan zuciyarsa kafin ya samu ya miqe tsaye yana duban ta.

"Adamamin tea din nan,abba ne ya kirani yanzunnan wai ya kusa sauka yanason nazo". Har ga Allah bata kawo komai ba,kawai mamakinta shine abban ke nemansu da safe haka?,kuma shida farouq?. Ba huruminta bane zafafawa kan sanin meye asalin ainihin kiran ba,don haka ta taimaka masa ya sauya kayansa ya fice zuwa ma'ajiyar motocinsa,inda ya taso jordan suka fice tare.

"La haula wala quwwata illa billah" Shine abinda yake maimaitawa kawai akan hanya yana murza goshinsa. Wani irin tashin hankali ne yaji yana lullubeshi,duk irin tsaron da ya saka.....duk yadda yake kaffa kaffa amma daga gefe akwai wanda yake fakonsu?.

"Su waye?.....su waye?" Ya furta a dan zafafe yana jinjina hannunsa yana duban titi,yana jin kamar ya tariyo daren jiya komai ya wakana a idonsa.

"Waye ya rage?,waye yayi saura?" Ya fadi yanason tunawa ko akwai wani abu daya bari wanda ya kamata yayi baiyi ba.

Wayarsa ya fiddo ya fara qoqarin gwada number amna da kanshi,amma switched off ake gaya masa.

"Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un" Ya koma maimaitawa. Anni kawai yakeji.....ko musaddiq zai biyo bayan anni ne wajen shiga rudani,saidai ita anni ta fishi dauriya da dakiya.

Tun daga harabar gidan daga kan fuskokin masu tsaron gidan ya karanci tashin hankali b'aro b'aro. Jordan na fakashi ya sauka da dan sassarfa ya wuce cikin gidan.

Da batulu ya soma cin karo,shugaban ma'aikatan gidan.

"Ina anni?" Ya tambayeta ba tare daya damu da amsa gaisuwarta ba.

"Tana sama sir"

"Okay.......Inaso kowanne baqo a gidan nan a kula dashi yadda aka saba,a kuma sallamesu ba tare da kowa yasan halin da ake ciki ba......a shaida musu an soke walimar saboda annin batajin dadi,likita kuma yace a barta ta kwanta ta huta sosai,saddiq zai sallami kowa,masu tafiya a jirgi da masu tafiya a mota,inaso nan da azahar gidan ya zamana daga mu sai mu,na tabbata ku kudai kukasan abun.....daga haka banaso labarin ya qara gaba"

"In sha Allah yallabai za'ayi duk yadda kace" Ta fada cikin girmamawa.

Yana shirin haurawa saman yaji muryar farouq,waiwayawa kawai yayi ya kalleshi yana amsa sallamar saiya juya yana haurawa saman. Hankalinsa duka yana kan anni,don haka ita ya fara gani a sanda ya bayyana a parlor din saman.

Kallo daya tak yayi mata yaga wata irin rama ta bayyana saman fuskarta,daga daren jiya zuwa yau?,idan kuma abun ya shallake haka kuma fa?,fu'ad ya tambayi kansa da kansa hankalinsa a tashe.

Sauke dubansa ya sakeyi ga huda,wadda ke cure waje daya taci kuka har ta soma jin ba dadi,saddiq na zaune kusa da ita,da alama qarfin gwiwar lallashinta yake neman tattarawa kuma bai samu hakan ba.

Musaddiq kuwa yana zaune kaman zane,ramarsa har taso wuce ta annin da wani taqi na musamman.

Kallon da yayi musu dukkaninsu a lokaci daya sai yaji zuciyarsa na nufin karyewa kaman yadda ta anni ta karye. Ganinsu sun biyun sai takejin dukka qarfinta ya tattara a nan....kaman sune duk wani hope nata a yanzun.

Fu'ad ne ya lura da yadda jikinta ya soma rawa,ya qarasa da sassarfa ya riqeta yana zaunar da ita. Komawa yayi gabanta ya zauna sosai yana tanqwashe qafafunsa.

"Kece qarfin mu anni.....don Allah ki sake bamu wannan qwarin gwiwar koda karo na qarshe ne....koda shine alfarmar qarshe da zaki mana mu 'ya'yanki". Duk yadda taso tsare hawayenta sai daya zarto,saidai tayi qoqarin saurin daukeshi,banda su farouq da fu'ad din ba wanda ya gani.

"Allah shine qarfinmu muhammadu.....shine kuma zai tsaya mana" Ta fada tana tattaro jaririyar dauriyar data rage mata. Saidai shigowar abba a daidai lokacin ya sanya qwarin gwiwar nata ya sulale yabi ruwa,don nufarsa tayi hawaye yana tsinke mata,fu'ad ya yiwa saddiq alama daya sauko da huda ya juya yana sauka da sassarfa.

*_BAYAN MINTI TALATIN_*

Dukkaninsu suna falon daya dauki shuru bayan gama tattaunawarsu akan al'amarin.

"Nayi alqawarin muddin ina numfashi......tsakanin yau da gobe.....idan yayi tsanani zuwa jibi,tabbas da ikon Allah,da kuma girman zatinsa amna zata dawo cikin ahalinta.....inason kowa a cikinku ya ajiyemin wayarsa.....BB harda kai,kubar security code dinku akai basai kun cire ba.....abu na biyu kowa inaso ya sanya ido akan motsinsa,da motsin duk wani mutum da yake mu'amala dashi komai qanqantarta.....anni ki saka taki wayar a ciki.....abba zanyi connecting kowanne kira da wayata basai ka bayar da taka ba.....but kowanne saqo ko.kiran duk da nayi connecting ka kula sosai yayin dagawa......zamuyi aiki da team dina na kwana biyu zuwa uku in sha Allah" Yadda yace din duka hakan akayi,har zai fita ya dubi huda.

"Bani taki wayar" Saboda wani tunani da yayi. Throughout yau bayason yau sabreen tasan komai ko taji komai,idam ta yuwu ma har zuwa sanda zaa kammala abun,saidai yasan abune me wahalan gaske,karbe wayar hudan zai rage shigarta tashin hankali.

Wunin ranar gaba daya bai zauna ba,dukkaninsu shi da farouq dinma,zirga zirga ce kawai ake yinta a sirrance. Hankalinsa dukka yana kan wayoyin daya karba,wai ko zaiga wani baquwar number ya shigo,saidai ko gilmawar saqo bai gani ba.

Zuwa yammaci saqo da kiran sabreen ya cika masa waya,sai daya idar da sallar la'asar ya ciro wayar sannan ya tuna tunda ya fita a gida bai kirata ba. Da sauri ya maida kiran nasa zuwa ga wayarta,bugu daya ta dauka,muryarta duk tayi wani laushi sosai.

"Am so sorry my world.....ayimin afuwa,munyi busy yau sabgogi sun riqe muffin sosai".

"Hamma na dauka ka manta dani ne yau?,yau Walmar anni,ga lokaci yana shirin kufcemin,na gama shiryawa ban sameka ba,kasan bazan fita ba kuma bada izininka ba,still kowa a gidan na kira number dinsa bai daga ba,hadda huda ma,lafiya kuwa hamma?". Yadda tayi maganar ya tabbatar jikinta ya soma raya mata akwai matsala,muryarta tayi wani laushi.

"Na saka an tsaida walimar nan sabrrr...zazzabi ne ya saukarwa anni,kinsan kuma tana da asthma.....so kiyi zamanki a gida.....i will tray my best naga na dawo gida da wuri". Dan jim tayi kadan kafin tace.

"Anya baka boyemin wani abun hamma?,ko wani abunne ya samu annin?". Murmushi ya saki me dan sauti na qarfin hali.

"Ba komai my world.....karki damu.....ki kulamin da kanki,ki gaidamin yarana". Ya fadi yana katse kiran.

Lamo kawai tayi saman gadon zuciyarta na wani bugawa,bugun sam ba daidai take jinsa ba,hakan yana sake bata tabbacin akwai abinda yake tafiya ba daidai ba.

Tayi juyi saman gadon har batasan adadinsa ba,a nan sallar magariba ta sameta taje ta bada ita,tayi isha'i ta sake dawowa ta kwanta.

Indai ciwon anni baiyi tsanani ba ai ya kamata ace ta samu koda mutum daya ya daga kiranta,bawai kowa ta kira wayarsa zata yita ringing bai daga ba.....ciki harda fuad din kansa.

Sanda tara na dare yayi sai taji hankalinta ya soma tashi,kiransa ne ya bata relief dan kadan.

"Am sorry....on my way dear,karkiyi kewata da yawa". Maganan da sukayi kenan a taqaice.

Yana ajiye kirannata wayar farouq ta dauki ruri. Da hanzarinsa ya ajiye tasa wayar y kuma daga wayar farouq din yana kallon screen din.

Baquwar number ce da babu ita a jerin lambobin kan wayar,baiyi jinkiri ba yayi hanzarin hada abinda zai hada ya kuma daga kiran.

"Farouqu hamza kibiya haka ne?"

"Shine" Fuad ya furta kansa tsaye yana fatan hirar tayi tsahon da yakeso.

"Yauwa......mune wadanda muka dauki qanwarka amna a jiya........saidai kafin mu tattauna komai daku muna buqatar kudi naira billon goma". Idonsa ya lumshe ya sake budesu,wani fushi yana taso masa yana lullube zuciyarsa. Ashar yakeso ya fara sake musu a matakin farko,to amma kuma har yanzu ba'azo gurin ba.

"Ba matsala.....zamu saka muku......amma idan munyi hakan zaku sakar mana qanwa salin alin?".

"Me yuwuwa....duk da bamu keda wannan hukuncin ba,wanda keda ikon fadin a saki ko a kashe daban.....wannan din ladan aikinmu ne muke buqata daga gareku". Bakinsa yaji yana motsi,amma sai yayi qoqarin danne zuciyarsa.

"Zamu biya mun amince......ku fadi inda za'a saka kudin".

" Zamu saka" Ya fada yana datse kiran.

"Oh shirt" Fu'ad ya fada yana dukan seat din motar. Qiris ya rage mintunan su cika.....baici nasara ba......

Bayajin wannan daren yana da nutsuwar gyangyadi ko bacci komai qanqantarsa.....maganar kisa suke fa idan ta kama?. Baiko jira Jordan ya gama tsaida motar ba ya bude ya dira daga ciki yayi cikin gidan.

Baiko tsaya tantance wanda yake parlor din ba ya ketashi ya wuce hallway,wannan qofar dake a kulle kullum ya danna ya budeta yana kutsa kansa ciki.

Ajiyayyen gurinsa ne dake dauke da tarin na'urori,ba kuma kasafai ya fiya shiga wajen ba sai ta baci ko kuma yana da babban aiki irin haka.

Gaba daya qwayayen ya kunna ya kuma kunna kowacce na'ura ya saitata kan aiki,ba dadewa komai ya daidaita,ya fidda gaba daya wayoyin ya zubesu ya riqe ta farouq a hannunsa yana kwafe numbers din zuwa allon screen din dake gabansa.

Tiryan tiryan ya soma kurdawa cikin bincikensa,saidai kaman yadda ya zata komai ya tsaya daidai iya mintuna daya kashe kiran.

"Ya salam" Ya fadi yana jin wani zafi da fusata.

"Da gaske dai wani abu ya faru" Muryar sabreen ta ratsa kunnensa. Da sauri.ya daga kai yana dubanta. Tana tsaye daga bakin qofa,sanye da night wear baby pink masu daukan idanu masu hawa biyu,gashinta ta sakeshi saman kafadarta,yayin da jaririn cikinta ya bayyana sosai ta cikin rigar kasancewar ta lafe mata sosai a jikinta.

Duk da yanayin da yake ciki na tashin hankali hakan bai hanashi hango kyawunta ba......hakan bai hanashi ganin wani kwantaccen kyau daga gareta ba.

"Listen sab....."

"Karka rufemin hamma.....na roqeka" Ta fada jikinta da muryarta dukka suna rawa.


*_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_*
08187255862


𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀
_Zafafabiyar_

ΜΆBΜΆOΜΆOΜΆK ΜΆ2

β±§Ι„β‚²Ι„β‚₯β‚³

π™‹π˜Όπ™‚π™€ 145


*_Bgawo's KITCHEN AND APHRODISIAC_*


*_WATA KILLATACCIYAR MASARAUTA CE,WADDA KE QUNSHE DA DUKKAN NAU'IKAN ABINDA KUKESO_*


*_GIRKE GIRKE NA ZAMANI_*

*_KAYAN MAQULASHE DA NAU'IKAN DRINKS KALA KALA_*

*_INGANTATTUN TSUMAMMUN MAGUNGUNAN GYARAN MUTUNCIN 'YA MACE......GYARA IRIN NA IYAYE DA KAKANNI DA INGANTATTUN MAGUNGUNAN DA BABU DUNGUSHE KO KOKWANTO A KANSU_*

*_KALAR MAGUNGUNAN DA SAO WAJEN IYAYENMU NA DAURI.....INGANTATTUN SAUWOYI DA SAQE SAQI DA AKA SARRAFASU ZUWA MAGANIN GYARAN DIYA MACE_*

*_BIKI KUKE DASHI KO SUNA?_*

*_SAUKAR KARATUN QUR'ANI?_*

*_KO KUMA WALIMAR AURE QARIN MATSAYI A GURIN AIKI KO KUMA WANI QWAR QWARYAN TARO?_*

*_KO YAU DIN BAKIJIN SHIGA KITCHEN?,TSAFTATACCE KUMA INGANTACCEN ABINCI KIKE BUQATA A CIKIN WARMERS DINKI KO FOOD FLASK?_*

*_HAIHUWA KIKAYI?_*

*_KO GYARA ZAKIYI KAWAI A MATSAYINKI MA CIKAKKIYAR MACE?_*

*_BGAWO'S KITCHEN SHINE MUHALLIN DAYA DACE DA DUKKA WADANNAN BUQATUN NAKU_*

_Maza garzaya ki tuntubesu ta wannan number wayar_

08104553105
08127084190

*_zaki godemin qwarai da haduwa da BGAWO'S KITCHEN_*


*_BGAWO'S KITCHEN_*
*MATATTARAR BIYAN BUQATUNKU*




144


"Is alright......zo ki zauna" Ya fada yana tashi da kansa,ya kuma tarbota yaja mata kujera ya zaunar da ita.

Ta bashi dukkanin wata nutsuwa da hankalinta tana kallonshi.

"Kiyimin alqawari ba zaki daga hankalinki ba....."

"Nayi hamma.....nayi". Kai ya jinjina,ya sake riqe hannunta sosai yana duban tsakiyar qwayar idanunta.

"Amna ce tadan bace jiya,amma yanzun haka ina kan gano inda take"

"Amna ta bata ko kuma an saceta?,wanne ne daidai a ciki?". Ta tambayeshi tana jin wata kaduwa tana kama ilahirin gabbanta.

Juya maganar tata yakeyi a ransa,ya sake kallonta yana ganin yadda ta kafeshi da ido kaman me tuhumarsa da aikata hakan.

" Kowanne za iya zama daidai....."

"Bazai zama ba.....inaji a jikina dauke amna akayi intentionally.....wallahil azeem" Tana kaiwa nan saita rushe masa da kuka gaba daya.

Rudewa yayi,gaba daya kukanta ya dauke masa nutsuwa.

"Bamuyi haka dake ba sabreen.......karki cutarmin da yara please" Ya fadi yana hade hannayensa guri guda gami da sanya nata hannuwan cikin nasanπŸ™.

"Me yasa zaka boyemin hamma?......sai idan ta mutu sannan zaka gayamin?,ina huda?"

"She's safe" Ya bata tabbaci. Kai ta girgiza,sam hankalinta bai kwanta ba.

"She's not safe tunda aka dauki amna.....nadra haneefa dukkansu suna cikin barazana"

"Like how?" Ya fadi yana dubanta da tarin tambaya gami da zama sosai a gabanta sabanin tsugunnon dazu.

Tambayarsa ta dawo da ita cikin hayyacinta. A hankali ta sassauta sautin kukan nata. Zato bai zama gaskiya ba.....zatonta kuma a yanzu baida hujja ko dalili sai qwqwaran zargi,tana gudun ta furta abinda idan yaje ya dawo zai zama ba gaskiya bane,da wanne ido zataci gaba da kallonsa?..

"Kina da wani masaniya ko hasashe ne?" Kai ta girgiza

"Babu....but duk wanda ya shiga ya dauki amna....nadra dasu huda ba zasu gagareshi ba"

"A tsukinnan indai ba aljani ba,banajin akwai wani dan adam daya isa ya keta tsaron da gidan yake dashi ya dauki amna.....ina kyautata zaton fita tayi.....zan binciki duk wani CCT footages na gida.....naci alwashin amna ba zata kwana uku ba cikin iyalinta ba". Wani irin abu taji yana yawo da ita,ya jima yana qoqarin daidaita mata nutsuwarta,amma kuma hakan bai hanata kwanan kuka ba,bisa sharadin itama gobe ba zata zauna a gidan ba,ya kaita gidan anni.....anni bata cancani fuskantar wannan tashin hankalin ita daya ba.

β˜…Taku biyu tayi ta sake juyowa tana komawa bakin window din. Sake riqe wayar tayi sosai a kunnenta tana jin wani farinciki yana yawo da ita,jinta take tamkar a saman gajimare. Karon farko data fara kasancewa cikin sa'a a rayuwarta,karon farko data aiwatar da wani aiki da

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login