Showing 150001 words to 153000 words out of 557259 words

Chapter 51 - πƒπ”ππˆπ˜ATA BOOK1 AND 2 HAUSA NOVEL

HUGUMA   

03 Nov 2025

569

da tsaffin 'yan wasa......gogagge ne kana kallonshi,kuma shima qwararre ne da irin tasa qwarewar,wanda idan kowa baiyi takatsantsan ba komai zai iya faruwa"

"Shege sama'ila" Barau ya fada yana qyaqyacewa da dariya

"Ka zuba ido kawai kayi kallo" Ya amsa masa yana maida hularsa daga gaban goshi zuwa qeya.

A duk sanda yakeson samun nutsuwa ta qwaqwalwa da ruhi sararsa shine kwanciya,ya rufe idanunsa yayi kuma shuru a waje da muhallin da ba hayaniya ko kuma motsin kowa. Ko yanzun hakan yayi cikin office din,saidai qarar wayarsa ya sanyashi miqa hannu ya lalubota don yasan ring din na daban ya sakawa kiran don kirane da yake buqatarsa

"Sir........yana gidan caca na green card"

"Good" Ya fada a nutse yana bude idanunsa

"Don't let him go.....ina buqatar information na wuninsa na yau gaba daya"

"Yes sir" Ya furta cikin girmamawa. Wayar ya ajiye,sai ya miqe a nutse ya zauna ranshi na wani mahaukacin baci. Ga wani zargin ya sake shigo kasa akan mikail yanason kore uzurin da zuciyarsa keson bashi. Muddin ya kuskura bincike yazo masa caca yayi da kudinsa na halal tabbas!,zai nuna masa ainihin kalarsa......zai gane waye zahirin muhammad jadda. Dukiyar da aka tarata da gumin halak?,dukiyar da ake takatsantsan wajen jefa haram a ciki komai qanqantarsa?,kudin ruwa da ruba dukkaninsu haramtattu ne a cakudasu cikin dukiyarsa,amma yau din zanyi ganganci ko kuskuren zarar halalinsa ya jefa a qazantaccen guri irin wannan?.

Tsam ya miqe,sai ya koma saman table dinsa ba tare daya sanya takalma a qafarsa,ya kunna system dinsa ya tattara hankalinsa akai.

Karo na kusan goma barau ya kalli kawu sama'ila kaman yadda mato ke zaune yana murmushi daga gefan mikail yana kuma tayashi lissafin maquden kudade da dukiyar da yaketa cinyewa ta abokan bugunsa.

"Sama'ila?,dama wannan shine hasashen naka?". Murmushi kawu ya saki yana karkacewa kaman abun ya masa dadi

"Gaskiyar kenan barau.....amma barshi ya gama iya tasa dabarar......uwayensa na nan zuwa su koyar dashi darasi" Wata dariya barau ya saki bayan ya gama fahimtar abinda kawun yake nufi

"Yanzu naji batu,amma ta yaya muna da kai zaka bari wannan jaririn yazo gidanmu ya cimu wasa?" Murmushi ya sake saki idanunsa akan mikail daidai sanda ya cinye alhaji wada miliyoyin kudi

"Talala ce me kaman sake.....barshi ya gama karbarmin kudaden tukunna da gidajen" Dariya barau ya sake saki harda buga qafa.

Cikin awa uku ya daurewa kowa jijiya a wajen. Cikin tumbatsa da izza mato ya miqe

"Akwai wani sauran wanda zai kara da sarki?" Yayi shela yana ji a ransa sun gama da kowa,babu me sauran motsi. Shuru ne ya biyo baya,sai ya sake maimaita tambayar yana duban kowa d'ai d'ai

"akwai" Barau ya fada da qarfin murya. Mato da mikail din duka suka waiwaya suna duban kawu dake qurya,sai suka dubi juna tsakanin mato din da mikail

"Waye kenan a cikinku zai shiga?" Tsam kawu ya miqe yana nuna kansa

"Nine" Ido suka hada sai suka bushe da dariya tsakanin mato da mikail

"Qaraso mana dattijo....koda yake ba dattijo a nan......inajin akwai rabona a jikinka ne kaima.....ko giya ta kwana daya na sha da canjinka". Boyayyen dariya kawun ya saki,ya fara takowa zuwa wajen kowa ya zuba masa idanu yana mamakin qarfin halinsa,kamar ba'a gabansa aka cinye kowa ko ba amma shi zai jefa kansa?.

"Dame zaka shiga?" Ya jefa masa tambayar a raine. Karkacewa yayi ya zaro wasu takardu yana dubansu. Takardun dake dauke da sunan alhaji aliyyu ahmad zaki......mahaifi ga sabreen..... Takardar dake matsayin mallakin magadan kuma marayan yaran da yayi Qundumbalar shiga cacar da ita,cikin jin cewa zata ciyo masa tarin maquden kudaden da zasu zame masa silar arziqinsa gaba daya.

Saman teburin ya aza takardar yana kallon mikail,hannu ya sanya ya dauka ya duba ya karanta ya kuma tabbatar original ce wanda gidan ya haura miliyoyin kudi

"Ashe.....kudinka baaba ai ya haura 'yan canji ma ai.......idan na samu nasarar cinye gidan nan ko?,rusheshi zanyi na maidashi gidan shaqatawa,ayita shigomin da 'yammatan unguwa ina hutawa dasu ina biyansu".

Wani abu ne ya cakewa kawu a rai,ya tsani zina,ya tsani harkar neman matan banza,kaman yadda ya tsani shaye shaye,barshi kawai da cacarsa data zame masa masifa wanda dama tana da shiga jiki. Kai tsaye yaji tsantsar cin fuska ce ya tanadeta zaiyi musu wannan ya sake aza wutar qaimi a zuciyarsa,ya karkace kaman yadda yakanyi a yanayi irin wannan,ya kalli Mikhail da kyau

"Idan dai har ya zama mallakin naka kana da wannan damar" Ya bashi amsar da wani irin kakkaifan kallon dake gaya masa kai tsaye na SAI NA BAKA DAMAR CINYE GIDAN SANNAN ZAKA AIKATA HAKAN.

Izza da jin cewa zai samu nasara akan kawun ya sanyashi ninka abinda kawun ya zuba shima ya zuba cikin cacar aka fara buga wasan. Tashin farko kawun ya maido takardun gidan yayi tafiyar ruwa da kudaden da mikail ya zuba,abinda ya jawo hautsinewar wajen,hankula dukka suka komo wajen,aka fara yo dafifi,wadanda aka cinye suke alhini dukansu karsahinsu ya dawo,sai aka fara zuba sabon wasa.

Da daya da daya ya dinga zuba abinda ya ciyo kawu sama'ila yana kwashewa. Duk abinda ya zuba kawun ya cinye shaidan zuciya da kuma mato saisu gaya masa ya sake zuba wani,zai iya yuwuwa ya samu nasarar dawo da abinda aka cinye masa a baya.

Tafi tafi cikin qasa da awa biyu sai gashi yana tashi daga Mikhail me manyan kudi yana komawa asalin mikail dinsa kaman yadda ya shigo wajen. Cikar awa biyu cif komai ya qare!.kawu sama'ila ya wawushe duk wata kadara daya cinyo daga wajen wasu ya zuba!,ya koma tsurar yadda ya shigo musu a wajen!.

Sowa ihu murna da tafi ya cika wajen,ainihin sunan kawu sama'ila na teburin ya soma dawowa bakunansu wato DA BANBANCI!.

Kowacce tsiga ta jikin mikail zubawa takeyi. Idanunsa sun kada sunyi jazur,jijiyoyin kansa sun fito rada rada. Sosai yakejin ya muzanta,ya toxarta. Ta yaya zai bari wani qaramin alhaki tsohon daya bashi shekaru masu tazara ya kafa tarihi a kansa?,tarihin da muddin ya bari ya tabbatu a haka.....to ko shakka babu ya xubar da kimarsa da kwarjininsa a idanun abokan cacarsa dake bashi wani irin girma. Karon farko a rayuwarsa da wani yayi nasara a kansa,shi kuwa ta yaya zai bari haka ta tabbata?.

"Ga wasu kudaden na zuba.....azo a sake zama!!" Ya furta da qarfi,sautin daya sanya wajen yin dif aka zuba masa ido.

Da sauri mato ya kalleshi,ya kuma ja hannunsa da qarfi yana dubansa qasa qasa

"Wanne kudi kuma ya rage maka indai ba motar da mukazo a ciki ba zaka saka?"

"Qyaleni mato.....bakajin habaicin da suke yada min?,dole na aje musu tarihi,dole sunan mikail suma yaci gaba da wanzuwa a kunnuwansu da bakunansu da wajen cacarsu".

"Wanne kudi ya rage maka?!"

"Ragowar abinda aka bari a asusun jadda" Ya fada yana jin zuciyarsa ta qeqashe,kuma tabbas wannan kudin xai dawo da sauran kudin da duka narke,duk kuwa da yasan mugun gangancin dake cikin aikata haka.

"Kada kayi haka!" Mato ya fadi a gigice.

"Anma yi" Ya amsa masa ba fargaba ko shayi saboda ya bawa kansa tabbacin shine keda nasara.

Wayarsa ya fidda yabi dukkan process yayi transfer kudin da suka rage zuwa account din wanda zai ajiye kudin,idan nasara tasa ce ta dawo masa,idan ta kubce kuma dukka kudi sun tabbata mallakar KAWU!.

Daidai lokacin da akayi alerting mutum biyu fitar kudin,sai fuad dake zaune yana bibiyar komai ya lumshe ido yana sauke siririyar ajiyar zuciya,daidai sannan kuma kira ya shigo masa. Ko daya duba sai yaga daga department din da aka kira ya daga yana cewa

"Just keep an eye on it,naga komai" Sai ya kife wayar yana maida dubansa ga allon system din yana qoqarin tracking account na wanda aka sanya kudin.


*_TURQASHI....QAQA QARA QAQA,BAZANCE KOMAI BAπŸ˜‚πŸ˜‚.....amma akwai ZAZZAFAR TURKA TURKA FA.....MUJE ZUWA_*

*HUGUMANKU CE*


*D U N I Y A T A*

*_H U G U M A_*

Page 82

A wannan karon......daga shi har kawu samaila sai da aka basu hutun mintuna ashirin,don kowannensu yayi iya shirin da zai qara yi. Magoya baya kuma jingima kawun ya samu,wanda kusan dukkansu suna murna ne da nasarar daya samu,don sun tabbatar cewa koda basu maida dukkan abinda Milakil yaci nasu ba,to tabbas kawun zai maida musu wasu abubuwa kasancewar shi din nasu ne.

"Me gida......ka tsaya iya waccar asarar da kayi......kada kayi kuskuren sake yin wani ganganci......ka fini sanin waye muhammad jadda"

"Sosai kuwa mato.....amma jikina yana bani nasarata tana tare dani wannan karon......bazan bari nayita asara ba" Ya amsawa mato cikin yanayin da yake alamtawa mato cewa mikail din yayi nisan da bazaiji kira ba.

Cikar mintuna ashirin aka sake zama,zaman daya dauki sabon salo ya kuma dauki hankulan kowa dake wajen. Tsahon wasu mintuna ana fafatawa,inda daga qarshe komai yazo qarshe. Kawu samaila ya sake wawushe kudin,ya kuma bar mikail cikin wani irin yanayi tsakanin mutuwa da rayuwa.

Dukka kururuwar murna da muryoyin abokan kawu samaila dake tashi a wajen baya iya fayyace komai. Abu daya kwanyarsa ke iya fahimta gami da maimaita masa

"An qarasa cinye kudin jadda diamond resources,ba abinda yayi saura".

Kowanne sashe na jikinsa ya dauki rawa da wani irin kalar tashin hankali mara misali. Yana jin komai ne tamkar yana mafarki.....yana ganin kamar xai farka ko zai tashi,yana ganin kamar ba haka bane har sai daya damqi hannun mato

"Mato da gaske ne?,ko mafarki ne?"

"Da gaske ne maigida......ai na gaya maka dama". Taga taga mikail din yayi zai fadi mato ya taroshi,jama'an dake kusa suka kuma karanci hakan suka kawo masa dauki ta hanyar tallafe masa mikail din suka zaunar dashi suna masa sannu

"Kaima banda abinka oga ai kayi wauta.....hausawa sukace idan bakasan gari ba saurari daka......na tabbatar rashin sanin waye sama'ila ya sanyaka sakin jiki dashi kan teburin caca......amma ita dama yau gareka ne gobe ga dan uwanka,idan an sake wani zaman ta yiwu ka samu nasarar maido wani abun naka"

"A wajen wa?......lallai garba ka manta waye sama'ila ne" Dan uwansa da suka kawo daukin tare ya fadi yana murmushin aikin gama ya gama.

"Kaini gida mato.....mu fita daga nan" Mikhail ya fada kaman wanda ya hadu da ciwon makanta,don gaba daya sai yakejin wajen ya matse masa ainun,kai......kamar ma baya shaqar numfashi yadda ya kamata a wajen.

Tsoro fargaba da mutuwar jiki suka saukarwa mato sanda ya tayar da motar da yake tunanin ita daya ce Allah ya mantar da Mikhail bai sanyata tsaiwa takarar na ciyo ko a cinyeni ba wato caca. Kuka rurus mikail ya fashe dashi. Yana ji har a cikin zuciyarsa bashi da wani sauran abinda ya rage masa,to wai shin idan baiyi kuka ba me zaiyi?.

Yana hango kawai yadda zai qare sauran Rayuwarsa ne a gidan kaso......yana hango yadda me jadda zai qarasa murqusa Rayuwarsa bayan rasa dukkan wata dama daya fara jiyo qamshinta a baya. Ba shakka fateema ta cuceshi.......har a zuciyarsa yana jin inda zai iya ido hudu da ita a yanzu babu abinda zai hanashi hallakata.

Sun dan dauki lokaci da malam suna hira tana ta juya yadda zata gaya masa batun tallafin data kawowa dalibansa da rabon jarin da takeson yiwa duk wanda ya isa munzali a cikinsu. Cikin kudaden tanaso ta yiwa malam din alherin kudaden da zasu taba rayuwarshi sosai. Sosai mutumin yake burgeta........namiji na farko baya ga mahaifinta da taji dabi'u da halayensa sun mata,namiji na farko da takeji nagartarsa ya mata......kuma namiji na farko da idan ta zauna suna magana dashi takejin kamar wani sashe na mahaifinta ne ya dawo duniya.

Duba da yadda lokaci yake qara tafiya,ta tabbatar qanqanin lokaci ya rage ya fita don yin sallar magariba. Sai ta daure ta gyara zamanta.

"Magana nazo muyi malam,saidai bansan yadda zaka karbi abun ba" Ta fadi kanta sunkuye a qasa.

"To ina jinki mana aminatu.....lafiya dai ko?" Zamanta ta gyara tana jin nauyinsa da kuma kwarjininsa yana ratsata

"Eh lafiya malam......akwai tallafi ne da wata qungiya ta sa kai ta kawo don a rabawa makarantun tsangayu..... To banyi qasa a gwiwa ba na sanya sunan makarantarka a ciki,don nasan akwai dalibai da qarfinsu ya kawo kuma suke da buqatar sana'a......hakanan kaima malam na saka naka sunan a ciki......an kuma dace sun bada kaso me tsoka"

"Toooo.......ikon Allah" Ya fada a tsanake yana nazarin abun

"To sannu da qoqari,Allah ya saka da alkhairi......to sudai yara ba za'a hana raba musu jari ba......saidai komai zai zama bisa tsari don kada su saka a gaba su cinye.......kuma tallafar Rayuwa ne don bakasan ta sanadin jarin abinda Allah ya hukunta wani zai zama ba......amma zaki raba musu da kanki......hakanan zaki rubuta da kanki......batun sunana da kika saka ni na yafe....na gode miki da dukka qoqarinki a kaina.......amma basai kin bani komai ba".

Shuru gurin yayi,qasan ranta tana jin wani abu maras dadi. Har ga Allah malam uba ta daukeshi........tana masa kallo ne irin na d'a da uba......to amma kuma tasan halinsa,ba kasafai yake canza hukunci ko magana ba idan ya zartas

"Lokaci yana gabatowa,zan fita na shaida musu su zama cikin shiri.....wanda kuma yasan baida sana'a kar ya shigo ciki"

"Hakan ma yayi malam" Matar malam din ta amsa masa,sai ya dauki butarsa da rumasa'u ta cika masa da ruwa yana ficewa.

Yammaci lokaci ne da kowanne ma'aikaci yayi handing over aikinsa na ranar......ya kuma tattara ya nasa ya nasa yayi guda ko kuma guraren da mutum keda ra'ayin zuwa.

Company din yayi tsit.....don hatta da masu danyin late kafin subar office din a yau sun fice,ba kowa sai muhammad fuad......saddiq da musaddiq ke zaune saman sofa,jifa jifa yana daka kansa ya kalli muhammad fuad da yaketa aiki haiqan saman system tamkar a nan zasu kwana ko bashi da niyyar barin office din a yau.

A hankali ya zare idonsa daga system din ya maida saman agogon dake daure a tsintsiyar hannunsa. Mikhail ya fado masa a rai,sai ya jijjiga kai a hankali ya maida dubansa ga musaddiq. Idanu yadan zuba masa kadan yana jin tausayinsa yana saukar masa. Ya tabbatar a gajiye yake,kuma bashi da burin daya wuce ya wuce gida,saidai kuma komawarsa gidan a yanzu babban hadari ne ga lafiyarsa dama rayuwarsa.

"Mu qarasa gidan malam muyi sallar magariba a can" Ya fada yana dan ture table din gabansa ya kuma miqe yana ware hannun rigar suit shirt dinsa daya nannade,sannna ya juya yana dauko suit din yana qoqarin maidawa.

Suna hanya kadan kadan yana jin saddiq da musaddiq din suna hira abinsu jifa jifa.....yayin da shi kuma ya tattara nasa hankalin kan wayarsa yana rage saqonnin da bai samu dubawa ba.

A zahirin gaskiya ya gaji,yana kuma buqatar hutawa ne daga gangar jikinsa har ma qwaqwalwarsa,to amma ya sani.....a cikin matsalolin dake cunkushe cikin kansa,muddin zai zauna na second biyar shuru tunanukane zasu addabeshi,wanda yayi imanin zasufi jigatashi fiye da gajiyar da yakeji yanzu haka a jikinsa.

Kamar kowanne lokaci malam din bai taba karbar komai a hannunta ya eabawa daliban da kanshi ba,yau ma ita da manyan dalibansa ya bawa dama suka tattauna,ta kuma rarraba kudin da zata raba musun sannan aka tsimayi sauran wadanda basu kusa suka dawo aka soma hawa layin karbar tallafin.

Har qananun cikinsu bata tsame ba,saidai kowanne tayi kudin girma girma,adadin na qananu daban,na manyan daban.

Ita da rumasa'u suka fito zuwa rumfar gaban gidan malam din,rumasa'u na riqe da jakar tana miqo mata,ita kuma tana miqa musu. Duk wanda ya karba sai ya balbaleta da adduar data dinga sanyawa tana jin saukar wani irin sanyi cikin ranta,wannan ya qara mata qwarin gwiwa taci gaba da binsu da kudin daya bayan daya.

Kaman yadda ya saba a kowanne lokaci ya sanya mota uku cikin motocin dame tsaron lafiyarsa tsaiwa su kuma jira fitowarsa daga ainihin bakin titin unguwar,motoci hudu harda tasa suka fara gangarawa zuwa ainihin layin gidan.

Suna shiga yana ci gaba da duban tsari da yanayi da banbancin unguwanni da al'umma ke rayuwa a ciki. Unguwannin da suke buqatar tsari me yawa da kuma tallafi don samun daidaiton rayuwa.

Kusan dukkan guard's dinsa har yanzu suna mamakin yadda yake zuwa unguwar lokaci lokaci. Ko tsoron lafiyarsa baya yi baya kuma duba girman

Chapters

Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login