Showing 249001 words to 252000 words out of 325075 words

Chapter 84 - SARAN-BOYE COMPLETE

20 Jul 2024

29165

ranar akai barci kowa na ?arshen gado. Washe garima ta?i kulasa shima ya shareta. Sai daga baya yaso su shirya ta?i. (A raina nace hummm Yoohan bakasan kafiyar Aymah bane ba).
Wannan tuburewar tata ya ?ara bashi haushi. Harya yanke shawaran ta shirya ta koma Nigeria tunda bazataji lallashinsa ba.
A mamakinsa kuwa sai yaga ta hau ha?a kayanta. Dan itafa tabbas tayi al?awarin bazata sake zama inuwa ?aya da Solomon ba. Dan tsaf ta gama fahintar wannan nanema Yoohan ?in da yakeyi akwai wata a ?asa. tabbas da gaske akwai abinda su papa suke ?oyewa game da Yoohan ?in. Inba hakaba minene na nana masa guard a duk inda yake. Sannan sau biyu tana kama Solomon na waya da papa. Na farko yare taji yanayi sai turancin daya saka ka?an ya sakata fahimtar papa ne. na biyu kuwa da turanci sukai magana. Hakan ya sata jin komai akan duk wani motsinsu Solomon yana sanarma papa. Dan a ranar shi papan har maganar ya kamata ta koma Nigeria yayma Yoohan. Amma shi Yoohan ?in ya nuna baya bukatar yana wani ?asa matarsa na wata ?asa. A ransa kuwa ya ?au alwashin Aymah bazata ?ara zama a gidanba baya kusa saboda Gebrail. Dan ba ?yalesa yayiba. ya ?au alwashin duk randa ya dira Nigeria sai Gebrail ya yabama aya za?inta.
Ganin da gaske shirin tafiyar take ya sakashi sakkowa daga fushinsa shi. Ya fara lallashinta amma ta?i saurarensa. Saima kuka da take masa mai cin rai. Daga ?arshe dai dole ya kira baba malam akan dan ALLAH ya lallasar masa ita. Dan shikam a yaune ya kuma tabbatar da borin Aymah bana wasa bane. Dan ko abinci ta?i ci, ta?i shan maganinta. ta birkice masa ita kawai ya kaita airport ta wuce gida kokuma ta tafi da kanta.
Murmushi baba malam yayi kawai yana girgiza kansa. kafin ya sauke ajiyar zuciya ya farama Yoohan nasiha. Daga ?arshe ya koma masa fa?a akan sakacinsane ai ya saka Nu'aymahn iya bijirema umarninsa. Dan haka ya nutsu sosai wajen ri?e gidansa da ?yau. dan su mata wani lokacin zuma ne sai da wuta. Sannan wutar kara ne sai da iji. Ba'a sakaci da su sannan ba'a musu tsauri da yawa. ana ri?esune tsaka tsaki sai a samu jin da?in duniya.
Sosai Yoohan yaji shawarar sirikin nasa. tare da ?arajin ?aunarsa a cikin zuciya da ?argo. Daga haka ya ha?ashi da Nu'aymah kamar yanda ya bu?ata.
Zata fara masa kuka baba malam yay mata jan ido. fa?a sosai yay mata akan tashiga hankalinta mijinta ba abin rainawarta bane. Idan batai wasabama sai yazo har Austria ?in ya hukuntata. Sai da ya tabbatar tayi laushi sosai da fa?ansa sannan ya koma yimata nasiha. Daga baya kuma ya bu?aci jin dalilinta na takurawa akan Solomon ya barsu.
Kasancewar Yoohan yana koyon hausa a wajenta ya sakata yin amfani da manya-manyan hausa wajen yima baba malam bayani akan abinda ta fahimta da zaman Solomon tare da su. Ta kuma bashi labarin abinda ya faru akan maganar hoto, harma da videos ?in da Omar (Richard) ya nuna mata kwanakin baya da suka shu?e. shi kansa baba malam ?in hankalinsa yayi matu?ar tashi. sannan zarginsa ya fara zama gaskiya kenan. Albarka ya saka mata sosai da fa?an rashin sanar masa zance hoton da tayi tun a wancan lokacin. Duk da ya fahimci mijinta take son bama kariya akan matsalar da gajeren tunaninta ya kasa fa?a?a mata. Yace,
"Mamana yanzu ina hoton yake?".
Hawayenta ta share da jan majina. Tace, "Abba yana nan Nigeria a cikin kayana".
"Masha ALLAH. ALLAH yay miki albarka. Saka wani ya ?akkosa bazai yuwuba. Dan haka zamuyi ha?uri har ku dawo ?asar sannan musan ta inda zamu ?uloma al'amarin. Batun Solomon kuma bata hanyar rikici zaki yakicesa a jikin mijinki ba. Cikin hikima da wayon da ALLAH ya baku na mata da tarbiyyar Umm ?inki zakiyi amfani wajen sakashi ya sallamosa. Ko kin ta?a ganin muna rikici da Umm ?inki ne a gidannan?".
Kanta ta girgiza masa tamkar tana a gabansa. Sannan tace, "A'a Abba".
"To amma shine ke zakije kina rikici da mijinki. har yana taroki kina ?wacewa? Wannan shashanci ne ai. Sannan kina zubar mana da kimar tarbiyyar da muka baki. Mu mazafa da kike gani munada wuyar sha'ani dason nuna mulki a gidajenmu, shiyyasa duk macen data fahimci haka ta iya zama damu mutane suke ganin kamar ta mallake mijintane nanko ba haka baneba. juriyace kawai da iya zama da mijin tayi. Ki kula da ?yau. Mahaifiyarki abin koyice a gareki akan zaman takewar aure. Babu wanda zaice ga Jannat da wata matsala a gidan aurenta. da da?i babu da?i ta jure ta shanye komai. Yaya muka kwana yaya muka tashi ta jurema ranta. har takai wasu na ganin tsorona takeji da yawa. Nanko ba hakan bane. Mune muka san sirrin kammmu fiye da duk wanda ke zagaye damu. Karna ?arajin haka kinji ko?".
Nu'aymah na sharar ?walla tace, "Insha ALLAHU Abba bazaka sake jiba".
"To Alhmdllh naji da?in hakan kuwa. ALLAH yay miki albarka keda mijinki damu baki ?aya".
Cike dajin kunya ta amsa da amin. Daga haka suka ajiye wayar. Ta ?an saci kallon Yoohan dake kwance ciki sofa idanunsa a lumshe tamkar mai barci. Tashi tai a hankali taje ta ajiye masa wayarsa a saman ciki batare datace komaiba.
Shima bu?e idanu kawai yayi ya bita da kallo harta shige toilet.

_________¡ï¡ï

Batare da tasan yaya zancen Solomon ya kasanceba washe garin da suke cika sati biyu. ta kama randa zasu bar ?asar kenan. Bayan sun kammala shirinsu tsaf sukaje asibiti aka ?ara tabbatar da ingancin lafiyarta, sukai sallama da su Dr Sophia kuma. Yoohan ya ?ara siya mata sauran magungunanta suka nufi airport cike da kewar ?asar Austria da garin Vienna. Harma da mutanen cikinsa.
Yanzunma suna nane da jelar tasu Solomon. Sai dai kuma suna zuwa Airport ta fahimci Solo Nigeria ya nufa. ita da shi kuwa U.S zasu wuce dan Yoohan ya koma hutu. Zai kuma gudar da wani aiki a ?asar United states ?in, da wani taron manyan likitoci da zasuyi kuma insha ALLAH.
Duk da basu shiryaba har yanzun ita da shi sai da ya ga farin cikin komawar Solomon 9ja a fuskarta. Shidai hakan na bashi mamaki. dan ya gaza fahimtar ?iyayyar dake tsakanita da Solomon. Shi kansa Solo ?in ya kula baison Aymah. Sai dai baya iya nunawa a gabansa saboda shakkarsa da yakeyi. shi kuma bai ta?a nuna masa ya fahimta ?inba dan yanason aje inda zai taka masa birki akan matarsa.
Shi kansa Solomon sai da sukaje airport ya fahimci Nigeria zai komai. Gashi babu damar kiran papa ko madam Chioma dan suna a tare. Sai dai zuciyarsa na ?ara jin zafin Nu'aymah. Dan ransa ya basa itace sanadin komawar tasa tabbas. Musamman da yaga yanda taketa faman moso. Dan ya fahimci kwana biyun nan daga ita har ogan suna cikin rikicine ko damuwa oho bai gama tabbatarwaba dai.
Jirgin su Solomon ne ya fara tashi zuwa Dubai. daga can zai hau Jirgin Nigeria. Ya tafi cike da alkairin da Yoohan yay masa da takaicin Nu'aymah da tsana mai tsanani. Dan shi baimasan ina zasujeba a yanzu haka. Solomon na wucewa da kamar mintuna ashirin da biyar suma nasu jirgin ya ?aga zuwa U.S. yana ta wajen Window tana gefensa a cikin jirgin. Sai dai ya ?auke fuska a binsa gashi ya ?aureta tamau. Daga ?arshema saiya kunna lap-top da li?a earpiece a kunne ya hau kallon film. Duk da ran Nu'aymah ya sosu saita fuske tai kamar bama tasan da zamansa a wajenba. Koda akazo tambayarsu mi zasuci catai bata bu?atar komai. Shi kuma yasa aka kawo masa coffee da biscuits.
Lokacin da jirginsu ya sauka a U.S Nu'aymah barci takeyi. Hakan yasaka Yoohan shafa mata fuska. Sai dai tana bu?e ido ya ?auke kansa tamkar bashine ya aikataba. Itama duk da ta fahimci shine ya tadata sai ta watsar da shi ta basar. Handbag ?inta ?ar ?arama kawai ta ?auka tai gaba. Shi kuma ya jawo trolly ?insu sai lap-top bag ?insa a hannu. Yana biye da ita a baya. Sai dai da suka sakko dole ita ta koma bayan nasa dan ba sanin hanya tayiba. Da wannan damar ta ware ido tana kallon airport ?in daya amsa sunansa airport. Sai dai ta ha?iye mamakinta a rai wai kar Yoohan ya rainata da ?auyanci??.
Taxi ya ?auka musu drop. Koda suka shiga nanma dai kanta naga Window tana kallon birnin da mutanen cikinsa. Daga haka suka isa wani ha?a??en gida daya amsa sunansa gida. A tunaninta gidan nasa ne. sai dai batasan haya ya kama musu ba dan a yanzun baya bu?atar zaman hotel ?in da ita. sannan yanason barinta anan U.S ?inne dan yasan bazai yuwu yayta gantali da ita duk inda yakeba. Inba wajen daya san zai iya yin sati biyu kwana goma ko sama da haka ba. Amma kamar tafiyar kwana uku ko biyu zuwa sati ?aya zai iya barinta yaje ya dawo. Inba dai bu?atar tafiya da ita taga duniya tasa suje tareba.
Komai da zasu bu?ata na gida akwaisa a cikin gidan. Shopping ?in abinci kawai zasuje suyi da kansu saiko suturar sakawa da sukazo da kayansu. Harga ALLAH gidan ya matu?ar burge Aymah harta kasa ?oye shau?in hakan a zahiri.
Duk da yaji da?in yanda tai farin ciki sai ya basar bai nuna mataba. Ya fara shiga ko'ina ya duba gidan da ?yau. Sai da ya tabbatar komai ya masa yanda yake bu?ata tamkar yanda ya gani a yanar gizo daya kama gidan sannan ya shiga wanka.
Yana fitowa Nu'aymah dake kwance a gado ta mi?e itama ta shiga dan wankan take bu?ata itama saboda gajiya. Koda ta fito zaune ta samesa a bakin gadon yana musu order ?in abincin ta wayar landline. Da alama dai gidan abincin yana kusa da sune, kokuma yanada ala?a da masu gidan abincin dama can.
Sai gashi kafin ta gama kimtsawa tai sallar magriba da lokacinta ya shiga an kawo abincin. Shine ya fita ya amso. Sai dai bai dawo bedroom ?inba yay zamansa a falo. Sallama acan yay abinsa.
Wani mahaukacin yunwa Aymah takeji. Hakan yasa bayan ta idar da salla ko hijjab bata cireba ta biyosa falon. Dan bazata iya basar da cikintaba ta halaka a banza a wofi. Turus tayi tana binsa da kallon mamakin ganin yanda ya baje yana ?ora abinci a cikinsa. Ta kumbura baki ?walla na cika mata idanu. Cike da fushin data koya kwana biyun nan ta juya zata koma bedroom ?in. Sai dai kuma caraf taji an ri?i mata hannu. ?o?arin fisgewa ta farayi hawayen da take ri?ewa na zubo mata a guje saman kumatu.
?aukarta yay gaba ?ayanta ya dawo da ita a falon. duk yanda take watsal-watsal da fa?in ya sauketa bataso bai kulataba. Ya zauna cikin lallausar zagayayyar kujerar da aka ?awata falon da ita kalar royal blue tana a jikinsa. Cikin hawayen da takeyi ta shiga kaimasa ?ananun duka a ?irji da fa?in ita ya saketa bataso. Tunda yabar sonta yaje ta ha?ura ta barma duniya dasu Miracle dake addabarsa da text massege kullum shi.
Zancen nata yaso bashi dariya. Dan haka ya lumshe idanunsa ya sake bu?ewa akanta yana ?o?arin ri?e hannayenta da take kaimasa duka a ?irji. A ransa kuwa yana sake jinjina rikicinta. Duk da ransa na raya masa wani abu game da saurin fushinta na kwana biyun nan. Sai dai bai tabbatarba dan ya san inma shine to ?aramine kuwa sosai.
Bakinsu ya ha?e waje guda. Tun tana turesa harya samu nasarar maida mata jiki la?was ta fara bashi ha?in kai. Da ga ?arshe ya ?auki abarsa cak suka shige bedroom inda zaiyi lallashi ?an gaske na zallar ?auna da babu gaurayen algus a cikinta??. Saiga mutuniyarkun muna funfun dake fa?in zata barma duniya dasu Miracle tai luf kamar bata gidan????.
(Su Aymah babu aji????)

Sai da suka gama wadata juna da farin ciki yanda ya kamata. Yoohan ya kalli Aymah dake lafe a jikinsa idanu a lumshe alamar barcin nata na ?a'ida zai ?auketa. Dan duk sanda hakan ta kasance a tsakaninsu sai tayi wannan barcin. Shiyyasa yake kiranta raguwa.
Guntun murmushi yayi da lumshe idanunsa ya sake bu?ewa a kanta tare da ja mata hanci. "Silly girl! Babu abinda ta iya sai jan mutane fa?a".
Lumsassun idanunta da basu gama washewaba ta bu?e a kansa. Sai kuma ta tura masa baki tana maidawa ta rufe tare da tirza ?afarta dake jikinsa tace, "Tab, kai wama ya kaika iya neman mutane fa?a".
Sake jawo bargon data zazzame da ?afa yayi ya lullu?esu da ?yau yana ?ara sakata jikinsa. "Nine ma mai neman fa?an kenan?".
"Sosai ma. Tunda ai kaine dai kasa akayi wannan fa?an".
Dariyar data bashi ce ta sakashin yin guntun murmushi. Ya sumbaci goshinta da la??anta yana sauke ajiyar zuciya da lumshe idanu. "ALLAH na gode maka daka mallakamin ?ar rigimarnan tawa. Tare da mai ramamin gashinan yazo".
"A ina?".
Tai tambayar cikin yanayin barcin daya figeta.
"Mi kikeci na baka nazuba, zaki gani ai". Ya fa?a yana mi?ewa zaune da ita a jikinsa. Cike da shagwa?a tace, "Ni wlhy barci nakeji".
"To muje ayi wanka, sai kizo kiyi Sweet girl ?in Yahya".
Da taimakonsa sukaje akayo wankan. Dan barcin da bataiba na bayan lobewa ne cike da idanunta. Suna fitowa kuwa ta zube a gadon ta fara. Kayan barci ya ciro mata yazo bakin gadon ya zauna yana kallonta na tsayin mintuna uku. Hannunta ya kamo ya na kallon tafin, kafin ya juya ya tsurama yatsun idanu suma na kusan minti ?aya. Ya mi?e inda ?afafunta suke ya dur?usa a gaban gadon yana kallon yantsun suma na tsayin mintuna. Sassanyan murmushi ya sauke da ajiyar zuciya, ya sumbaci ?afafun duka biyu sannan ya dawo kusa da ita ya zauna. Sake tsirama fuskarta ido yayi na tsahon wasu mintunan cike da so da ?auna, kafin ya ran?wafa kanta yana sumbatar bakinta da kumatunta, idanun har wuya. (Ni mai ?auka muku rahotonma sai yaban dariya. Dan na kasa fahimtar inda ya dosa????).
Kayan barcin ya sanya mata, ya gyara mata kwanciya, shikuma ya koma bayin ya ?auro alwala ya dawo yay zaman karatun al-qur'ani. Dan tunda suka fara rigimarnan ta Solomon kota ?ora masa karatun ba fahimta yakeba da ?yau. Haka yake kwata-kwata bayason damuwa. Koyaya irin haka ta faru da shi duk sai ya fita hayyacinsa. Ya jima yana duba al-qur'anin da sauran buks ?in kafin ya mi?e zuwa fallo ya tattaro abincin da yaci ya rage dan yasan saita tashi cin abinci tunda yunwar takeji. Kwana biyun nan haka take, batama abinci sau?i. Kodan jinyar da tasha ne oho. Sallaya ya hau ya kabbara sallar isha'i, bayan ya idan bai kwantaba ya ?auki wayarsa da tun ?azun yake ganin tana haske, ya tabbatar kuma kiransa akeyi dan a silent take.
Ilai kuwa missed calls ne na papa har guda takwas, sai na Momynsa biyar. Sai na Omar (Richard) biyu. Sauran kuma duk ba important bane a garesa dan haka baibi takansuba dan harda mayyarsa Miracle.
Kiran papa da Momy yasan bai wuce saukar Solomon Nigeria ba. Dan haka yay kiran Omar (Rich) kawai da shima yana Nigeria.
Sallama kawai Omar (Richard) ya amsa masa, ya shiga masa sha?iyanci wai yanzu soyayya tasa sai ya gadama yake amsawa mutane kira a waya. Su G-boy ma jiya suka gama masa tsogumi a wajen birthday ?in Osin da akayi a garin Lagos. Kai abokan suma da yawa sunyi wannan complain ?in duk da dama sunsan shi Yoohan fa bai cika ?aukar kiran da zuciyarsa ta raya masa mara amfani bane, saboda yanayin aikinsa da duk ya maidasa busy a gaba ?ayan rayuwarsa. Sai dai idan yana a cikin hutu da kansa yake bin abokan mu'amulat nashi masu muhimmanci ya kirasu su gaisa koda bazai zauna hira da kai ba. Musamman ma daya musulinta ?in nan ya ?ara sanin darajar zuminci.
Murmushi kawai yayima Omar (Rich) ?in da cewa "Humm ka samin ido da yawa". Dariya kawai Omar yayi da ga can. Dan ya fahimci ?an miskilancinne a kusa yau. Ajiye maganar wasan yayi suka fara tattaunawa kamar haka.
"X-man duk yanda muke tunanin aikinan bazai kasance mai sau?iba. Amma dai na turo maka dukkan bayanan dake a hannuna yanzu ta Email ?inka. Ni dai yanzu shawarar dana yanke, mizai hana mu sami wani amintaccen jami'in tsaro da zai taimaka mana akan case ?in nan. Dan tabbas sai munyi kutse a cikin


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login