Showing 222001 words to 225000 words out of 304363 words
lokacin da tambayanta waye zai turashi wani wajen don yai kudi dashi koshi Amadin har yanzu yarone kuma da za a turashi abu bai tashi yiba ?
Tace nasani umma tunda bai cikin hankalinshi daidai sai abinda akace yayi yakeyi yanzu komai ma ai yana iya faruwa a hakan yanzu.
Na daiga alaman nan gaba nice zaki kira da manya kan danki a gidan nan tunda yanzu idon ki ya bude uban kowa baki kunya ke yanzu don take takenki sarai naganeshi a gidan nan.
Yanzu dai umma nagane zance ina yarongane baki son in saka baki daga yau na dai kada kuma a fadi abinda bance ba gashi naji an fara fadi yamzu.
Sunyi hakan da kwana biyu cikin dare misalin shadayan dare sai gashi kamar anjefoshi daga sama mukaji sallaman shi nikan na rufe a lokacin saida Asmau ta kwankwas min kofa nace waye tace ki tashi ki bude yayane ya dawo.
Asmau kinsan fa idan nayi barci banason a tasheni don Allah kada ki dameni sai naji muryanshi yana fadin bude min kofan mana na shigo.
Jin hakan yasa na zabura da karfi na zo na bude kofan yana tsaye da suith baka daya balle aniniyar jikinta kina iya ganin farar riganshi dake ciki farinshi na asali ya fito fili sosai ya sake kamani a dan lokaci kankani da yayi batare damu ba ga kanshi yayi aski gashinshina fulani daya soma fitowa yayi kwace lup bakikirin a saman kan nasa gwanin ban sha,awa a lokacin..
Kallon shi nayi na dukar da kaina don nasan banda gaskiya na dance mai sannu da zuwa ya amsa min da yaiwa ki bude kofan can a shigo min da kaya ya fadawa Asamau din dake tsaye dauke da wani jakkar kayanshi a lokacin.
Yasa hannu ya karba daga hannun sister nashi nakai hannu zan karba a hannunshi yace no bar wanan in shiga dashi ciki tukunna.
Na jaye ya shige da shi zuwa uwar daka ni kuma na fita zuwa kitchen dina in duba ko akwai ruwan sayi a lokacin nayi sa,a na samu zan shiga dakin da ruwan muka hade dashi yake fadin wai har yanzu basu shigo min da kayan bane kome ?
Basu shigo ba na basa amsa a dadare ya fice da sauri daga part din zuwa wurinsu can naji muryanshi sama sama yana fada na saurara da kyau naji yana fadin ansan menazo dashi da za ace akawo min kayana nan idan na nan ne ai nan din zance su kawo dana shigo.
Muryan Dije naji tana fadin in,maba hauka ba mutum da matarshi yanzu za ace ai masa hakan ina ruwanku da abinda yazp dashi din tunda ko bamu gani ba zai kwaso ya kawo muna indai abin amfanine.
Ni wanga halin naku bansan inda kuka samoshi ba ace komai na yaro idonka nakai aiko akwai aiki ga hakan indai shi zaki koyawa yaran ki.
Nidai na ganshi da kaya niki niki yana shigowa dakin dasu bai ko tsaya shan ruwan dana aje mai din ba saida ya gama shigo da kayan kaf yace ruwane nan zan kaiwa drivern daya kawonine.
Naga ya fice da sauri na sake binshi da kallo karo na barkatai kamar a ranan na fara ganin shi a rayuwana don yadda yai min kyau a fuskana gaba daya ya canza min lokaci guda haka.
Ko kafin ya dawo na hada mai ruwan wanka na juyo ina kokarin harda wormer dina don akwai shinkafa da miya danayi na danci kadan na aje saida safe.
Sai gashi ya fado kwatsam sai nayi niyar gyara in kawo mai tunda dare yayi sosai lokacin naji daga bayana yana fadin mekuma zakiyi a kitchen yanzu.
Saida na dan juyo na kalleshi kafin ince dashi abinci nake hada ma sai naji yace ki barshi nazo da abinda zamuci don nasan kafin mu iso dare yayi sosai don haka na riko muna take away a hanya.
Yanzu wanka kawai nake son inyi ko zan danji dadin jikina ruwa na bayi na hadama ko na bashi amsa ina cire joni din wayan dana hada sai naji yace masha Allah .
Allah yai maki albarka yana kokarin cire nicktie din dake daure a wuyanshi saman riganshi ya wurga min saman kujera ya shige dakin kai tsaye.
Tattara kayan daya watsar nayi zuwa ciki na kwashi sauran na zuba wurin kayan wankin mu na kara gyara ko ina sai kamshin da ummah ta aiko min dashi da kannena sukazo.
Take dakin har falon ya dauki wani irin kamshi mai dadi har ya fito yana dube dube a cikin dakin baidaiyi magana ba ya bude inda kayanshi suke ya fito da wata jallabiyanshi fara ya saka ajikinshi bayan ya fesheta da turarensa da bantaba jin irin kamshinsa ba sai lokacin.
Falo ya fito ya sameni kwance saman dogon kujera na daga kaina sama ina tunane banyi aune da fitowan nasa ba saijin shi nayi ya zauna a kusa dani yana fadin wai Allah abin godiya.
Princess Zahra wai fushine kike da Prince din naki haka danayi laifin me har ake kin daukan wayana don ba a damu da rashina a gidan ba ke nan kome ?
Dagowa nayi niyar yi in bashi amsa sai naji ya dannena koma kwance a lokacin ne kuma yayi min rumfa da chest dinshi gaba daya ta yadda ban iya dagowa a lokacin.
Ga kuma numfashin mu yana dukan juna gaba daya jikinane ke mutuwa lokaci guda saboda yanayin dana kwana biyu ban ji irinsa ba kuma ban shigesa ba sai a yanzu din ya tuno min da wani abu.
Kokarin kai bakinsa a nawa yakeyi da sauri na samu na kawar da kaina gefe ina fadin da kyar baka fa rufe kofa ba baka gudun wani tashigo yanzu.
Wanda ya shigo nan yanzu gulma ya kawoshi dama don haka yaga abinda yazo gani ke nan a lokacin sai kawai ya cakumoni gaba daya lokaci guda dakyar na samu na kwaci kaina na mike da sauri cikin tsoro.
Ya bini da kallo yana kaiwa kwance alokacin tare da mayar da kanshi saman filo yana lumshe idon shi a hankali ya dauki hannunshi daya ya dora saman fuskanshi.
A wani irin kasalalen murya mai rauni ya furta Zahra nasan har yanzu fushi kike dani akan wayan mu na ranan ba zaki taba fahintana ba zahra don baki sannin a lokacin da nake kama da mahaukaci ba.
Lokacin da nake neman yan uwan da zasu tallafa min kona abincin na dinga samu wanan dalilin yasa kikaga ina mutunta malam Tanimu a garin nan har gobe.
Don gidansa kawai nakan dan samu ragowan abinci ko kanzo naci kafin na fita neman abinda ya kamata damu a gari tun ina dan kankani nake fita na nemo abinda zamuci do malam Ladan yana kwance a gida ba lafiya.
Malam tanimu shi yakan sani kwashe mai icce in tara komai yawanshi komai rana ko ruwa da iska ya dan bani kudi da zan soyo muna garin kwaki muci nida kakannina a lokacin.
Ina kallo kiri kiri kakana malam ladan ya yarasa ransa don babu wanda zai kaishi asibiti asan abinda yake damunsa a lokacin.
Gashi da yan uwa kin sani da suka fito ciki daya amma suna bakin ciki dasu taimakawa dan uwasu a cikin jinyar nan nasa dukkansu uku suka kara aure lokacin guda.
Har ya tafi yabar masu duniyan basu barmu da abinda yake damun muba kuma suka bullo da cewa wanan gidan gidan gadon sune a lokacin.
Sai naga ya girgiza kai ya dan lumshe idanunshi kafin yace ban iya mantawa da yadda Dije take kuka a lokacin amma mutanen nan basu tausaya mata ba saida Allah ya taimaka lokacin tsohon soja nada rai shine ya tsaya mata aka bar muna gidan nan.
Amma abin mamaki ashe duk wahalan nan da nake sha a duniya zahra mahaifina yana raye a cikin jin dadi da daulan duniya dashi da iyalinshi daidai da rana daya bai taba tuno yana da wani dan a wani gari ba ya yar dashi ga duniya .
Sai yanzu da rana tsaka Allah ya fara yaye min wahala zai bulo yace wai yasan da zamana a matsayin dansa na yarda sam wanan ba zai taba yuyuwa a gareni ba gaskiya.
Jin hakan daya fada yasa na dan tako daga inda nake tsaye na tokare bayana da bangon shiga kuryan mu ina sauraren bayaninshi na baya da yake fada in brief cikin bacin rai a lokacin.
Zama nayi a tsakiyan kujeran da yake kwance a kai duk da ban zauna da kyau sosai ba a lokacin don yana kwance mike na fara fadin.
Haba master kada ka zamo cikin muranen da basu yarda da kaddaransu ba har ka fadi jerabawan ka da Allah ke gwada imanin ka akai mana.
Ya dawo gareka yayi nadama sun nuna fitar masa da hankalishi akayi gareka duk dadewan nan yasa bai taba neman ka ba sai yanzu wata kila abin kuma ya karyene a kansa din.
Dan yunkurawa naji yayi yakai hannunsa tsakiyan marata ya dan tausa kadan yana fadin ki bini kawai yadda na bisu shine alheri a gareni yanzu.
Da zaran na nuna zumudina akan ganin shi ba zan taba tasiri a zuciyanshi har ya tuno da irin wahalan danasha a bayansa ba bance bashi bane mahaifina naji na karba mahaifinane shi har abada amma ba yadda yake zaton zanyi zumudi akanshi ba don yana da kudi har gobe na tsaya a inda Allah ya ajeni bankai kaina garesu ba balle su kara fitar dani daga rankowa.
Kadaibi sannu don hakkin mahaifa kada Allah ya tambayeka hakan don ya nuna nadamarshi sosai ga Dije da sauran kakaninka da aka zauna din.
Cikin wani irin dagowa yace wasu kakanina ke nan aka zauna dasu nace su malam Bawa mana da sauran mutanen gidan kaf sukazo nan aka zauna dasu.
Kai duniya ina zaki damu yanzu su basuji kunyan zuwa akan zancen naba harsu zauna don mahaifina yazo ?
Mutanen nan fa Zahra sune suka fara shegantani cikin garin nan har sauran mutane suka dauka hakane nidin shegene banda uba sai naji yayi shiru bai sake magana ba ashe hawaye yakeyi a lokacin.
Wani irin kuka mai ban tsoro akuyan nan nasu ta sake lokaci guda saida na dan kadu ina fadin innalillahi bana son kukan akuyan nan wallahi .
Don da zaran tayi shi hakan na nufin wani abune mai muhinmanci zai faru a gidan nan na rigada nayi marking dinta da hakan a raina na fada kamar ina sambatu .
Ji nayi ya jawoni ya kwantar a samar kirjin shi muryan shi da tanayin da yai magana yasa na fahinci kuka yakeyi a lokacin yana fadin.
Kwarai kuwa ba sani don uwar garke kamar aljanna take yanzu abubuwanta na al,ajanini idan tayi sai me hankali yake gane hakan nariga nima nasan da hakan gareta.
ZAINAB IDRIS MAKAWA[6/19, 8:05 AM] Mmn Bibo: 🌱TUMFAFIYA UWAR KWANKWANMAI ,,,,,,,,,,
🌱TUMFAFIYA BAKI FITA A WURIN BANZA ,,,,,,,
🌱TUMFAFIYA SIRIN KI SAI ALLAH ,,,,,,,,,,
ZAINAB IDRIS MAKAWA
7️⃣7️⃣
ONLINE PAID NOVEL YARUWA KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMA DARI BIYAR NE DON KIRA 08036959257 KO BIYA KI AIKA 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KATIN WAYA MUN GODE UBANGIJI YA BAKI IKON BIYA AMIN,,,,,,,
Kuka akuyan ta karayi a cikin wani irin sauti mai ban tsoro zakace wani kosasashen dabba ke kukan kafin yan uwan suma su dauka a lokaci daya .
Zakice sunga wani abune ko wanine yazo wurinsu yadda suke kukan gaba dayansu dan kokarin yunkurawa naji yanayi zai dago daga kwancen da yake din.
Jin hakan yasa na dan daga daga jikinshi din ya samu yakai zaune lokaci daya yana fadin Allah sarki nasan muryana sukaji suke wanan kukan gashi dare yayi balle na zagaya wurin su.
Aiko dabba yasan mai kyautata mashi dole suyi kuka don basu samun irin kulawan da kake basu idan suna Dijece mai kula dasu kuma ba kafa ke garetaba sosai.
Kingani ko wallahi ina can ina tunanen su nima don nasan ba zasu samu kulawan daya dace ba dama har mafalki dasu nakeyi wani lokacin idan na kwanta.
Jin hakan yasa na dan kalleshi kafin ya fadi wani abinda zai daga min hankali ya hanani barci da dare nace dashi.
Dare yayi kan nima kwantawa zanyi kada in Makara don gobe muna dashiga school affa nafa shafa zaki fita goben ai ya fada sai kuma naga ya dukar da kanshi kamar mai tunane a hakan na sulale na shige dakin.
Bandaki na shiga na kara gyara kaina kodana fito na
sameshi ya shigo yana cire rigan dake jikinsa yana fadin zafi yakeji duk da sanyin da yai yawa a lokacin.
Azoto na yadda ya gaji din nan ba zai nemeni ba a ranan son gajiyan dake tare dashi tunda yace min a ranan suka sauka Nigeria ya shigo jirgi karfe hudu zuwa sokoto a nan kuma ya dauko mota haya ya karaso dashi gusau.
Don haka na dauka gajiya bai bari mu kasance tare a ranan sai gashi ina kwanciya naji muryanshi a bayana yana fadin Zahra kinsan fa nayi missing dinki sosai duk da banga hakan a gareki ba.
Master agajiye kakefa kaima ka sani yanzu me zaka iyayi bayan wanan gajiyan dake tare dakai oho haka kikace yarinya aini ba raggo bane irin ki bari ki gani yanzun nan in nuna maki hakan.
Koda gari ya waye na tashi duk jikina yayi tsami kuma ga shiga school ga hada
breakfast da zanyi muna dolene tunda master yana garin duk da rashin kuzarina haka na daure nayi aikin dake gabana a lokacin yana kwance yana barcin gajiya kilama baisan na tashi bani .
Abinda bai taba yi min ba kenan don tare mukan tashi idan ina aikin safen ya taimaka min dasu shara da wanke wake da gyaran daki amma a ranan ban samu hakan ba duk ni nayi aikin da kaina ni kadai.
A gurguje nayi wanka nakai masa nasa ruwan dumin don huturun da akeyi sosai a wurin mu din wanka saida ruwan zafi ga mutum.
Ina dauko kayan da zan saka ya falka a gajiye ya bude idanunshi yana fadin har kin tashine ashe na dan juyo nace eh .
Yanzuma school zan wuce saboda na dan makara nasan yau yana da wuya na samu shiga darasin safe yadda na makara din nan ya akayi kika makara naji ya fada abinda yasa na juyo ke nan ina masa kallon mamaki don duk lokacin nan da muke magana fuskana yana kallon cikin wardrobe dinane.
Kwane yake ya dunkule saman gado ya dora kanshi a filo ya lefe yana kallona murmushin danagani a fuskanshi yasa na gane zolayata yakeyi da hakan .
A dan marairaice nace haba master kaifa ka hanani barci daren jiya kuma yanzu na tashi nayi aiyukan safe ace tsakani da Allah amma baka tausaya min ba ?
Yana fadin ayya sorry yarinya shine baki tasheni in tayaki ba, dan zo nan na dan karasa don ban kwankwasa kofan da mukajine da karfi daga wajen part din mu ya hanashi karasa maganan da zai fada din naji yaja tsuki da karfi yana kokarin saukowa daga kan gadon .
Sai kuma ya koma ya zauna ya kalleni yace yanzun haka innace fita kice mata ban tashi ba daga barci ba har yanzu.
Kalloshi nayi ya kafin nayi magana muka kara jin dukan kofan da karfi wanan karon hakan yasa ya dago a hasale ya nufi kofan da kanshi yana fadin wai waye don Allah zai balla min kofa hakane.
Mune yaya Inna ce tace mu dibo ko kun tashi taga baku fito ba wai muryan Asmau ke fadin hakan yace shine tace kizo ki dinga dukan kofa haka cikin daga hankali kice in mun tashi ai zamu shigo ciki mu gaidasu da kwana kada ki kara gigin zuwa nan kice kinzo tayar damu don ranki zai baci.
Ya mayar da kofan falon daya bude da karfi ya buga din bai bude na shigowa part din ba a lokacin ranan ne karo mm a farko da hakan yai min zafi har nake tambayan kaina wai me inna take nufi da hakan da takanyi munane.
Inma har tana tunanen wani abune ai mun riga mun more junan mu da dareko don ba zata hanamu kwana tare ba na fada a kasan zuciyana duk dana makara ban fita ba don yunwan da nakeji don haka na zauna na karya ni kadai a falo shi yana cikjn dakin ashe wanka ya shiga
Ina gamawa ya fito yana fadin wani mashi din dai zanyi kokarin saye kafin in koma zaria in aje don zuwan ki school bakiga yadda bin achaban nan yake ci min raiba wallahi.
Kawai dai banda yadda zanyine a yanzun din yasa na kyale hakan amma wanan abin yana damuna a rayuwa na dauki ruwan tean dake gabana ina kurbawa nace don kawai wasu mazan na daukana ko ?
Haba dai ni bama wanan ba duk wanan fa zahra ta dalilina kika shiga wanan halin a yanzun don kawai kin aureni yasa aka kwace maki motanki a hannunki akabawa wani yana hawa ina gani.
Shi kuma Abba