Showing 264001 words to 267000 words out of 304363 words
house irin wanan ai sai su mama da aka saba da hakan.
Ke ni ku rabani da zancen Alh yanzu ba shine a gabana ba zancen wanan yar iskan sarkin naci shi yake damuna don inba nayi da gaske ba sai salma ta zamo min kaya a gidan nan nan gaba don alama ya nuna hakan.
Ta yaya haka zai faru mama Aisha ta tambaya yaya ba zai faru ba ga zahiri kin gani kuwa ita da yarta duk abinda zanyi a kansu sai sun tsallakeshi shegiyar yarinya shiyasa take kama da uwarta kamar an tsaga kara.
Mama yaya ko zakiyi nifa naga kuna son dorawa kan ku wahala a barsu mana tunda haka Allah ya nufa don zahra taje kasan waje da mijinta shine me mama zata hanamu numfashine ko me ?
Shine kuwa komai ke rukky bansan irin zuciyar ki ba keda yannen ki ana fahintar daku abu baku fahinta bari kawai mama lokaci zai fahintar da ita hakan ai Aisha ta fada a hasale.
Barta barta kawai yanzu ke kina son ace wanan abin ba a dakin nan yafito ba ace a cikinkune wata tafi koda muncewa mutane aikin gawa yakeyi a can ai idan wasu sun yarda ai wasu kallon mu zasuyi a yan hassada.
Ga wa yan nan yannen naku narasa gane kansu kullun cikin yi min karya suke na yau daban na gobe daban dole kuga na damu haka da wanan zancen.
Kowansu shiru yayi suna nazarin maganan mahaifiyar tasu saidai ita rukky da bataga wani abin damuwa ba a nan tasan dai tafi zahra gata da uwa to me zai dameta yanzu da zancen zahra can.
Matsalanta daya shine mijinta da yanzu baida abinyi tunda yayyenshi suka kwace kudin da yake juyawa don sunga kudin zai salwanta shine kawai damuwanta a yanzu ita.
Daga cikin dabarun master tare da tunanen shi ya samu na farko don yanzu ya dasawa mahaifinshi kaunarshi tare da shakkarsa a zuciyarsa daman haka yake son abin ya kasance kamar yadda suka shirya da malam musa.
Don idan ya shiga cikinsu haka zikau daga sama ba zaiyi wani tasiri mai ma,ana ba ko agun mahaifin nasa yasa sukai ta ja masa aji tun farko yanzu ko dabaransu yayi don ya dasawa nahaifin nasa kaunarsa tare da dan shamaki a kansa don gudun kada yaki zuwa gareshi.
Yasan duk abinda za ayi a yanzu mahaifin nasa ba zai shagala a kansa ba dole yana da muhinmanci a zuciyar mahaifin nasa gashi a yanzu suna waya sau uku ko biyu suna fadawa juna matsalan su.
Sannu a hankali gaya yanzun wata irin shakuwa mai karfi ta shiga jikin junan su baya shaka ko nauyin kiran dan nasa a gaban kowa yauma a irin hakan yana zaune a falo da dukkan iyalansa.
Wanan wata sabuwar dokace a gidan nasa nayin hakan a ranan jumma,a duk wani wanda ke rayuwa a cikin gidan dole zai fito falo ya zauna kowa na fadin bukatunsa.
Dama suna hakan a baya saidai a lokacin dagasu sai diyansune a wanan irin zaman sabanin yanzu da suke da bakin fuskan da suke gani a cikinsu.
Wanda ba kowa bane sai hjy murja da yaranta biyu da take riko a yanzu a hannunta wanda hjy yabi take gani da sun mata kutse a rayuwanta dana diyanta don ganin hjy murja din takeyi a matsayin yar ci rani a cikinsu tazo zata koma.
Daddy dinne ya fito daga part dinshi dama kusan ko yaushe shike karshen fitowa gashi anyi sa,a kowa na gidan yana nan don har kananin sun samu hutu sunzo a lokacin.
Yar computer yake kokarin dannawa har ya kai zaune suke gaidashi yake amsawa kafin ya dago yana fadin mustapha bari na faral gaisawa da babban yayan ku ko ?
Muji lafiyan su nasa dana iyalansa a cikin mamaki yaron daya kira da musty din ya dago yace wa,wooo daddy big brother kuma bayan ya Yasir akwai wanine ?
Kwarai kuwa first son dina Ahmed mai sunan dad dina yanzu yana aiki a America shine zan kira ku gaisa dashi a karo na farko ya kamata ku sanshi ko ya kalli yaron sai yaron ya dan daga kai yana mamaki.
Hello Abba an wuni lafiya yaya aiki ya iyali lafiya kalau muke baba karami ya can ya naka iyalin kuma ya dan sosa kai yace suna lafiya Abba.
Ga brothers dinka zaku gaisa dasu yau don kowa na gida a yau mun hadu wani iri kowansu yaji a lokacin cikin ransa Ahmed din ya gyara yace OK cikin nuna rashin damuwa.
Yasir kazo kusa ku gaisa dashi Abban ya fada kamar ba zai taso ba sai shi karamin yace bani mu gaisa daddy ya leko kai don ganin fuskan sabon yayan nasu da mahaifin nasu ya fada.
Yace wonderful wanan ai kamar kai daddy hakan ya kara tarwatsa zuciyan hjy yabi dake zaune a gefe takai iyakan kuluwa da zancen mahaifin nasu wai yau ita ake fadawa wani zancen dan uban diyanta a gabanta.
Dan uban kuma har yakai matakin da taron gabansa a yanzu sai tayi aiki sosai kafin ta shawo hakan don ya riga har ya taka kasa ya wuce tata a wurin ta a yanzu.
Look alike wanan ai photo start din daddy ne aje yasir da bata san yakai wurin ba ya fadi hakan tare da dagawa dan uwan nasa hannu yace hey shima ya dago yana fadin sallamu alaikum.
Saman karamin table din gaban shi ya aje na,uran suna zuwa daya bayan daya suna gaisawa dashi tare da fada mashi sunan su yana furta masha Allah shukuran.
Har yakai hjy murja da kowa na falon in ka debe hjy yabi dako motsawa batayi ba a inda take din zaune don firgita saboda bata taba sawa a zuciyanta akwai irin wanan ranan tafe mata ba.
Muryan shi radau a cikin nauran yake fadin ina mama firgigit ta dawo da hankalinta tana kallon na,uran yaji sunce gata zaune aka juya fuskan computer a wajenta .
Hannayenta ta matse lokaci daya a jikin kujera don firgita da irin kaman data gani yaran na fadi ta dauka kamar wasace sai ga idonta ya gano mata zahiri ta gani itama.
Lalai kan idan rana ya fito tafin hannu baya rufeshi don tayi sake dan zaki ya girma bata iya taronshi a yanzu don wanan matashin akwai baiwa a tare dashi wanda ya hasaka kuma taga hakan a fuskansa yanzun din da suke waya.
Mama kuna lafiya ya family sannu da kokari ya fada a cikin waye kuma kai tsaye yana sake murmushin da take ganin barazane yanzun a gareta kai tsaye.
Suna gama gaisawa shi da kansa yace bye Abba i will call you letter in the night see you guys ya kashe na,uran wayan dip lokaci guda.
Falon yayi tsit kamar ba mahakuki a cikinsa sai zuwa can hjy murja tayi karfin halim fadin kai amma gaskiya Alh kamar ku dashi har ya baci da ganinsa ba sai an tambaya ba don ba inda ya rageka haskene kawai ya dan daraka dashi yanzu.
Sai ko yawan fara,a don yafika sakin fuska da alama shima yana da saukin kai sosai Dad amma baka taba fada muna zancen shi ba ki sau daya.
Ko yanzun ne din ya zama danka kaima kasan dashi Salima ce me wanan tambayan daga inda hjy yabi take zuciya yana cinta tace kuma dai kwa tambayeshi hakan don da dan halak ne da kowa yasan shi tun farko ai.
Keee ya fada a cikin wani irin tsawan da duk basu san yana da murya haka ba ga dan yatsan shi daya daga ya nuna mata a makale ya kasa saukewa haka kuma banda kalman ta ke ba abinda ya iya yi a lokacin sai hannun dayake nunawa matar tashi.
Kada yatsan ya farayi yana carstinel da ita tana bada sauti kas kas kafin ya tsayar ya kara nunata ya juyo da yatsan yana nuna yayanshi kana ya dawo da hannunsa kan hjy yabi din yace duk daya suke da wayan nan.
Na fada maki duk daya yake da wa yan nan yadda aka taru aka daura auren ki har kika haifa min yara gasu haka aka taru aka daura aurena da uwarshi har muka sameshi .
But daddy as how ita mum din nasa bamu santa ba kuma bamu taba jin labarin hakan ba don ace muna mun ce first wife dinka ai ga wanan kace ya girmeni kuma.
Good question zan dan fadama yanzu abinda nake son ku tambayeni ke nan tun farko zan fadama in brief saura kuje gun uwarku ku tambayeta dalili itake da amsan hakan.
Falon yayi tsit yace anyi wani lokaci da wasu azzalumai sukai min asiri na bar gida na bar iyayyena da dukiya don kawai suna son su mallaki dukiyan nawa da Allah ya ban ta hanyat gada a wurin mahaifiyata da itama kamar nine gada tayi gun nata mahaifan da tazamo ita kadai a wurinsu.
A wanan lokacin na shiga duniya na nufi garin illorin nabi motan masu kai shanu a can a illorin din na danyi shekaru biyu a can ina aikin shanu nasha bakar wahala gani da kwazo da iyayyena suka samu labarin inda nake suka biyoni na samu kabarin zuwan su .
Shine a ranan nagudu nabi wani Alh dan Zamfara da mukai sabo dashi idan sun kawo kaya shi nabi zuwa garinsu a cikin babban motarsu na katako da ake kwasan kaya dashi har zuwa gusau da yanzu ake kira da zamfara.
Shiya zama uban gidana a can har ya tsaya min akai aurena da wata yarinya mai tallan kunu a wurin mu itace mahaifiyar Ahmed shekaran mu biyu da rabi da aure Allah ya bata cikin Ahmed.
Mahaifina kuma bai zauna ba suna magani sosai kuma sun rike min amanan dukiyana sun hana wa yan nan azzaluman tabawa da sukaga haka shine suka kara yin asirin da zan dawo gida.
A daidai lokacin haihuwan Ahmed lokacin asirin ya kare a kaina naji gida kawai nake son zuwa a lokacin ji nake kamar wuta ake saka min a zamfara din.
Naso nazo da matata nan mambila ita kuma sai iyayyenta suka kafe bazasu bani itaba zuwa wuri mai nisa a lokacin shine suka sa na saketa duk muna son juna a lokacin tun wanan tafiyan ban sake ganin shi ba ko tunawa dashi .
Saboda wa yan nan azzaluman da suka sake plan a kaina suka mantar dani wanan yaron suka makala min son su suna juyani yadda suke so akan abin duniya.
Sai gashi Allah da ikonsa a yanzu Allah yayi shidin rayeyene ya girma ya nemoni lokacin har yayi aure yana aiki yanzu a America ne acan kuma yake zaune tare da iyalanshi.
Kai kai kai Dad su waye wa yan nan azzaluma gaskiya sunci akai gaban alkali ayi karansu wanan zalunci yayi yawa dad da zan gansu dani zan hukuntasu da kaina don suncuce ka dayawa.
Kallon hjy yabi yayi tare da alama da hannu kinji ko daga bakin diyan cikinki caraf a idon hjy murja ya dan share hawayen daya gangaro mai a fuskanshi ya mike tare da fadin zan shiga inyi alwala sauran bayani anjima mu hadu.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
[7/3, 6:42 PM] Zainab Idris Makawa Writer: 🌱TUMFAFIYA UWAR KWANKWANMAI ,,,,,,,,,,
🌱TUMFAFIYA BAKI FITA A WURIN BANZA ,,,,,,,
🌱TUMFAFIYA SIRIN KI SAI ALLAH ,,,,,,,,,,
ZAINAB IDRIS MAKAWA
9️⃣0️⃣
ONLINE PAID NOVEL YARUWA KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMA DARI BIYAR NE DON KIRA 08036959257 KO BIYA KI AIKA 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KATIN WAYA MUN GODE UBANGIJI YA BAKI IKON BIYA AMIN,,,,,,,
Tabbas Aljanni na tsoron hatsabibin dan adam hakama maye yana tsoron cin mai baki hakika haka zancen yake kuwa don ni na sheda hakan .
Tabbas Ahmed yasan meya taka ya kuma san ko meye yake bibiyan mu fadi daine kawai baiyi don haka maza suke koda sun san abu haka zasu danne a zuciyarsu.
Su nuna basu san komai ba hakan kuma ke faru damu din saidai koda wasa bai nuna hakan gareni ba ko a wani nawa.
Sannu a hankali cikin jikina yake girma amma saboda lafafen cikina ba zaka dauka cikin ya girma sosai ba a lokacin don bai wani taso ba da za a gani sosai ba.
Zuwa da dije ya taimaka min matuka don da ita nake zama inyi hira sai yamma idan ya dawo yake dan zama damu ayi hira a irin hakane muna zaune ranan wayanshi yayi kara ya dauka yake fadin innace fa.
Amma ai yanzu dare yayi sosai a can mana yake fada lokacin da yake daukan wayan yayi sallama ta amsa mai gaisuwa ya fara mata bata amsa ba sai cewa da tayi dashi.
Duk yadda ka daukeni dai uwarkace ni kuma nina kawo ka duniyan nan da har wasu suke kallon ka a mutum yanzu har suke ganin sunfini iko ko wani abu dakai.
Kai ya dago ya kalli Dije ya kara sautin wayan yana fadin meya kawo zancen nan kuma inna na taba fadin bake kika haifeni ba ki na taba wani magana da bai dace ba a kankine ?
Aiko bakayi ba ka nuna hakan tunda ga zahiri mun gani ni kuke dauka manya ko wata muguwa da har zaka hada kai da mahaifinka da iyayyen matar ka ka dauke matarka a gabana zuwa wata kasa don kar na cinyeta ko me ?.
Innalillahi ni akace na fadi hakan akanki ko wa don ni bansan da wanan zancen ba sai yanzun da kikeyinsa eh ba zaka sani ba amma gari yanzu kallon da ake min ke nan ai.
Ko ita umman mu din da aka hada baki da ita ana min kallon zargi yanzu ba zance komai ba amma kuje can din inda bani ku haihu din wai ashe matarka cikine da ita don kada in sani har ake min boye boyen hakan.
Kuka hada baki da mahaifinka ya kirani yana kokarin fada min maganan banza ban san hakan ba a lokacin dana fada mai yana sonkane balle abinda matarka zata haifa ?
Ko yanzune har yasan zafika su kuma gidan matar naka dana fada masu cewa ai sunsan nice uwarka suka baka diyarsu inma ruwan kasari mukesha musha tare da yarsu a nan.
Yanzu inna duk meya kawo wanan magana me zafi haka akan son Dije da zahra sunzo nan don jikinta kike wanan zance haka a cikin bacin rai ?
Har kina kokarin ki batawa kanki suna ki kira kanki da manya to nidai ko wani na kusa dani Allah ya sheda bamu taba fadin haka ba kuma ba wanan zancen a zuciyar mu.
Zakace haka yanzu ai tunda kagama bata min suna a gari ana fadin don ni aka dauke ta akabar kasan nan da ita saboda halina.
Allah ya baki hakkuri inna ya fada ya kashe wayan koda ya dago kai ya dubo inda muke ban wurin na shiga daki sai dije da tayi shiru tana saurarensu tace.
Halin Rashida sai ita wallahi wanga magana haka ina ya fito zancen bata san matarka nada ciki ba idan ita a matsayinta na tsohuwar mace a yanzu bata gane haka ba har sai an fada mata .
Wa take son ya tareta ya fada mata zancen cikin matarka ko kai take son saika kirata ka fada mata don ta samu wurin yi maka iya shige.
Dama abin Allah haka yake da zaran anyi mace gorin haihuwa a cikin kwanakin Allah sai yaji tsusayinta wani lokacin ya bata ciki da wuri ta haihu.
Don nan da kace zaka zo nan take fadin zaka tafi ko kwai matarka ta kasa nasawa a gani inka dawo dolene tayiwa danta aure ka auri mai haihu ba wace keci kullun tana kaiwa masai ba.
Na san kuma da matarka take wanan zancen a fakaice bandaiyi mata magana bane lokocin don akwai mutane a wurin sosai yasa na kyaleta ban tankata ba.
Amma na rasa gane dalilin dayasa Rashida ta tsani yarinyar nan duk da hakkuri irin na matarka wani lokacin sai Rashida ta kaita iyaka wanan halin dame yai kama haka don Allah ?
Alkawari na daukarwa kaina Dije akan zahra don nasam me inna take nufi sarai akanta don haka nima nayi alkawari a raina kuma ina rokon Allah ya cika min burina a kanta din insha Allahu zan gwadawa duniya niba butulu bane.
Mum suwaye daddy ke magana a kansune haka don ni har yanzun na kasa fahintar ko suwaye sukai masa hakan a cikin labarin daya bamu din.
Tunda bai fada ba ai shike nan ko meye na tambayana abinda ban sani ba yanzu saidai zancen wanan yaron dayake ikirarin cewa dansa ne shine ban yarda dashi ba har sai gwaji ya tabbatar da hakan.
No no no mum kada kice zaki hakan don kema kinsan daddy ba dan iska bane don sanin halinsa nema har watarana nakan yi tunanen ina muka kwaso namu halin ne wai ?
Don haka ki barshi da dansa mutumin daba zama zaiyi a nan tare damu ba shimafa yana