Showing 195001 words to 198000 words out of 304363 words
min.
Kinyi kokari zahra dadin hakkurin ki yana tafe insha Allahu a sanadin ki yau Allah zai cika muna burinmu mu bar bawan Allah yayi rayuwan sallama.
Zakice mutumce yar uwana muke hira a lokacin da ita sai har nake ce mata kuda suwaye tace nida na tare damu ai tun yana goye muke bibiyan lamarinsa.
Tun ranan da uwarsa tayi fushin zuciya ta barshi waje a tsakar gida shi kadai ya kwana don mahaifinsa zai wuce ya barta tun wanan ranan muke bin duk wani al,amarinshi.
Wanan mahaifiyar nasa tayi watau da yawa akan zafin kinshin barin mijinta har ta dorawa dan yaro laifin dabashi bane yayi shima mahaifin nasa ai kiran gagawane ya samu bai isa ya kara kwana uku a wanan garin ba lokacin.
Amma duk basu gano hakan ba a lokacin saboda idanunsu ya rufe sun kasa fahintar ba tafiyan lafiya zaiyi a wanan lokacin ba.
Ki tambayeta kiji a cikin darene suna kwance ya zabura yake fada mata inane nan meya kawoshi nan ita din waye har taso dora mai rashin hankali a lokacin.
Amma da akai mai bayani ya gamsu bai kisu ba ya kuma karbesu hannu bibiya har ya bukaci a barshi yaje dasu garinsu amma iyayyenta sukai tsaye ba zasu yarda da hakan ba.
Munturashi garin baban shi mun hadashi dashi ya ganshi duk ta hanyar hikima irin namu mune kuma mukasa a karya asirin a yanzu haka yana gab da haduwa da mahaifinshi insha Allahu.
Munyi maganganu da dama da ita har da wanda ya shafi rayuwata dana gidan mu wanda hakan ya bani mamaki sosai a lokacin.
In kina son ki gaskanta hakan ki tambayi tsohuwa yadda akayi rikon mijinki ya dawo gareta don sunso ya mutu a lokacin daga mahaifiyarshi har yan uwanta sai tsohuwar nan da mijintane basu yarda da hakan ba.
Ki fadawa mijin ki in mahaifinshi ya zo gareshi kada ya nuna masa bacin ransa don shima ba yin kansa bane hakan duk da an fadamai a baya.
Ni zan koma gida dama nazo mu gaisane kuma in isar maki da sako gareku daku kara hakkuri farin cikin ku yana tafe bada dadewa ba amma sai kin hada da hakkuri ga abinda zai biyo baya.
Ina kallonta sai naga ta shige cikin icen tumfafiyan dake daga can gefen rumfarsu sai wani haske ya baiyana kamar walkiya a lolacin ta bace.
Sai lokacin wai naji tsoro na yanka wani irin ihu ina salati hakanne ya farkar dani daga barcin kuma ina ihu ni kadai a cikin daki ga wani irin duhu daya mamaye dakin bako dan haske sai hakan ya kara ban tsoro a lokacin.
Can naji kamar abu yana bin wuyana da sauri na shafa saidai bani ganin komai a lokacin amma ina tamtaman zufa don yadda naji goshina ya jike a lokacin.
Amarya lafiya kike kuwa ta dai bude kofan mu shiga naji muryan Inna bayan na Dije dake tambayana a lokacin hakan ya sanar dani cewa ihuna yakai ko ina a gidan ba iya cikin mafalki nayi wanan ihun ba ashe ?
Wayata na laluba inda na ajeta saidai ban jitaba a inda na aje din haka yasa na fara lalubenta da sauri kafin naji wani motsi a dagan dakin kamar wani abu ya fita dakin da sauri lokacin.
Jin hakan ya kara min kaimi wurin lalubo wayan najita can karshen gado na dauko na haska ina amsa kiran da Dije din ke min a lokacin a gagauce hankali tashe.
Na samu na amsa ina kokarin bude kofan dan falona jin ina budewa inna ke fadin ko lafiya dai kike wanan ihun haka da tsakar daren nan na bude ina fadin lafiya inna kila mafalki nakeyi.
Wanan mafalkin ko ba maikyau bane da jinsa tunda baki taba irin sa ba a gidan nan kai wallahi duk munji tsoro mun daukama wani katone ya shigo maki ai kike wannan ihun hakan.
Kaiya ina wanan zancen ya fito maki kuma haka babu dadin ji a bakinki wanga wani irin fatan banzane kuma ga sarakuwan ki da zaki mata zaton kwarto a dakinta ?
To umma nidai ban iyawa a cikin daren nan yadda tayi ihun ne yasa na fadi hakan ke wuce muje mu karasa daren tare a nan Dije din ta fada yaran nan na tayaki kwana amma saida aka san yadda akayi aka hanasu kwana tare dake dakin nan.
Ni ban hanasu ba itace dai take nuna bata so don kafin suzo ta rufe kofanta ta juya ta tafi tana fadi adan hasale tabarmu da Dijen nan muka kwana tare da ita a part dina.
Washegari sai bayan mun idar da sallah wuri yayi haske ta fita zuwa dakin ta tana min adduan tsari daga duk wani shedani dake bin bayana a rayuwana na amsa da Amin.
Har nagama shiri na tafi makaranta duk da akwai barci a idona sosai don rashin samun safiya da banyi ba na karfe hudu zuwa biyar da bawa kanji dadinshi a lokacin fiye dana tsakiyan dare.
Sai wajajen karfe ukune wani irin zazzabi ya fara ziyartana a lokacin sai gashi duk dauriyan da nakeyi na kasa hakan don jiki har yana kaduwa hakorana suna hadewa wuri daya a lokacin don zafin zazzabin daya sauka min lokacin.
Da taimakon su hannatu na samu na dawo gida tare da ita a ranan haka muka shigo gidan ina gigice cikin wani yanayi.
Hankalinsu Dije ya tashi ainun don inna batama gidan a lokacin ganin haka yasa Dije fadin Aisha maza karbi canjin nan kije wurin mai kemis ku sayo mata paracetamol ta hade.
Ta karbi kudin da sauri zuwa wurin mai shago din tasayo maganin aka kawo min ko kallonshi banyi ba don ban masan inda nake ba lokacin.
Ganin yadda nake hakan ya tayarwa hannatu da hankali tashige daga kuryan dakin ta kira ummah tana fada mata abindake bata wani daga hankali ba sai cewa datayi da hannatun ga Tani nan zuwa ta gani.
Zuwan tani tazo min da magani daga wurin ummah na tasa akai min hayaki a dakin takumayi dabaran shaka min a hancina lokacin sai da aka dauki lokaci na dan samu nayi attishawa maidan karfi Allah dai ya taimaka iya mune a dakin lokacin daga haka kuma barci ya daukeni lokacin.
Wayana ke ringing ta dauka master ne jin an daga wayan yake fadin haba dai my princess kinsan ina exam shine koki kirani kiji ya pepper ?
Hannatu ce master muna gida zahra ce ba lafiya wallahi sai yanzu ta dan samu barci tayi yanzun hakama tana barcine.
Subbahanallahi bata da lafiya meya sameta ya tambaya cikin damuwa take fada mai dai dukkan abinda ta gani tace kuma a karshe zazzabine dai mai karfi ya rufeta.
Bakuje asibiti bane da ita hannatu ya tambaya cikin damuwa a muryanshi sai tace munje asibiti sun bata magani nan school cleanic .
Daga school din muka dawo gida da ita ina gudun mu tafi FMC daga can ya zama magana kuma amma yanzu ummah ta aiko da magani tasha shine harta samu barcin.
Ok kun sanar mata ke nan to yaya jikin da sauki yanzu ko ya kara tambaya tace da sauki gaskiya bisa ga dazun din don yanzu har gata tana barci Dije ma tabada kudi kuma an sayo wani maganin chemist dazun da muka dawo saidai bata samu sha ba.
Don Allah hannatu idan ta falka kikaga tana jin jikin ki taimaka min ku tafi asibitin zaifi tace insha Allahu, master and please call me indan ta falka tace mai tau.
Gida kan yanzu ya canza don da can gidan shirune don sauran yaran gidan dake makaranta a lokaci amma zuwan su hjy murja yasa gidan ya rayu tsakanin jiya dayau din nan .
Har zaka danji hayaniyan mutane jefi jefi babu komai a ran hjy murja din a lokacin sai fargaba da tsoron hjy yabi don sanin halinta da tayi na rashin barwa Allah zance.
Gashi tun zuwan su garin ba wanda ya lekosu daga bangareta son ko yarta murja bata kara bi ta kansu ba lokacin asalima ta manta da zancen wasu baki a gidan lokacin.
Andai kawo masu abinci da suka iso haka an kawo masu na dare sunci tun lokacin ba wanda ya kara leko part din nasu sai su kadai ke sha,aninsu suma di cikin sakin jikinsu suke komai.
Washegari misalin karfe bakwai da rabi na safe wanan mai aikince tayi sallama ta sake shigo masu dauke da manyan kuloli ta aje masu kana ta gayar dasu da kwana.
Suna gaisawa ta daga zata wuce taji dayan na fadin mama kece mai aikin gidan nan ko ta juyo tana dan murmushi tace nice dai daga haka tayi sauri ta fice part din.
Tana fita dayan ta bude dayan kulan taga soyayyen kwaine da irish acikinsa saida aka cika har baki dayan kuma ferfesun kayan cikine a cikinsa mai yawa wanda zai ishesu sai dayan cuscusne yaji hadin kayan labu an zuba mai kamshi da kalan abinci ya canza kala.
Itace ta dawo dauke da kofuna da bread manya guda uku sai kayan shayi ta aje masu a inda ta aje na farkon suna mata sannu ta dawo da flask din ruwan zafi ta aje ta fita suna mata godiya.
Wanka suka fara shiga sunayi kafin su zauna gaba dayansu suna karyawa a lokacin nan dayan kewa yan matan fada cewa su dai iya kansu a gidan yadda sukaga yar uwansu tanayi banda rawan kai da saka ido ga komai.
Sai bayan sun gamane an dan jima Alh ya shigo suka gaisa yake kara masu bangajiya kafin ya dago yacewa matar nasa murja.
ZAINAB IDRIS MAKAWA🌱TUMFAFIYA UWAR KWANKWANMAI ,,,,,,,,,,
🌱TUMFAFIYA BAKI FITA A WURIN BANZA ,,,,,,,
🌱TUMFAFIYA SIRIN KI SAI ALLAH ,,,,,,,,,,
ZAINAB IDRIS MAKAWA
6️⃣8️⃣
ONLINE PAID NOVEL YARUWA KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMA DARI BIYAR NE DON KIRA 08036959257 KO BIYA KI AIKA 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KATIN WAYA MUN GODE UBANGIJI YA BAKI IKON BIYA AMIN,,,,,,,
Jiki wasa wasa yaki dadi gareni a kullun sai kara gaba gaba yake min hakan yasa har na dauke kafa ga zuwa makaranta a lokacin.
Tun hankalin inna bai dagaba har wani dare dole ta fito da damuwanta fili ta nuna tausayawanta gareni tana fadin kalamai a tausashe saboda ta tsorace da yadda tagani kwance.
Ganin zan mutu a gida sai magani nake sha ba a san makarin ciwo ba yasa nasa hannatu kiran ummah ta fada mata halinda nake ciki din.
Sai cewa ummah tayi yanzu hannatu ya kuke son nayi tunda nauyin ta ba a hannun mu yake ba yanzu kawai dai ku kira mijinta ku fada mai abinda yace sai ai hakana.
Ga hankalin hannatu duk a tashe yake shi kuma macan hakane gashi suna test a lokacin suna gab da zana jerabawan fitane a lokacin.
Data kirashi cikin daren tana mashi bayani hankali tashe murya kamar mai kuka yake fadin don Allah ummah tayi hakkuri a taimaka mashi ga halinda yake ciki.
Amma sai hannatun ta kasa kiran ummah din don yadda sukayi da ita da farko dole dai shi din da kansa cikin dare da inna taga zan mutu ta kira shikuma ya kira sai hankalinta ya daga sosai ta kira shehu da daren nan yanzo suka kamo hanyar gidan mu din.
Da karfe Biyar da rabi na asuba ummah sukazo da shehu aka daukeni zuwa asibiti muna zuwa fada suka fara cewa yaya akayi har na gala baita haka ba a shigo dani asibiti ba.
Nan dai suka karbeni baya korafi da sukasha wurun nurse din tayi muna hanyan ganin likita ya auna yasa a sayo ruwa da magani aka dora min sai lokacin na samu barci mai nauyi ya daukeni sosai.
Ana idar da sallah asuba yana kiran layin wayana yajishi kashe sai na ummah din ya samu tana kuma azzakar bata magana a lokacin sai ta idar.
Hakan ya daga mai hankali ganin ya kira har sau uku karshe ma ta kashe wayan gashi duk sauran wayoyin nasu basa shiga a lokacin nan ya soma shirin baro zaria duk da yasan test din dake gareshi yana da muhinmanci sosai a lokacin.
Ya gama shiri zai fito wayanshi ya dauki kara ummah ce mai kira a lokacin gabanshi na faduwa take fadin tana sallah a lokacin yasa bata daga waya ba.
Bai tsaya gaida itaba yace ummah ya mai jikin kuma tace da sauki sosai ta samu barci gata nan kwance tana barcin tunda aka fara karin ruwa.
Sauran gwaje gwaje sunce sai gari yawaye za ayi ka kwantar da hankalinka don da sauki sosai insha Allahu zata samu lafiya yace to ummah da yanzu zan biyo hanya inzo.
Tace a,a ba ance kuna test bane kokazo me zaka iya mata kadai mata addua shine take bukata ta samu lafiya sosai fa yanzu don numfashin nata ya koma daidaima a yanzu.
Jin hakan yasa shi ya tsaya ba don yaso hakan ba a lokacin anyi duk wani abinda yadace ayi amma sai cewa sukayi maleria da thaphod ne ke damuna a lokacin.
Karfe takwas ummah ta kira gida take shedawa mama suna asibiti dani tunda safe mama din ke fadin me kuma ya sameni tace zazzabine dai tayi Allah ya sauwaka ta kashe wayan a gundure.
Bayan ta kashe take jan tsoki tana fada su gwaggo shafa ne dai sukai tawaga sukazo dubana anyi sa,a lokacin Tani ta kawo kayan da ummah ta umurceta da takawo muna asibitin.
Da badon hakan ba babu komai da inna tayi yunkurin biyomu dashi asibitin saidai sunzo dubana ita da yaranta tunda farar safiya shine kawai gaskiya kokarinta a lokacin.
Karfe daya saura yana cikin gusau asibitin ya nufo daga nan ko gida bai isa ya aje kayanshi ba yazo har dakin da nake kwance har lokacin barci nakeyi sosai don gaskiya na wahala.
Kwana biyu bama barci da hannatu data zauna a wurina a karshema har makarantan itama ta daina zuwa tana zaune tare dani a gida tana kula dani don har mutanen gidansu saida sukazo gaidani.
Mamako Abba ta kira tana fada wai ummah tana kokarin raba daya biyu duk hakkurin da takeyi da halin ummah zata kaita makura wai suna asibiti dani amma ummah bata fada mata ba sai da ranan nan donta dauketa muguwa kome ?
Amma ta fada min ta kiraki tun takwas na safe ma don na tambayeta ta kira ta fada maku tace eh yanzun ta gama waya dake ta sanar maku.
Wai halin hjy salmane kuma baka sani ba ni dai na fada bana son hakan da take min gaskiya da wani abune da yanzu ta kira tana fadama sai kawai ta kashe wayanta lokack guda a hasale.
Duk da yaji mamakin hakan data fada amma kuma ba zai iya cewa komai ba a lokacin karshema kiran ummah yayi yana fada don me bata fadawa mutanen gida zancen ciwona ba.
Ina wani abune aiduk ita tajawa kanta wanan wullakancin tunda ita tanacewa wanan fakirin yaron tace shi zata aura yanzu duk wullakancin daya biyo baya ai ita tajawa kanta kuma ?
Ummh,humm ka gama kada ka mace da duk mai rai baya wuce kaddaransa a rayuwa ni ban raina da auren zahra da yaron nan ba don bansan dalilin da Allah ya hadasu tare ba.
Kuma ai naga banina aurawa yarka shiba kai kaga dama ka aura mata shi a matsayinka na ubanta koka taba jin inda mace ta aurawa yarta aure koda kuwa shegiyace ita ?
Sannan ita hajiyan datace ban fada mata ba Allah ya sheda karfe takwas na kirata na fada mata itace mutum na farko dana fadawa kuma har kusan duk yan uwa sunzo asibitin nan duban mu.
Kawai idan wani tsegumi takeji dashi ta fada zaifi amma ba wanan ba taje tayishi a wurin ka kaida kake daukan tseguminta ba bincike ko yaushe ni ba wanan bane a gabana yanzu ba.
Tana fadin hakan ranta ya gama baci sosai a lokacin don haka ta kashe wayan a hasale Allah ya taimaka daga ita sai tani dake shirin zuwa gida a lokacin sai koni dana falka banyiwa kowa magana ba nake jin yadda sukeyi da Abba din.
Da kuma fadawa Tani abinda ya faru din da takeyi a hasale tana hawaye tare da fadin kasheni suke son yi ni wanab abin ya isheni a yanzu gaskiya idan kayi magana ace kayi hakkuri don yara kuma.
To hjy idan ba hakkurin ba me za a baki yanzu halin hjy maimuna ne kin saba dashi makircine kawai irin nata ta dauka wani kudi zai turo maki ai laluran nan dashi shine take kokarin bata tsakanin ku ayanzu.
Makircine kawai irin na mata ita dai kada taga anyiwa yar uwa wani hidima sai a yaranta kadai gashi kuma Allah ya kadara yaran nata da yan uba.
Ni bashiba Tani yadda Alh ke biyewa maganan ta ya rufe ido yana neman yaciwa mutum mutunci akan zancen ta haka suka kwasa da hjy karima wanan zuwan da sukayi akan dan abu kadan yaso ya bata mata kanta ita kuma ta rufe ido taci masu mutunci dukkansu gaba daya.
Karshe sukai tafiyan