Showing 252001 words to 255000 words out of 304363 words
mutum don ni wallahi kamarninsa baiyi kama dana yayan tallakawa ba jifa jiya nan take ya kaso kudi a asibitin nan har muna dariya zai kashe dan jarin nasa wurin son a yabeshi.
Ashe yasan abinda yakeyi mune abin dariyan ke nan watau shiyasa ummah bata damu ba ta yarda akai komai tana muna kallon mai a saman ruwa ke nan.
Lalai ummah na yarda makirace sosai mama jifa koda wasa bata taba nuna hakan ba gareshi har muna mamakin ita wacan shegiyar data mara akai komai ko itama don a kuntatawa ummah ne ashe tasan komai mu suke kallo uku saura.
Ni wallahi tun farko naso nayiwa zahra sinerching dinshi amma sai naji kuna fadin wai fakirine tilis a haka zahra zata tabbata a cikin talauci da tsiya don baida hanyar yin arziki har abada.
Kunga da yanzu nice a cikin wanan daulan da kuke fada sai ta mike ta nufi wurin fridge din dake gefe a falon ta bude tana neman abinda zata karya dashi a cikin fridge din.
Aisha da mama suka bita da kallo kafin su juyo su kalli junansu lokaci guda Aisha ta fara jan tsoki itama uwar tamere baki kafin tace munafukai don hakan ne ai basu sanar da kowa koshi waye ba a lokacin don wanan salman karshen makircine ita.
Duk sukai shiru in ka debe Rukkaiya da yarta dake faman shan wani hura dayayi sanyi a cikin gora a lokacin kafin mama din tayi wani irin nisawa mai kyau tace yanzu meye manufa kun daiji abinda ke shirin faruwa yanzu damu menene abinyi.
Me za ayi kuwa mama Rukkaiya dake daga goran hura daga bayansu ta fada duk suka kallota a hasale mama din tace rufa min baki sakarai kawai ke ba abindake damun ki sai bakinci ana maganan mafita kina batunci kina fadin shirme.
Toni rabasu zanyi na fada na kara ko zan kaucewa Allah sai nayi na raba tsakanin su muga karshen munafunci indai har wanan maganan gaskiyace wallahi.
Lokaci daya duk suka zubawa uwartasu ido cikin mamaki tace kwarai ba wanda keson yaga kishiya ta fishi da ko dingon gashin gira balle na kai.
Kai mama don Allah dai ki rabu dasu hakana badai akanki suke zaune ba ai to meye na damuwa tana fadin hakan taci gaba da zukan furanta.
Waike halan baku girkine gidan ki ina kula da mun zauna kin fara neman abinda zakici ke nan keda yarki aina fada maku yanzu Faisal baida kudi ko.
Yayanshi dake bashi kudin sana,an tundana haifu ya karbe sauran kudinshi a hannushi manejin rayuwa mukeyi a yanzu so ba ko yaushe yake kawo muna abinda zamu dafa ba yanzu.
To ba kinji ba irin abinda nakewa gudu ke nan ai yanzu har in zancen nan ya tabbata gaskiyane wallahi kunya zamuji nan gaba sai mutane su fara muna ganin banza.
To shine me mama badai mai fadamuna maganan banza badai ga miji tafimu baga uba kome zasu fada su fada Rukkaiyan ta fada cikin rashin damuwa.
Kinji shirmenta ko itafa har yanzu bata gane me kike nufi ba mama bata dauki wanan a ci baya ba a wurin mu don Rukkaiya da nake gani zata iya zuwa wurinsu rokoma.
Naga alama uwar ta fada tana jefawa Rukkaiya din harara tace wanan ai akwai sakariya a zahirine kawai take fitinanna amma sam bata san inda ke mata ciwo ba ita ko kadan.
Zaune yake akatafaren office dinshi dake maitama by pass wayanshi yayi kara alaman shigowan sako ya share sakon don nai faye duba sako ako wani lokaci bashi.
Yaci gaba da karanta abindake hannunsa din wanda zasu tura gidan gwaunati don a basu daman gina masana,antan tatse madaran shanu akasa ana ssyar dashi fresh.
Sakon ya tuna ya mika hannu ya dauka yana dubawa sskone na tabnatar da shedan cikakken ma,aikaci a kungiyar UNICEF ta duniya daga Ahmed Abubakar Gusau.
What ya fada da dan karfi kafin ya tuna shi kadaine a cikin office din lokacin ya maimaita sakon yafi sau biyar yayin da idanunshi ke kafewa ga sunan mai sakon yana mamakin hakan.
Tabbas ba karya bane dansane ya turo masa wanan sakon saidai baida layinsa na Nageria wanda aka basa yana gwadawa baya shiga.
Kamar da wasa ya danna kira a layin sai ko yayi sa,a ya shiga saidai ba dauka ba har ya katse kira uku ya daina kiran layin nan ya shiga cikin tunane mai zurfi.
Haka abin yayi ta damun zuciyarshi sai bayan ya fito office a hanyanshi ta zuwa gidane ya sake gwada sa,an nasa ya kara danna kira da wani layinsa sai yayi sa, a aka dauka.
Tare da sallama cikin murya mai nuna cikakken addini ga maishi dan sauke ajiyan zuciya yayi kafin ya amsa sallaman tare da fadin .
Yau baba karami ka gama fushin naka ka tuno da mahaifin ka ke nan ina farin ciki da Allah ya nuna min wanan ranan kai abin alfaharine agareni ka gafarce don Allah da mai sunan ka nasan nayi ma laifin laifin da sai ka yafe min zan samu sukuni a zuciyata.
Shiru yaji ba amsa hakan yasa ya cire wayan daga kunnensa yana dubawa har lokacin wayan tana a kunne saidai amsawane kawai ba ai masa ba daga bangaren.
Jin shirun yayi yawa yasa ya kashe yana sauke ajiyan zuciya don yasan yaron nasa ba zai amsa ba a lokacin ke nan ya lumshe idanunsa yana murmushi a fili.
Can yaji sako ya shigo ya dauka suna gab da shiga gidansa ya duba ya fara karantawa kamar haka a cikin sauri da mamakin kalaman dan nasa yasan yana da zuciya shima amma da alaman ta dan nasa ya doke nasa a yanzu.
Ban turo maka sako don neman wani abuba a wurin ka face albarka irin ta mahaifa dako wani da yake nema a cikin al,amarinsa na yau da kullun.
Zanso ace munyi gaba dagaba irin ta da da mahaifsa sai dai ina gudun dakai da iyalinka ku dauko ina neman wani abune a wurin ku.
Zanso kasancewa dakai Abba amma ba a cikin gidan ka ko wani wurin da yake mallakinka ba don kaucewa zargin kwadayin dukiyan ka gareni don dukiyan ka bashi gaba face nasaba kawai ta mahaifi yanzu da nake nema a wurin ka.
Inda hali zan shigo Abuja wani satin sai mu hadu a Central Mosque mu gaisa idan hakan yayi maka ko kuma kawai a barshi gaba in Allah ya nufa mu gaisa dakai din .
Wani irin yarr yaji alokacin da yake karanta sakon nasa shi kuma ya zauna nan cikin motar ya mayar masa da amsa kamar haka baba karami.
Ka gama neman komai a wurina tunda ka nemi nasabata a yanzu gareka kada ka manta nidin daine mahaifin ka wanda a yau jn na mutu dole kana cikin magadan da zasu gajeni.
Shima Ahmed din yana karanta sakon mahaifin nasa ya tura mashi da amsa kamar haka masu bukatan arzikin ka su rike don hakane nake gudun zuwa wurinka a yanzu.
Idan Allah yai min budi a lokacin zan shigo cikin ku kusandani ba yanzu da ake gudana da arzikin ka ba ka gafarce idan zancena yayi tsaurin karantawa a gareka nagode.
Yaron nan ko yana da hankali wanan wani irin zuciyane masa haka har ya kasa cire nufinshi a zuciyarshi duk da yasan abinda ke nan yanzu.
Bai mayar masa da amsa ba ya fito daga motan din ya shiga gida a lokacin ne idon shi ya sauka kan motar yasir dake aje ta bugu sosai da gani anyi hatsarin gwajin arziki da ita a ranan.
Haka ya wuceta zuwa ciki bai tsaya kula meya faru ba da ace dane can baya zai tsaya ya duba yaji tun a waje ainihin meya faru da mai motan da motan haka .
Duk abindake faruwa hjy yabi na tsaye wurin tagan dakinta tana kallon mijin nata da a yanzu suka zama kamar makiya dashi a gidan.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
[6/26, 10:43 PM] Zainab Idris Makawa Writer: 🌱TUMFAFIYA UWAR KWANKWANMAI ,,,,,,,,,,
🌱TUMFAFIYA BAKI FITA A WURIN BANZA ,,,,,,,
🌱TUMFAFIYA SIRIN KI SAI ALLAH ,,,,,,,,,,
ZAINAB IDRIS MAKAWA
8️⃣6️⃣
ONLINE PAID NOVEL YARUWA KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMA DARI BIYAR NE DON KIRA 08036959257 KO BIYA KI AIKA 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KATIN WAYA MUN GODE UBANGIJI YA BAKI IKON BIYA AMIN,,,,,,,
Dije waya daure wanan akuyan jiyane data banye Ahmed dake tsaye rike da abincin dabbobin yake tambayan kakar tasa banyewa kuma yaushe ta banye don koda safe da zan shiga bandaki ai a daure take banga alaman ta banye ba.
Kallon mamaki yakewa kakar tasa ganin haka yasa tace dashi amma barin tambayi uwarku inji ko itace ta daureta ko kuma wata daga cikin yan uwan naka ta daure.
Kai ban tsamani don naga kamar ai ba ruwansu da dabbobinsu barshi kawai kila dai na mantane ya fada ya nufi hanyar shiga wurin dabbobin dauke da abincin nasu.
Yana isa itace ta farkon tasowa da farko ya dauka cewa saboda abincin data gani a hannunshi yasa ta nufo shi amma sai yaga sabanin hakan don jikinshi takebi da sunsuna tana dona kanta saman jikinshi.
Baya jin komai game da akuyan don haka ya dauki hannunshi ya dora a kanta ya fara sosa mata saman kan nata a hankali yana shafan bayan ta har zuwa tsawon wani lokaci.
Kafin shima ya sauke ajiyan zuciya yana fadin uwar garke bari naba yan uwaki abinci kada muyi laifi a wurinsu kuma daga haka ya duka ya fara kokarin bude ledan abincin nasu ya fito da harawa ya zuba masu nan suka rufe daci shi kuma ya fara gyara masu wurin da yai kwana biyu ba a gyara masu ba.
Kamar ance ya dogo kai ya kallo iccen tumfafiyan sai yaga alaman wasu ganye suna ja a jikinshi shi a zatonshi iccen ne keson mutuwa a lokacin don haka ya nufi wurin da zuma ya kai hannu ya duba.
Aikuwa daga can wanan akuyan ta soma wani irin kukan nan nata mai nuna inkiya ga mutum lokacin da wani abu zai faru da mutum din a lokacin da sauri ya cire hannun shi daga iccen yana kallon akuyan dake kuka tana tuma tana nuna alaman kada ya taba icen sai kuma ya koma kallon iccen ya dan kurawa icen ido kananan tuho yagani a jikin iccen sun tartso a jikinsa ya sauke ajiyan zuciya tare da dukawa ya dan fara tsuntar busasshen ganyen icen daya fado kasa yana tarawa don yana da bukatanshi.
Kafin ya fara kawar da kayan da aka watsar da shara a gindin itaciyar ya share wurin tas har ko ina yana Allah waddai da hali irin na kannesa dako shara basa iya yi suna mata dasu .
Har sai yar tsohuwan dake fama da kanta wani lokacin ta duka ta gyara wurin da kanta haka kuma ba kunya zasu kara bata wurin saboda basu da kwabo.
Har lokacin wanan akuyar uwargarke tana tsaye ta kafa mai idanu saida taga ya kauce daga wajen lokacin tayi kamar ajiyan zuciya irin na mutane ta soke kai ta fara sunsunan abincin daya aje masu din.
Ya gama dasu shine ya dawo falo ya zauna yaci abinci lokacin ne ya bugawa mahaifinshi waya don haka kawai yaji yana kewan mahaifin nasa yana son yajishi yaji yaya muryan mahaifin nasa take ya dauki waya ya danna masa sako don yasan zai kira idan yaga sakon nasa saidai bai dauka haka da wuri mahaifin nasa zai kirasa ba.
Sai gashi nan take yana ganin sakon ya dauki wayan ya kirashi shi kuma yaki dauka ya fito daga daukoni ya ajeni asibiti wurin Abba zai dawo gidane ya tsaya wani shigo yayi sayayya don inna ta fada mai kayan miyarsu ya kare.
Ita kuma a zatonta yana asibiti yana dawainiya da yan gidan mu shine ya fita batunsu har kayan abinci ya kare bai sayo masu ba don haka ta sameshi a part din mu tayi mashi tas tana fadin cewa ya kama dangin mace ya fita batunsu su.
Shine dalilin tsayawanshi ya sawo masu abinda tace din ya kare masu lokacin saiga mahaifin nasa ya kirashi da wani number sai ya dauka ba tare da sanin shibane a lokacin don da bai daga wayan tasa ba ya nasa a zuciyar shi.
Sai gashi kuma ranan ya kasa barci don tunda na dawo naga canji a fuskanshi saidai bansan abinda ya sameshi ba bai kuma fada min ba don haka na dauka ko dashi da inna ce a lokacin.
Washe gari aka sallamo Abba da safe don haka ban samu zuwa ba sai weekend na shirya zuwa gidan namu da sunan idan naje a can zan wuni saida yamma zan dawo gida.
Sauri nake ina ta dan aikin da zanyi lokacin ne na dago jakkarshi da yai tafiya da ita zuwa bambarake tsuki naja don sam na manta da jakar a wurin tun lokacin daya dawo din.
Na dauko jakkar a cikin sauri ina kokarin cire kayan dake cikin jakkar naga kullin maganin daya dawo dasu kamshin maganin kawai naji saida kaina yayi wani irin sarawa lokaci guda a saman gado na dora mashi su naci gaba da aikin da nake ga warin maganin yana shiga min hanci ba dadi a lokacin.
Ya dawo daga sayen kosai ya shigo dakin tun daga kofa yaji kamshin maganin ya fara dan waige waige yana duban ko ina na falon kafin yace zahra na amsa mai daga ciki ina fitowa daga bandakin dana gama wankowa a lokacin.
Na fito muka hade a kofan falon yake fadin naji kamshin wani abu a dakin nan mai daga hankali nima yanzu na dauko wani leda a cikin jakar da kadowa tafiya dashi ga yacan saman gado na ajema na fada mai ina kokarin fita don kaina dake sara min a lokacin.
Waje na koma na zauna jina shiru ban shigo dakin ba yasa ya leko wajen yana fadin wai aiki kikeyine kizo mu karya zaune ya hangoni nayi tagumi da hannu daya ina sakin hawaye a fuskana.
Subbanallahi zahra meya faru ko Abbane shiru zahra ya kara maimaita sunan yana kiran sunana tare da dan girgizani idona yana kafe wuri daya banko kyaftawa.
Innalillahi ya fara nanatawa a bakinshi kafin ya juya zuwa dakin da sauri ya dauko wanan maganin da aka bashi ya bani yana zuwa ya turmuza min a hanci kafin ya fita da sauri zuwa wurin su inna ya debo garwashi a murhu saida ya kamo hanya ya fara kwalawa Dije kira yana fadin Dije dije dije da sauri bai tsaya ba ya nufo part din mu kuma.
Bai tsaya rufa min komai ba ya zuba hayakin hakana ya tara a fuskana yana dan hura hayakin dake tashi da hannunshi zuwa jikina kuka sosai na fara cak ya mike ya daukeni zuwa kuryan dakin mu kafin ya fito zuwa dauko bin hayakin ya shigo dashi.
Amadi lafiya kuwa muryan dije ke tambayanshi daga kofan ga kuma wanan bakar akuyan nasu ita da tan uwanta sun dauki ihu lokaci daya daga can ciki yake ba dije amsa da shigo dije zahrace wallahibta rikice min yanzun nan fa.
Subbahanallahi meya faru meya jawo hakan ta fada cike da kulawa tana karasowa cikin dakin idonta ya sauka a kaina ta fara fadim aashaa dama tana dasu ke nan dai eh tana dasu saidai ban tsamanin suna tashi haka dama.
Ko yanzu wani maganine dana zo dashi shine sanadin tashin nasu yanzu din don maganin yana da karfi sosai gaskiya wallahi ban ma san lokacin data dauko maganin ba na dawo daga sayen kosai na samu ra fito dashi a jakata yana magana yana kokarin maida hankalinshi a kaina ya fara karanta min addua kafin ya koma kira,a suratul sulaimana.
Har akaci aka sude wai inna basuji duk abinda ke faruwa a wurin mu ba sukace don sun koma daki sun rufe suna barcin safe a lokacin hakan ya hana masu jin abindake faruwa a lokacin.
Barci na samu nayi sosai sai sha biyu na mike ina salati tare da kallon lokaci ina kokarin son in tuna abinda ya faru dani amma na kasa hakan saidai jin jikina da nakeyi kamar andokeni konayi wani aikin wahala.
Kin tashi ke nan ya fada na amsa mashi da eh kawai ina kwance zakici wani abune yanzu naje na sayo maki ya tambayeni cikin kulawa nace bana jin cin komai.
To dan daka ni kazo ka fita min da wanan mashin din daya tare muna hanya mutum yana cikin daki da mace tun safe ya kasa fita ko ina dan sana,anma da kakeyi yanzu nema kake ka daina in an kyale ka duk saboda mace.
Innace tsaye a kofan falon mu take fadin wanan maganan cikin daga muryanta wai zata fita da kaya mashin dinsa ya tare mata hanyan da zata fita tace.
Baiyi magana ba naga kawai ya mike ya fita zuwa wajen can naji muryan shi yana fadin haba inna na dauka ai ko kare na kawo gidan nan da sunan nawane zaki kula min dashi balle matata zahra inna.
Nina rasa me yarinyar nan ta tare maki kullun kike hattaranta