Showing 180001 words to 183000 words out of 304363 words
masu karfi bane a garin tallakawane tilis inba Allah yai masu wani budi daga baya bane irin haka dole ke nan yaron a yanzu yana can cikin wahalan rayuwa.
Bayanshi yana nan da nasa iyalin a cikin daulan duniya da jin dadin rayuwan da bai musaltuwa a lokacin son shidin ba mutum bane mai tauye iyalinshi.
Yanzu ina zai fara bullowa wanan matsalan da wani ido yanzu zai baiyana garesu yace yana neman dansa dan da baisan cinshi da shansa ba har ya rayu yakai wanan shekarun masu yawa haka ?
Dolesu jauro zai nema a asirce kamar yadda yanzun ma suka tunatar dashi hakan asan yadda za a bullowa maganan da wuri kada ya mutu ya bar baya da kura kuma don yasan halin matarshi ba yarda zatayi da hakan ba shi yanzu ina zaikai wanan alhakin a rayuwan shi.
Godiya da tasbihi ya shiga yi a zuciyan shi yana mai lumshe idanuwan shi kadai yasan yadda yake ji a zuciyanshi yasan alhakin hakan dole ya kamashi a wani bangaren rayuwa.
Hjy Yabi ce ta shigo part din a lokacin jin motsin mutum yasashi dago kai ya kalli mai shigowa dakin a lokacin matarshi ya gani hakan yasa ya sauke kanshi kasa daga kallonta.
Barka da hutawa yaji bakinta na fadi yau karo na farko azamansu kunuwanshi ya jiyo mai hakan a bakinta a ciki ya amsa mata ta samu wuri ta zauna tana mai kallon fuskanshi dake daure lokaci guda.
Alh wai da wani matsalane ka canza gabadaya cikin yan kwanakin nan mu bamuji dadin kaba kai kanka bakaji dadin kanka ba kuma kaki fada muna abindake faruwa mu sani ?
Lafiya nake haka dai naga shine daidai yanzu don naga kina kokari dake da diyanki ku maidani mace ke ki zamo miji a gareni yasa na daukarwa kaina matakin hakan shine kawai ya fada yana dago kai tare da kallonta.
May ya kawo wanan zance kuma ana zaune kalau zaka fadi haka a cikin mu waya nuna maka cewa baka a matsayin ka na ubangidan nan yamzu ?
Nina gani na fahinci hakan don haka nake shirin daukam matakin daya dace dani a yanzu wanda shine daidai gareni gako wani magidanci kuma.
Gaban hjy yabine yake wani irin faduwa don abinda take tunane shidin take ganin ya faru a lokacin hakan na nufi duk wani shiri na sihiri da kulli da sukai mai suka daureshi abin ya karye a yanzu haka ke nufi.
Cikin karfin hali irin na hamshakan mata tace dashi kai Alh wanan zance ai bai kamata a bakin ka wani power naka zan dauka ko yaran nan su bani bayan kowa yasan a karkashim innuwan ka muke rayuwa a gidan nan.
Idan ma Baku sank ba said Ku fara sank son Abubakar din da kuka sank a baya bashi bane yanzu kuke kallo wanda kuka mayar dashi da banza duk days a wurin Ku.
Shiru tayi tana Dan kakaro murmushin dole a fuskanta don tunanen ta ya wuce abinda takeji a gareshi yanzu dole wani aikinsu na baya ya samu matsala a wani bangaren .
Inko haka tasan akwai aiki a gareta babba yanzu don't yaushe zata iya tuna wani abinda akai mashi a baya ga kuma hjy Korau uwar rikon nasu sun samu matsala yanzu da ita akan yayanta.
Zakace ba haihuwa akayi ba a lokacin don't yadda naji gidan shiru koda yake darene a lokacin watakila kowa ya nufi gidansa sai kuma gone su dawo ga yadda nasan aal,adan yan uwan my ko garin mu
In an haihu kai maigida ka shiga uku don yawancin yan uwa a nan suke tarewa kullun suna gidan sai dare za a watse said bayan suna kafa ya dauke.
Shine abinda ya bani mamaki a was a wanan karon data kofa muka tsaya muna sallama kusa sau ukku ba a amsa muna ba kallonshi nayi ganin haka yasashi daga muryanshi da karfi ya kwada sallama a daidai lokacin aka bude kofa.
Mama hafsice zata fito tsci karo damu tsaye a kofan dakin cikin mamaki ta amsa muna sallaman tana fadin ashe bakine daga can ciki naji mur I an mama tana tambayanta da su wayene a kofan ?
Nice mama nayi saurin bata amsa kafin mama hafsi din ta bata amsa ta bude muka shiga au Zahrace ashe yanzu like tafe aina dauka bakiji haihuwa ba ma son ban ganki ba ?
Naji mama dazun nan ummah takirani tana fada min anty Aisha ta haihu barkan mu da arziki ubangiji Allah ya rays muna bisa kan sunna amin.
Nafada freely da murmushi a fuskana tace amin gaba daya hankalinta na kaina tana kallona daga samana har zuwa kasana lokaci guda nikuma na fahinci hakan.
Nasan ba komai take kallo ba sai shigana na lokacin duk da ba laifi amma ita taga kasawa a hakan dama shi take son gani a gareni don' komai daya shafeni baya burgeta ita.
Ki shiga suna ciki tare da hjy tsohowa cewa kakan mu sai nace a cikin kunya tare muke dashi yana kofa yazo yai maku barka shima OK tare da mijin naki kike ashe ?
To kije ki shigo dashi ciki mana ta fada a cikin izza da isa iron nata na mike na fita ta bini da wani kallo mai kama da harara tana jan tsoki tare da kawar da kai gefe daya.
Nayi masa iso da mu shiga daga ciki na juya zan shige naji ya dan jawoni na juyo kudi ya danka min bansan ko san ko nawa bane nayi godiya yace No da sauri.
Ina gaba yana biye dani a bayana zuwa ciki yayi sallama suka amsa mai su ukune zaune a falon lokacin har kasa yakai ya gaidasu kafin ya fara masu barka da karuwan da aka samu din.
Rakiya kira masu hjy nan su gaisa ta fada a gadarance don mama badai magana a gadara ba kan balle ta samu wurin yi a yanzu.
Jin hakan yasa nasan ba sai mun shiga ciki ba kenan a nan zasu zo mu gaisa dasu son azato har maijegon din amma sai naga hjy ta fito ita kadai dakin itama saida ta jima ta ja muna rai tabarmu a zaune shiru a falon kafin can ta fito tana Dan dingisawa irin na manyanta.
Su waye ke neman ta fada a gyatsire tana kaiwa saman kujeran farko dake falon bayanta kalle mu gata nan takwarankice ita da mijinta sukazo barka mama ta fada har lokacin tana mike a saman dogon kujera da waya a hannunta.
Waye takwaran nawa ta fada kamar bata shedani ba tana wani gimtse fuska a cikin daurewa mama tace gata maisunan kicefa ta nan gidan.
Yanzun taga daman zuwa ita issasa duk yan uwa dake nuna farinciki sunzo sun tafi wani iri naji a lokacin, bansan lokacin da nace muma ai farin cikin mukazo nunawa kedai hjy duk da kin dade bakiga mutum ba sai kin yaba masa magana son ranki.
A,a makka kikaje karshen dadewa ina kina cikin garin nan dai karshen dadewa unguwar sullubawa da kika zabi zama.
Sai naga mama ta kalloni ban fasa maganan ba naci gaba da fadin yanzu da naji din bagashi munzo tun ba,a kwana ba ?
Ke kada ki shiga min ido ana magana kinayi har wani aure kikayi na gwadawa tsara da kike ganin wuyan ki yakai yanzu da zaki fadawa mutane magana yadda kike so .
Tashi muje ya fada a hankali daga bayana inda yake zaune din itako taci gaba da fadin masu manda da uhumm basu rawan kan aure.
Naji zafi naji ciwo a raina amma saina dake INA fadin in auren banzane kije kiyi mana ai naggidan ai zawarawan fake sonki had yanzu na mike da zuman shiga dakin naji mama Rakiya na fadin Aishan ko ta samu barci fa.
OK in ta tashi a gaida mun ita muna mata barka da sauka lafiya ya mike yace mama zamu tafi Allah ya raya muna na mikawa mama rakiya kudin daya bayar abawa jaririya nace ga wanan inji shi asaiwa jaririya kwali.
Kai haba dai kana fama da kanka da iyali cikin Dan kunya yace ba komai mama ayi hakkuri dashi son Allah to an gode ta fada nayi mask saida safe muka fito zuwa part din mu.
Nan ma bamu dade ba min gaida ummah ta tambayemu mutanen gida na barsu tana kara mashi nasiha na shiga wurin kannena har sunyi barci a lokacin.
Mukai mata sallah muka fito bar muka hau mashin din my banji yayi magana ba a lokacin zuwa gida don haka nasan ranshine ya baci sosai nima nayi shiru.
ZAINAB IDRIS MAKAWA[30/04 8:14 AM] Ummu Ammar: 🌱TUMFAFIYA UWAR KWANKWANMAI ,,,,,,,,,,
🌱TUMFAFIYA BAKI FITA A WURIN BANZA ,,,,,,,
🌱TUMFAFIYA SIRIN KI SAI ALLAH ,,,,,,,,,,
ZAINAB IDRIS MAKAWA
6️⃣2️⃣
ONLINE PAID NOVEL YARUWA KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMA DARI BIYAR NE DON KIRA 08036959257 KO BIYA KI AIKA 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KATIN WAYA MUN GODE UBANGIJI YA BAKI IKON BIYA AMIN,,,,,,,
Zahra kiyi hakkuri don Allah nasan duk nina ja maki wanan abin da yan uwanki ke maki don da ace bani kike aure a yanzu ba wani can hamshaki nasan da dole sunayi dake.
Amma yanzu aurena yasa duk suna ganin ke ba kowa bace a cikinsu yanzu don ban taba zaton har hjy da girmanta zata iya fadin wanan maganan haka a gabana ba sai gashi a yau ta fada naji.
Uhumm ka dauka donkane take wanan maganan wai itafa hjy haka take ga duk wani dan dakin mu duk sanda muka hadu ba a kwashewa lafiya da ita saita yaba muna magana.
Ni na saba da irin wanan halin nata don ba yau ta fara nuna min hakan tun ina gaban ummah haka muke kwasa da ita dama.
Amma duk da haka na yanzu yafi dukda bansan nada din ba yadda kuken sai nake ganin kamar don kina aurena a yanzu ina fakiri hakan murmushi kawai nayi ba tare da nayi magana ba shima bai sake fadin komai ba lokacin.
Munkai bakin wani shago ya tsayar da mashin din yana fadin bari na dan shiga in fito ya sauka saman mashin din zuwa cikin shagon.
Yadan jima ya fito dauke da ledoji guda biyu ya miko min na karba ya hau mashin din yana fadin kayan teane a ciki naga wanan sun kusa karewa kuma zan dade wanan karon ban dawo ba gashi teane abincin ki ke.
Na karba har lokacin banyi magana ba don raina ya gama baci da abinda hjy tayi min a lokacin don koba komai ya kamata ta raga min tunda muna tare ai.
Washegari sammako yayi yabar garin zuwa zaria don haka danayi barcina na tashi na fara gyaran dakina daduk part dina ina tsaka ga aikinne na fara jin kukan dabbobin har yana shiga raina.
Gashi nayi alkawarin ba zan sake zagawa baya inda suke daure ba don na tsorace da lamarinsu sosai gaskiya don hakane na kyale ban zaga inga ko kukan me sukeyi ba.
Kukan yayi yawa don haka nayi tunanen yunwa sukeji gashi da alama ba wanda ya damu da kukan nasu lokacin haka kuma nayi tunanen ina Dije take don tana da kokari dasu gaskiya.
Kamar wace akaba umurnin tashi haka naga na tashi na nufi wajensu kai tsaye tun daga nisa na hangosu tsatsaye sai kuka sukeyi.
Suna ganina duk suka maida hankalinsu gareni lokaci guda basu da komai na abinci wurin don hakane na dauki tsitsiyan gyaran wurin a karo na farko na fara share wurin a tsorace.
Na koma part dina na debo masu ruwa don ni baya tafiya ba wadatani da ruwa ba sai ya cika min komai nawa na zuba ruwa yadda zai wadataceni zuwa wani lokaci.
Na debo na dawo ina zuba masu naji muryan Dije a bayana tana fadin yauwa yar albarka yanzun nake fada da yaran banzan nan su taso su duba minsu sunki zuwa shine na lalabo nazo in duba .
Tun safe ina daki kwance bana jin dadin jikin nan nawa sannu nayi mata tare da tambayanta meke damunta lokacin tace jikintane ke ciwo alaman zazzabi a jkkin nata dai.
Abincinsu dake cikin buhu na jawo na zuba masu banyi aune ba saiji nayi a bayana kamar za a kasheni ashe uwar garkene daga inda take ta sako min kahonta ajiki tana dona kanta jikina.
Bansan lokacin dana sake sauran abincin ba ya zube kasa na kwasa da gudu zuwa wurin Dije ina haki don na tsorata da hakan.
Lah akuyan kike tsoro kuma diyar nan me akuya zatai maki kuma ta fada tana karasawa zuwa wurin dana fito ta duka tana kwashe abinda ya zube din .
Aike amarya godiya take maki da hakan idan dabba taji dadi hakan takewa mutum ta shige a jikinshi shine godiyansu ai sai kuma ta koma fadin yaudai angon namu ya tafi.
Allah ya tsare muna shi ya kare yanzu kan ai yayi nisa ga tafiya da yardan Allah ta fada duk hankalina nakan wanan bakar akuyan banyi aune ba naji ta saki wani irin kuka lokaci guda saida na kara kaduwa a hankali na sulale nabar wurin a tsorace da ita.
Shigowan ta falon bai hanashi wayan da yakeyi din ba wanan karon bai kuma fasa fasin abinda yake magana a kai ba don ta shigo falon lokacin saici gaba da fadin da yayi.
Dane na cikina shekara ashirin da bakwai zuwa takwas ke nan yanzu rabona dashi a nan cikin zamfara suke indai ba barin garin sukayi bayana kai bama inda zasu don kowa nasu yana garin.
Gabatane yayi wani irin mugun faduwa lokaci guda zancen da bata taba kawowa kusa ba ke nan a ranta sai gashi taji yana waya akan hakan don haka take duk wani annurin jikinta ya gushe lokaci guda.
Karfi hali tayi ta zauna har zuwa lokacin da ya gama sauraren abinda mai wayan ke fada masa a lokacin don ba jinsu takeyi ba daga inda take zaune din ba.
Nagode Alh ina sauraren ka insha Allahu zan kara jira inji inda zancen ya kwana don Allah aimin kokarin hakan ina cikin wani hali kan wanan zancen a yanzu.
Nan kan ta kasa hakuri ta danne zuciyarta don saida ta kalloshi a cikin wani irin razana ya kashe wayan yana dorawa saman dan karamin table din gabanshi tare da dago kai ya kalleta .
Alh wani zancen naji kanayi yanzu ta fada daidai lokacin da yake kawar da kai daga kallonta lokacin hakan yasa yayi wani irin juyowa a ciki mamaki ya jefa mata wani irin kallo lokaci guda kafin yace.
Meya shafeki da wayana yanzu ko dama kin zauna ki sauri abinda nake fadane wai inma son ki sani kikeyi to ina zance akan dana Ahmed mai sunan baba dana haifa da matana ta farko a zamfarane.
Zubur ta mike tare da nunashi ido rufe tana fadin wana zancen ma karyane wallahi dan da ka samo a cikin duniya kabaro shi can yanzu zakace zaka daukoshi a matsayin dan cikin ka kuma ?
Ohh dama haka kuka dauka shine zatonku bata hanyar sunna na haifeshi ba shine dalilin watsar dashi danayi a rayuwana kome inma zatonku ke nan ku jaye don dane na halas kamar ko wani da a cikin gidan nan shima.
Kaika san wanan zancen don duniya bata sheda hakan ba gareku don haka ina da ja akan wanan zance nida yayana kan hakan ta watsa mai wani irin kallo ta nufi hanyar fita daga falon a fusace.
Tsuki yaja ya bita da kallo shima ya mike a fusace ya fito daga falon ko kallon abincin data aje mai baiyi ba a lokacin driver shi na ganinsa ya taso da sauri ya bude mota suka shiga sauran motan ma suka biyosu a baya lokaci guda.
Bai tsaya ko ina ba sai airport inda jirginsu zai tashi zuwa adamawa daga can zaibi motan dake jiranshi a can zuwa mambila garinsu na haihuwa.
Hjy kuwa tana fita dakinta ta nufa ta figi waya tanayi da yarta a cikin kuka take labarta mata abinda ya faru tsakanin su hankali tashe.
Saida yar nata ta gama saurarenta ta katseta da fadin ke kam yabi baki da wayau wallahi kin fa san da zancen nan a baya.
Don me yanzu zaki nuna hakan don da daya ya shigo cikin ku yanzu me zai fiku dashi ko me zai kaiku a rayuwa yaron dama ya rayu a cikin talauci da tsiya yabi in kin kwantar da hankalin ki aisai yadda kikayi dashi dagashi har uban nasa.
Dama na fada maku wanan ranan yana tafe ki shirya mashi kikace a,a keda hjy aikun gama da wanan matsalan ba zaisake wawayen yaron nasaba a rayuwanshi yanzu gashi ba aje ko ina ba ya fara wanan zancen.
Don Allah Nkki ki bar wanan zancen yazu bashi bane a gabana mafita nake duba a yanzu ta fadawa yar uwanta cikin zafin rai taci gaba da fadin na kulla Nkki baki san zafin hakan ba ka hada dan uba da diyanka yafi komai muni a rayuwa.
Nkki din tace ina zan