Showing 201001 words to 204000 words out of 304363 words
zakai arba,in da wani abu sama ke kuma ga wata nan zakuyi aiki tare zan baku a wata dubu arbain da biyar duk wata maigadi kuma dubu arba in.
Kallon juna sukeyi kafin Bala driver yace Alh ai dama ni sha biyar ake bani duk wata yace what yace kwarai kuwa Alh ga yan uwana nan ka tambayesu kaji maigadi yace goma ko takwas ake bani ba da abinci ba hakama mai wanki da guga.
Wani jiri ne yaji ya dabeshi lokaci daya ya dafa motan shi saida driver shi ya karaso yana fadin Alh abi a sannu sun sha min wanan korafin lokaci lokaci ina basu hakkuri.
Watau shi kadine ake ba kudin shi daidai ke nan a cikkn su shima don kudin basa yana fitowa daga company sune yasa haka da wurintane zata gunce ta basa rabi ke nan ?
Wai me hjy ta dauki daukan alhakine a rayuwan ta ya tambayi kansa lokaci guda kafin ya juya zai shiga mota da sauri driver yazo ya bude masa saida ya zauna ya dago kai ya kallesu yace.
Daga yanzun nan biyan kudin ku zai dawo hannun hassan gashi kowa ya koma bakin aikinsa suka amsa suna godiya suka koma shi kuma suka fita da driver shi.
Duk abinda ke faruwa a gaban idon hjy Yabi dake tsaye a window dakinta tana kallo saidai abinda ta kasa fahinta shin Alh ne ya tara dukka yan aikin har Asabe mai aiki ko kuwa dai Asaben ne ta kai karanta ya kirasu.
Ganin ya fita yasa ta sauko kasa gagauce tana kwalawa asaben kira lokaci guda gabanta ya fadin jin irin kiran da hjy din ke mata a lokacin Asabe uban me kukeyi waje da Alh dukkan ku ?
Hjy shine ya kiramu yana kara muna kashedin aiki a gidan nan shine kika ganmu akan me tace akan dai zuwan hjy karamane dai ya kiramu din yana bamu umurni.
Ashe ko duk zaku bar gidan nan kuwa duk wanda ya ketare dokan dana saka mashi albashin ne hakan ta barta tsungune ta fice daga falon can ma amsa daya ta samu nan ma din tayi masu bara zanan irin wanda taiwa Asabe din a cikin gida.
Shigewan ta maigadi ya kalli mai wanki yace rabu da idan duniya taso basheka haka kake komawa kamar tababe a cikkn mutane mu ai gaba zuwan matan nan ya kaimu don zuwanta ya zama muna alheri a gidan nan yanzu.
Daki ta koma tana daka hannayenta a wuri daya babu abinda take fadi sai watau akwai dan karamin yaki gabanta kwanan nan ita da Alh a gidan na ke nan kan zuwan wanan kuchakar yar kauyen matar nasa.
Har yaushe murja ta zama mace a wurin sa da har yake wanan rawan kafan akanta yanzu indai hakane ya zama dole itama ta nuna mata cewa bata kaiba kuma bata isa ba don ita bakuwace a wanan harkan.
Zata gwada mata gaba da gabanta ko a wanan harkan na bin bokaye da malamai don meke ga murja da har zata kai masu.
Mamaki da tunane ya hannashi magana ba abinda yake tunane a lokacin sai yadda yai sakaci haka a rayuwanshi har yabi ta shige mashi gaban komai na rayuwan shi daya kamata ace shi namiji shine ke kula da duk wanan abin a gidan sa wayan shi ya dauki kara ya dauko ya duba dansa yasir ke kiranshi a lokacin.
Cikin ajiyan zuciya ya dauki wayan tare da fadin salamu Alaikum sai dan ya amsa da hey dad ya kuke ya yanayi bakaji sallaman danayi ma bane ka amsa min da wanan kallaman uban ya fada rai bace.
Meye a cikin haka kuma dad dama na kiraka ne na tambayeka ko mum ta fadama ina bukatan kudi banji an aiko min dashi ba ya fada a kasalance irin na sagartatun diya.
Bata fada min ba kota fadama yanzu ba zan turo maka da komai ba sai wata ya cika don yau sati biyu ke nan dana saka ma kudi ga accoun din ka.
Why dad kafa san kudi shine rayuwa zan zauna ba kudine a hannuna cikin hasala uban yace idan ban sako maka ba ka mutu can ya kashe wayan nasa yana tsuki tare da fadi a fili malam Sale nayi sakacin da a yanzu nake nadaman shi a rayuwana.
Alhaji hakan ba yin kanka bane duk aikin sihirine ga yadda alama ya nuna yanzu kamar ka kurto daga daurin boyen da akai makane a baya.
Don abin yana da mamaki yau kaine ke tsaye haka kan hjy wanda a baya a gaban kowa kana iya bata hakkuri kan abinda bai taka kara ya karya ba saidai na tare dakai yaji haushin haka.
Wanan gaskiyane nima a yanzu ina wanan tunanen da ada bai taba kawo min ba a zuciyana sai yanzun nake dan gane kuskurena.
Sayayya sukayo kashe rika a wani sabon store dake kusa dasu a can magariba ya samesu don haka yana dawowa sallah ya fara gabatarwa kafin ya fito don yaci abinci karo na farko tun bayan kauracewa cin abincin gidan dayayi na yan makwani a gida.
Babu komai saman dinning din a lokacin hakan yasa daga inda yake tsaye cikin daga murya yake kiran Asabe mai aiki da karfi karo na farko da suka fara jin hakan gareshi don dauka suke baima san sunnanta ba duk zamanta a gidan.
Itama din a gigice ta fito daga kitchen inda take faman wanke kwanonin da tayi amfani dasu da yamma din tazo da sauri tana rusunnawa tare da fadin Alh gani.
Cikin daure fuska yake tambayan ta yau lafiya bai samu abincin shi a falon bane yadda ya saba sai tayi kasa da kai don rasa na fadi a lokacin ya kara maimaita tambayan nasa da fadin yau baki girka abincin dare bane a gidan.
Alh na girka hjy ce tasa na zubar wai ba wanda zaici yau a gidan ta bani umurni da hakan kuma kin zubar din sai tayi kasa da kai can ta dago tace Alh ka gafarceni na zubar amma ba duka ba saura na kitchen na aje.
Kina iya tafiya ya fada a sanyaye kafin ya juya nufi dakin shi ya kira malam sale driver a waya ya bashi umirnin a shigo masu da take awaye na tuwon shinkafa mai kya guda goma.
Motan farko na garin zaria ya bi zai sauka a maraban Funtuwa daga nan motan bata tsaya ko ina ba sai inda yace zai sauka din nan mota ya tsaya ya sauka.
Sunan unguwar ya fadi mai mashin din yace ya hau su tafi a hanyane yake tambayan mai mashin din ko yasan malam idi mai rafannai a unguwar ?
Yace kwarai kuwa duk garin nan waye bai san shi ba aiba bace yake ba da kayi mai inkiya da wanan sunan gidansa zakane muje can din ?
Yace eh bai tsaya ba sai kofan gidan kamar yadda ummah ta kwatatabta mashi gidan haka ya samu wurin daga kofa ya tsaya ya sallami mai mashin din.
Kafin ya tattaro natsuwa yasawa zuciyan shi ya samu yaro yace ai masa sallama da maigidan bakone daga gusau yace ace dashi bako daga wurin salamatu ko ?
Yace eh daga wurintane yake tafe akace ya shigo ya shiga daga zauren gidan ya sameshi zaune a zauren saman wani katon farin buzu na fatan rago ga tulin littatafai daga gefen shi sai goruna dake aje da ruwan rubutu wasu har kura ya hau kansu don dadewa a wurin.
Sallaman Ahmed din yasa shi dago kai tare da dan kura mai do har lokacin da ya kai zaune yana fadin barka da warhaka malam mun sameku lafiya ?
Alhamdullahi ya fada yana kawar da allon dake gabanshi lokacin yace zama tsakanin gusau zuwa nan ya koma kamar tafiya zuwa unguwa dazun da safe nan naga zuwanka nan gashi cikin hukuncin Allah har ka iso.
Eh malam ana fitowa daga sallah na nufo nan din don in samu in koma da wuri insha Allah dama ummah ce ta turoni nan wurin ka don matsalan , , , ,
Hannun daya daga mai yasa yayi shiru lokaci guda yana kalon malam din shi kuma kamar mai sauraren wani abu a lokacin zakace yana magana da wani ko yana sauren abinda ake fada mai a wayan kafin ya daga yace na,am ya kallo Ahmed din yace.
Kayi saurin gano matsalan matarka cikin lokaci don ta riga da ta firgice tun a cikin mafalkinta da tayi a ranan sai kuma aka samu wasu shedanu dake son bata tsakanin ku a gefe wanan yasa harta kai kwance.
Lamarin ai mai sauki ne don daga kai har ita akwai tsari na Allah a tare daku da ba yau ba wanan bakar matan dake bibiyan ku koda yake su biyu ne na gani da suncinwa manufarsu akan yarinyar nan.
Sakaci irin na salamatu yana ban mamaki da yaya aka samu suka sakar mata mahaifanta harta samu rabon diya a duniya don lamari da mai tsafi abune mai wuyan sha,ani tasani.
Yanzun dai ba dogon bincike zan baka wanan kaje yau din nan ku shaka mata zatayi barci sosai kada ku damu ita da kanta zata tashi har ta nemi abinci taci.
Don zasu koma gun wace tayi amfani da damanku ta turo maku abin saboda sakon bana yau bane sun dade suna son kafan da zasu shigeta basu samu ba don irin abubuwan dake kanta ba nawasa bane.
Abubuwan kanku kusan gudane kuma Allah ya gyara fararene ba masu cutarbane su shiya komai naku yake zuwa da sauki ko wani lokaci.
Ga alheri nan babba tafe ma da sunan ka zai amsa sosai za a sanka zakayi suna mai ma,ana nan gaba kadan insha Allahu amma akwai kakubali hakan a kanku.
Ka zama namiji sosai a wanan lokacin kada ka zama cikkn butulai yan adam masu manta halarci kaci gaba da rikon ammana duk yadda yazo maka.
Karbi nan wanan ya isa hakan kaje kuyi amfani dashi ku duka Allah ya tsare ya kare jeka kada rana yai maka ka koma zuwa garesu.
Malam na gode ya fada yana amsan dan goran daya miko mashi din yace ba komai kadai kula da abubuwan dana fada maka din zaifi.
Yaya kakar ka da akuyan ku tana nan dai kuna cigiyar mai ita ko ka hutar da zuciyar ka ba zaka taba ganin wanan dattijon ba don taimakon ka yayi ta wanan tsigar.
Kayi hakkuri da zancen mahaifin ka don duk abinda ya faru bayin kansa bane asirine mai karfi yake aiki a kansa tsawon lokacin nan amma ka godewa Allah don a sanadin ka komai ya karye a yanzu.
Zai nemoka da kansa da taimakon abokanan sa da sukai masa tsaye dakai ancinwa manufa yanzun sai dai sun koma zargin wace bataji bata gani ba kamar yadda abubuwa ke faruwa a gidan sarakan ka a yanzu da nan gaba zasu kokawa hakan.
Jeka a dunkule na baka bayani da sannu kanka zai hasaka ka gane inda zancena ka yanuf dan maganganun a yanzu suna dunkule yasa hannu a aljihu yana ciro kudin don ya bawa dattijon .
Ya ciro kudi masu dan yawa yana kokarin bashi ya dakatar dashi da fadin ko kusa kai ai jikanane yanzu dole in maka nayiwa banza balle irin ku kadai kula da kanka ka hada kuma da hakkuri da duniya .
Allah ya aauke ka lafiya ka gaida min da ita salamatun kace ta dai dage da yawan addua kamar yadda ta saba da hakan duk da hakan sai da Ahmed din ya kasa wucewa bai basa komai ba sai ya zaro leda daga aljihun shi yace ta malam ga wanan gorone ka karba ya kalli ledan kafin ya mika hannu ya karbi ledan a hannunshi.
Sukai sallama ya mike ya fita bai tsaya ko ina ba sai inda zai samu mota nan ya juyo zuwa gusau zuciyar shi cike da tunanen sarkakiyar maganan tsohon da yai mai.
ZAINAB IDRIS MAKAWA🌱TUMFAFIYA UWAR KWANKWANMAI ,,,,,,,,,,
🌱TUMFAFIYA BAKI FITA A WURIN BANZA ,,,,,,,
🌱TUMFAFIYA SIRIN KI SAI ALLAH ,,,,,,,,,,
ZAINAB IDRIS MAKAWA
7️⃣0️⃣
ONLINE PAID NOVEL YARUWA KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMA DARI BIYAR NE DON KIRA 08036959257 KO BIYA KI AIKA 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KATIN WAYA MUN GODE UBANGIJI YA BAKI IKON BIYA AMIN,,,,,,,
Zakice bashi yai tafiya ba a ranan don ya dawo a cikin lokaci yaso ya samu ummah a asibitin amma sai akace masa bata leko ba tun safe haka yasa yaja bakinsa yai shiru da zancen.
Saidai yana kokarin ganin ya samu dama ya shaka min maganin kamar yadda tsohon ya fada mai yayi Allah cikin ikon shi sai ga Dije na fadin Aisha ta kaita gida tayi wanka su dawo tunda Ahmed din nan wajen hannatu kuma taje gidan su tun safe bata dawo ba.
Haka ya tun kareni gadan gadan bai tsaya shakar komai da nufin ya shaka min caraf yaga na bude idanuna dake rufe lokacin don haka zan rufe ido zakice ko barci nakeyi alhalin idona biyu a lokacin.
Wani karfi da bai taba zaton ina dashiba yaji nayi mai a lokacin shima hakan yayita maza baiyi wasa ba ya shaka min maganin tare da murza min sauran a fuskana ya shafe .
A take nake wani gumji a daidai lokacin hannatu ta shigo dakon hannu ya daga mata alaman kada tayi magana ina karewa sai barci mai nauyi dayazo min ban kara sanin inda kaina yake ba kuma.
Wai master yanzu fa gwaggona ta gama fadin anya ba mutanen boye bane suke damun zahra nake cewa a,a likitoci sunce thaphod ne da maleria.
Cikin damuwa yake fadin dama kinsan tana dasu ai basu dai faye tashi mata bane ko wani lokaci don farkon haduwana da itama a cikin irin halin nan na sameta a school cilin mota kowa ya watse ya barta saida nazo na taimaka mata.
Wallahi ban taba sanin hakan ba batama taba fada min tana da wanan laluran ba gaskiya ai kinsa bata da yawan surutu haka balle ki sani.
Ta dan kura min ido na dan lokaci kafin tace iyayyenta sun san da wanan laluran nata kuwa master yace sun sani mana ai don mahaifiyar na tsayene ma abin yai sauki a lokacin.
Yanzunma ina ganin wani abune ya faru har hakan ya tashi mata da badon haka ba ai basa tashi irin hakan har su wahalsheta irin haka tun wancan lokacin don har ina dauka sun bartane kwata kwata ashe har yanzun suna biye da ita din.
Idon shi ya sauke a kaina na fada sosai na rame hancina yafito sosai a lokacin nayi dan wani haske ga ganin shi ajiyan zuciya ya sauke shi kadai yasan abinda yake ji game da hakan.
Makwabata ta shiga diban wutan murhu nan suka tsaya suna tambayanta ya jikin nawa ta fara fadin umm,humm bari kudai yayan masu kudi suna wada suka so.
In banda lalaci shigan ciki aka kwantawa asibiti harda su karin ruwa da kwanciya sai wahal da mutane akeyi suna sintirin asibiti shi dan rawan kan tunda ya dawo sau daya na sakashi a ido ban kara gani nai ba har yau dinga.
Keko dai da wagga maganan wa yanda ma ba diyan kowa ba sun kwantawa ciko balle ita da ad diyan mai kudin gari yanzu ai haka yayina ga matan yanzu abu kadan atai asibiti a kwanta mazan suyi ta wahala koda miji baida shi.
Ashe kegane dauri yaron ga kahin ya auro ta babu dai ababu gidan nan amma tunda ya auro diyaga yanzu daka mai magana zaicewa shi baida shi a,a ankason yayi da rayuwatai .
Amma ita yar mulkin ko cewa tayi tana son kan dan sarki ko wuta zai shiga ya samo yanzun na kana ganin an kawo matashiya muko ko o,oho,ho,ho .
Ai kesan dama haka zai faru tunda ta hito daga gidan masu kudi sai ta dan tabe bakinta kafin ta juya baya ta dawo da fuskanta garesu tana fadin inda ba masu kudin ko wa take ko a gidan nasu suda banza duk daya a gidan ai .
Keko in bashi ba ana daukatan haka zikau a bashi nidai nasan wagga basuwa da ankaimai bata banzata ba da wata a kasa maji magani in gaskiya tta bayana.
Keko bar wanga batanci ga danki mana wata yar dattijuwan gidan ta fada daga gefensu cikin takai ke kanki ke nuna ko dan naki ba cikakena bake nan.
A,a wallah nikan dana ai garau yake mi att matsalanai ita daita dole akwai matsalan da yasa suka bashi ita don har gobe bincike nakai ko zanji wata matsala da aggareta.
Ke arr da wanga halin banzan naki abinga da nikaji ashe shin da gaskiyana baki kaunar diyanga da alheri ke kan Rashida anyi mutumiyar banza wuringa.
Shin yanzu mi nice na ganin laihins ga wanga maganan wai gaskiya naka hwadi kuma shina laihi ni kunga ida niyi tana fadin hakan tasa kai ta fice daga gidan da garwashin wuta a hannunta
Nan suka sameta suka zageta