Showing 186001 words to 189000 words out of 304363 words
princess ina magana kina bani amsa wani iri ba yadda kika sababa sai naki yin magana a lokacin.
Da sauri yace min ko wani abu ya farune kuma nace gaskiya nagaji da irin yadda inna ke min don kawai na hadawa Dije tea shine zai zama wani magana har tace aurena dakai yasa yanzun baka kulawa kana kwasan kudin ka kana kashewa a kaina ni har, , , , ,
Cool down my dear ba sai kin kai karshe ba don nasan kina hakkuri da zancen inna dama yau daine tayi maki fiye da kullun don Allah zahra ki kara hakkuri da inna tunda kinsan halinta.
Naji nace amma kawai don Asmau ta fada mata magana sai ta dinga zuba min arashi kamar sa,anta nake mahaifiyarta fa na taimakawa.
Kin gani ba nan zaki gane abinda nake fadi da farko kina fada kina ganin laifina nace kai dantane ai dole ka bita ko yaya halinta yake .
Wai Asmau bari yar kam uban nan da nadawo zasu koma gidan dagin ubansu su zauna na gaji nagaji wallahi da yan iskan yaran nan dako sharan gida basu iyawa saici da tsegumi.
Ka hada takardun ne na katseshi da fadi naji yaja tsuki yace barin loda kudi na sake kiranki ya kashe wayan a cikin takaici.
Nima na jefa wayan gefena inna son zuwa in duba tsohuwar da jiki saidai kuma takaici ya hana inje part din nasu don nasan inna na nan sun baza tabarma da diyanta a lokacin.
Sallama naji daga kofa na amsa Aishan shice ta shigo wurina a cikin rashin sakin fuska na amsa mata ta shigo tana fadin ashe baki barci ba na dauka harkin kwanta ai.
Nace ban kwanta ba Aisha ta zauna tayi shiru na dan lokaci kafin tace Anty Zahra banji dadin abinda ya faru tsakanin ku da inna ba dazun.
Duk Asmau ce ta kawo zancen nan duk dai bata dauka itama zancen zaiyi tsawo haka ba don ta shigone tanawa Dije sheri shine inna ta karbe maganan ta juyeshi ya zama haka.
Don Allah kiyi hakkuri kin saba da halin inna ai yanzu kibar tankawa don Allah kada ajiku da ita nasan idan yaya yaji hakan ba zai masa dadi ba.
Kinga ni yanzu na gane tana kallo ko yanzu na shigo nan din don ba zata rabamu ba muna gida daya kina muna alherin da zakiwa kannen ki don haka kika daukemu muma.
Asmauce ta shigo itama tana fadin nikan na wuto wai innace ke kwala min kira na dawo naki matan yaya kallo zaki kuna muna a waya muyi dama don yaya na nan ne bamu zuwa.
Mamakin halinsu naji nikan na jawo wayan na kuna masu wani film din tan Philippines da muke kallon season film tana fadin mun wuce nan ai yana kiran wayan.
Hakan bai hanasu yin surutunsu ba yace keda suwaye a dakin nace su Aisha ne ya kunduma zaki dame sukazoyi yan kaza uba ?
Kasa kudin ke nan na fada na kawar da zancen a lokacin yace eh yanzu na sayi a banki kin saka loudspeaker ne ko kuwa nace ban saka ba yace tambaya dama zanyi yaya akayi guy din nan zai bamu aiki.
Kai tsaye nace idan zancen bai kwanta maka bane a barshi don Allah ni j nagama zan nemeshi yabani tunda niya sani yace haka zakice min nace naga kana son fassaramin zancen ne da wani manufa banji yayi magana ba ya kashe wayan.
Na kunna masu na mike ina fadin zan dubo Dije in gaida ita da jiki suka amsa da sai kin dawo nan na fita na barsu zaune suna kallo can na iske inna tayi bakin mata masu zuwa sayen kayanta.
Na shiga wurin Dije muka gaisa na samu tana cin abinci lokacin yasa na dan jata da hira tanaci muna taba hira tana ban hakkuri kan abindaya faru nace ai ya wuce yanzun ma su Aisha na wurina na barsu suna kallo.
Ban jima ba na mike zuwa part dina na kwanta ina fadin in sun gama su tayar dani in rufe kofa Asmauce tayi saurin fadin ni a nan zan kwana barin tashi in rufe gida dayani.
Inna nada baki a cikin gida na fada tace zan fada mata ta rufe don yaya yaja muna kunne sosai kan rufe gida wai barayi ke yawo a unguwa.
Ta mike zuwa cikin gida bata dade ba ta dawo tana guna guni ta fadin wai inna kada mu kwana nan yau don dama idan baya gari a yan kwanakin nan da muka fara shiri dasu sukan kwana a part dina saboda kallo.
Ai basu koma a nan din suka kwana dukkan mu falo muka kwana tare dasu nayi sammakon tashi zuwa school inda daga can gidan mu zan tafi in duba maijego sai dana shirya na shiga sallaman su nake fada masu sai da yamma zan dawo zan tafi gidan mu daga can in duba mai haihuwa .
Asmau tace dani aida daga nan zaki tafi da mun tafi tare ina son zuwa gidan ku wallahi mutum baj fitowa ba a bashi wani abin karuwa ba gashi kuma kaci ka koshi farat inna tace to yar mayunwata fada mata gidab ku gidan tallakawane.
Ji inna meye yanzu matar yaya bata sani ba game damu saidai idan mutanen gidansune basu sani basu ni dai na fita na barsu da shirmen su.
Ina mamakin yadda Ahmed ya fito cikin cikin wanan matar haka halinshi ya fito daban shi kodan bai tashi tare da ita bane oho don dana biye mata ko da safe da mun kwasa tana fada da yaranra kan sun kwana part dina tana fadin wai ana dauke masu hankali da kallon banza da zai lalata masu tarbiya
Kai haba inna wani irin bata tarbiya mutanen dako yarensu bamuji kuma ba irin tufafin mu suke sakawa ba don Allah ya horewa yaran nan ta baki basu da kwabo ko kadan.
Shiru yayi yana sauraren abokin nasa har yakai karshen magana kafin ya dago ya kalli sauran dake saurarensu sukace kwarai kuwa don ko gaskiya Alh jauro ya fada.
Duk yadda mukaso muzo kusa dakai a lokacin matarka dama kai kanka baka yarda da hakan saidai aimu bamu kika ba don ko yaushe muna tare dakai don munsan hakan bayin kanka bane.
Duk abinda kake yi alama ya nuna muna ba a cikin hankalinka kake muna mun so mu share zancen ka mu zauna a inda Allah ya ajemu saidai a yadda muka taso dakai mun kasa hakan gareka.
Badon komai ba sai sanin cewan da mukayi cutar dakai zasuyi a karshe don badon Allah suke tare dakai ba kuma gashi duk yan uwanka sun kawo ido suma sun saka maka duk da sunsan gaskiyan zancen suma sunyi fushi dakai a yanzu subar zancen ka.
Idanunshine ya ciko da hawaye lokaci guda don jin zantuntukan da abokan nasa suke fada a yanzu yaushine mace ta mayar hakan a cikin yan uwasa da abokanan sa lokaci guda.
Yanzun dai mu godewa Allah dayasa ka gane hakan da wuri tun lokaci bai kure maka ba don da ka mutu a cikin halin gaskiya akwai matsala babba.
Aishi mutum mai alheri Allah baya barinsa haka dama don ko sun hanaka komai basu hanaka alheri ga mutanen makwabtanka ba.
Wanan ma ya isa ya taimaka maka ka fito daga kanginsu don ba haka sukaso gani a gareka ba sunso suga sun rabaka da kowa a garin nan.
Yanzun dai ba wanan ba yaya zancen da muka fara dakai a waya na yaron nan don ya kamata ace zuwa yanzu kasan matsayin da yaron nan yake ciki.
Fuskanshi ya shafo don maganganun nasu sunyi masa yawa a kai duk da dama yasan dasu abaya amma yanzun da yake kara jin hakan a bakunan su sai yake jin zancen kamar sabo a gareshi.
Sun dauki lokaci a tare dashi har zuwa magariba kafin zuwa sallah bayan sun fito kowa ya nufi wurin iyalinshi akan da safe zasu fito su rakashi zuwa wajen yan uwan nasa na haihu.
A cikin gida kuma itama hjy mariya mamakin abubuwan dake faruwa sai take ganin abin yau kamar a falki yake zuwa mata ba gaskiya bane yau mijin nasune yazo gareta shi kadai ba tare da matarshi wani lokacin da yaransu da basu da kwabo ko kadan.
Zasuzo su mayar da ita kamar yar aiki agidan sai sun tafi take samun sa,ida a rayuwanta don hakanema bata kaunan zuwan nasu saboda cin fuskan da ake mata din idan sunzo.
Ya shigo gidan bata saba idan yazo ta sameshi ba kamar yadda ko wace mace ke samun freedom da mijinta idan yazo sai gashi ta kasa zuwa gareshi.
Sai shi din ne daya fahinci hakan ya taso zuwa gareta sai taga abin wani irin bambarakwai a gareta don haka lokaci guda ta rude da ganin shi kai duniya.
ZAINAB IDRIS MAKAWA🌱TUMFAFIYA UWAR KWANKWANMAI ,,,,,,,,,,
🌱TUMFAFIYA BAKI FITA A WURIN BANZA ,,,,,,,
🌱TUMFAFIYA SIRIN KI SAI ALLAH ,,,,,,,,,,
ZAINAB IDRIS MAKAWA
6️⃣5️⃣
ONLINE PAID NOVEL YARUWA KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMA DARI BIYAR NE DON KIRA 08036959257 KO BIYA KI AIKA 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KATIN WAYA MUN GODE UBANGIJI YA BAKI IKON BIYA AMIN,,,,,,,
Na gaji sosai dana dawo don haka na kwanta da wuri a ranan sai washegari dana tashi nayi dan gyara kafin in in fita na kwashi takardun nasa don ranan nake son in turo wa Brother Bisi dasu kada yaji shiru.
Na fito da shirina zuwa cikin gida don in gaidasu kuma in sallamesu na samu Dije a waje tana cin kayan bukin a wanan lokacin ya kirani a waya na dauko na daga ina fadin bari mu gaisa da Dije da tana hangoni tace yau kina shiga makaranta ke nan nace eh kwana biyu banje ba kada a wuceni da karatu sai na manta wayan a kunne take.
Nayi mata inna kwana kana na nufi wurin inna da itama tana zaune daga kofansu tana cin nata kayan bukin nayi mata inna kwana cikin ladabi.
Ta amsa min yadda ta saba ba yabo ba fallasa na juya muna gaisawa dasu Aisha daga cab Asmau ta leko ta daki tana fadin wai matar yaya wanan dayan mai cikin din da muka gani itama yar uwankuce ?
Nace eh itace akai muna aure rana guda mu uku kai amma duk kin fisu kyau nisa ba kusa saidai su gwada maki jin dadi yanzu kawai don suna da sallo sosai wallahi.
Kai ji yar nan da wani zancen banza su ba diyan masu kudi bane kuma yanzu suna aure me kudi in akwai kudi ina ruwan mutum da muninka ?
Wani kallon takaici na watsowa inna din lokaci guda nace amma kada ki manta asalinmu daya duk abinda suke takama dashi dashi nake takama nima ai kudin mazansu wasuke ba ?
Don nawa mijin baida kudi a cikon mu bashi ke nufin na koma baya ba Allah bai bashi ba yanzu in Allah ya nufa zaiyi nan gaba sai muyi harma kila mufisu arzikin da suke takaman dashi a yanzu.
Wanan shine maganan gaskiya Dije ta fada daga kofanta ni kuma ina fadin haka na juyo zan bar wurin naji inna tace yanzu dawa kika wanga magana cikin mu ?
Kemana Dije ta bata amsa yara na maganan su mikaiki saka masu bakinki ciki don wanga maganan ma sam bada wagga diya kikayin shiba danki kika hwadawa magana shida hannunshi bai kai ba.
Sam na mace wayan yana kunne har lokacin saina dawo na fada a daidai lokacin da inna ke babatun fadin don na saka bakina ba gaskiya na fada ba ai banki mijin nata yai arzikin ba nima.
Dije duk ake magana sai kiyi kokarin juyawa mutum maganan shi yanzu meya kawo zancen dan dije cikin maganan nan ?
Nidai na fita ina jan tsoki ashe yanata magana a wayan banji shiba karshema dana fita na jefa wayan a cikin jakata jin nafice daga gidan yasa ya kashe wayan tasa a lokacin.
Na isa makaranta daidai malamin zai shiga don haka kusan a tare muka shiga dashi lokacin bayan mun fitone muke hiran da hannatu dataga yadda nake rai bace a ranan.
Sam har ya kwana biyu ya koma basu yarda sunyi zancen Ahmed dashi ba kamar yadda malamin ya fada masu iya lokacin da zasu kai kafin su tunkareshi .
Hakan yasa suke kyale har ya tafi baisan komai ba gashi har Ahmed din ya kira Alh jauro kamar yadda ya saba kiransu lokaci lokaci daya bayan daya yana gaisawa dasu a matsayinsu na iyayyensa da suka tsaya mai a yanzu din cikin lamarinshi.
Suma hakan sukan kirashi suji lafiyab mu don hakanema nake dauka da mahaifinasa yake waya wani lokaci sai daga baya na gane ba haka bane ashe.
Koda ya koma komai bai canza ba tsakanin shi da hjy Yabi har yanzu zaman nasu suna dai yinshi a takurene da juna don sam yanzu baya shiga tsabgansu.
Ita dai ke kokarin taga sun gyara koshi don tacinwa manufartane akanshi yanzun din kuma yasan da hakan don akwai ranan data fita ya kira mai aikinsu ya tsureta akan in bata fada mai gaskiya ba zai koreta a gidan.
Jin hakan yasa fa kwashe komai data sani ta fada mai game da hjy saida hankalinshi ya tashi sosai bayan ya gama jine ya sallameta da jan kunnenta kada ta yarda ta nuna mata yasan da hakan don hakan zai jawo ta iya rasa aikinta idan ta shine tunda ta taimaka ta fada mashi ba wani mahaluki da zaisan wanan zancen.
Tayi maigodiya shima yace ya gode amma duk lokacin da taga wani abin cutarwa a gareshi don Allah ta taimaka ta fadamai tayi alkawarin hakan.
Haka yasa ya kara jan jikinshi da ita sosai dan dama dama diyanshi yana mu,amula dasu yadda ya kamata ko wani mahaifi yayi da dansa.
Ya dawo da kamar sati uku tana dawowa unguwa ta hango yan aikina aikin gyaran dayan part din dake rufe a gidan da mamaki ta fito daga dakin tana tana binsu da kallo har zuwa wurin su.
Basu dakatar da aikin da sukeyi ba sukaci gaba dayansu take tambaya yace maigidanne ya kirasu suyi aikin yana fadin haka yaci gaba da aikinshi ya barta nan tsaye tana ci gaba da kallonsu.
Ciki mamaki da samun daurewan kai ta taka zuwa part dinsu yarta ta sama a dakinta ta shiga a rude yarinyar na kwance tana waya dakin duk ya turare da hayakin shi-sha a lokacin.
Shigowar uwar ta dan dago tana fadin mummy lafiya kuwa na ganki a haka kamar a rude salima wanan uban hayakin da kika turara a daki haka anya kuwa zai baki lafiya karshe ?.
Mum wanan ba komai bane fa kin sani yarta fada ta mere baki uwar tace daddyn ku ya fada maki za ai gyaran wancan part dinne kafin ya fita ganin yakan dan zauna da yaran yayi fira wani lokaci yasata tambaya haka.
Haba mum bai fada maki ba ni zan sani kawai dai kila yaga kayan cikin sun dadene yasa a gyara diyar ta fada cikin ko in kula sanin suna yawan gyaran gida akai akai.
Salima ki dawo cikin hankalinki ki natsu ki fahinceni maganan abinda ke shirin faruwa a gidan nan nake maki kina karanto min hauka ke kuma.
To ki sani idan ba aure zai kara a yanzu ba akwai wani plain da yake shirin yi dolene akwai abinda yake shiryawa bada sanina ba a yanzu ya zama dole in sani meye manufanshi da hakan idan ya shigo.
Amma mummy daddy baya gari ya fada min da safe nan kafin ya fita zai tafi South Africa shida Alh badaru zasu wani business a can nima naji hakan ne lokacin da Alh Badarun ya bugo mai waya suna magana.
Mamakinta kara ya fito a fuskanta har tana watsawa diyar wani irin kallo kamar itace tayi laifin a lokacin yarinyar ta gand meke zuciyar uwan da sauri tace.
No mum nimafa da suka gama wayanne ya fada min cewa Alh badarune zasu tafi South Africa tare da shine a yau din.
Amma salima ya kamata tun lokacin ki sanar dani ba yanzu ba don fadin baida rana tace sorry mum na dauka aikin sanine ?
Bata iya yin magana ba lokacin sai dagawa da tayi ta dan kure yar nata da idanu na dan lokaci kafin ta juya ta bar dakin zuwa nata dakin.
Gado ta fada hankali tashe a hankali ta mayar da idanunta rufe ta rasa ta ina zata fara tunane ma don yadda take daukan zancen yafida nan a gidan nan yanzu.
Tana nan kwance tunanen ta ya tsaya akan danta yasir lokaci guda don shine kadai zai iya takawa mahaifin nasu burki a yanzu kafin ya idda nufinshi dake cikin zuciyarshi akansu.
Don ita salima da ita da babu a yanzu duk dayane kamar ba mace ba bata ko gwada kishin abinda mahaifin nasu ke mata a yanzu.
Bayan tunanenta ya tsaya a yasir din ta samu zuciyanta ya dan rage zafi lokacin ne ta jawo waya don labartawa yarta