Showing 243001 words to 246000 words out of 304363 words
sauri yana fadin daga wancan mutanen da suka kaimu wajene fa kwanaki suke kiran layina yanzu Zahra.
Zanyi magana ya dauka yana gyara murya suka fara gaisawa da mai kiran nasa wani mr Atom ya gabatar da kansa gareshi tare da fadin har sunyi given up cewan ba zasu sameshi ba ai.
Don suna kiran layinsa kusan sati ke nan basu sameshi ba congratulation to him once more again don ya cinye interview dinsa da sukayi a US yanzu ya zama one of there members zaiyi reporting a daya ga watan biyu na sabon shekara saura two months ke nan yanzu yayi mai sallama.
Zubur naga ya mike tsaye yayi kamar zai shiga daki sai kuma ya dawo ya kalli gabas ya daga hannu yanawa Allah godiya tare da jero kyawawan sunan Allah yana jera masa kirari dasu lokaci guda.
Kafin ya duka yai sujada ya dade a duke yana godiya ga ubangiji Allah kana ya zauna ya sake daga hannayensa sama ya godewa Allah.
Hawayene da bansan kona meye ba a lokacin suke zubo min saiji nayi shima ya rikeni yana fadin Alhamdullahi zahra Allah ya karba muna adduan mu sun daukeni sunce sun daukeni zahra ya rugumoni yana fadin hakan kamar wani zaucece dashi.
Master naji meya fada mungodewa Allah Allah yasa hakan alherine a garemu baki daya yace insha Allahu alherin muce yazo muna kurkusa zahra.
Naji dadin jin hakan Allah nagodema da ka bani wanan aikin ubangijin ka kara tabbatar min da hakan a rayuwana .
Zahra na kara yadda da kaddara a yanzu tana iya cin maka a lokacin da baka zaci hakan ba gareka idan ba don keba zahra a ina zan taba samun wanan aikin a rayuwana haka ?
A,a kobani zaka samu tunda rubutacene a gareka dama master bari nayo alwala na dan fita injira sallah waje daga can zanyi sadaka na kara godewa Allah.
Ya mike zuwa ciki ya dan dade ya fito ya sameni kitchen ina hada muna girki daga bayana naji muryanshi yana fadin ba dai abinci zaki dora yanzu ba kuma ?
Cuscuses zan dora muna ai yanzu zan kare kafin a shiga sallah don naga Dije tana sonsa sosai yace gaskiya badon Dije din ba da kike son taci sai ince ki barshi in sayo muna wani abu idan na fita.
Bari dai kawai in hada muna ina da alaihon dana sayo a hanya sai a hada ko don dije din to ki hada kadan dai don akwai dan canji a aljihuna zan dan sayo muna wani abu muci mu.
Saidai ka sayo din ke nab yau cikin kudi kake jin kanka tun baka fara rikesu ba yace dolene aiyau mu dan walwala don ranan farin cikine a garemu ya kamata in nuna hakan ai.
Bayan fitan shine daga part din ina gab da karasa girkin ummah ta kirani take fada min Abban mu yazo ba lafiya kuma don haka in samu lokaci in lekoshi.
Nan na rude bata tsaya yimin bayanin komai ba naji ta kashe wayan nata a gagauce na karasa girkin nakaiwasu Dije dasu inna take tambayana ina shi Amadin yake ?
Nace ya fita sallah yau ai jikin nasa yayi sauki sosai daga can inda inna take take fadin ai gara dai din ya mike yafi ko fita yayi ya nemo muna abinci ai.
Tunda shi bajin maganan na gaba gareshi ai mutum ya zauna yace shi baida aiki sai bakin rai da kowa ga shegen tauri kamar mazan farko.
Badai sai ya fita din zai samo kuci ba koda yake kwance din yana ciwon kuke ciyar da kanku din Dije ke bata amsa lokacin naji inna din na fadin umma ko baki son a fadi gaskiya sai an fada.
Yaron nan har fa ciwon jikinsa yakewa mutane taurin kai son yaga ana kula masa yaya ba za ai masa fada ba kuwa tunda shine mai fita ya nemo muna muci yayi kwamce gida yaki zuwa nemo lafiyanshi.
Ni abin haushi da takaici yake ban in anyi magana yace wai yasan abinda yakeyi yafison aita kira mai shege a gari har ana fakewa da bashi gaibu waida sunan taimako.
Abindake damun zuciyana a lokacin ya dameni na game da ciwon mahaifina da ummah ta sanar dani shine ya damu zuviyana a lokacin me zan tsayawa sauraren abinda na saba ji gun inna.
Don ita a yadda nake tune inna ta dauka cewa ni da mahaifiyatace muke juya mata da a yanzu har bai iya sakar mata kudi yadda take so a gareshi saidai ya sayo masu abinci ya dan manna mata dan dubu ko dubu biyu shike nan.
Ta manta cewa hannun ne baikai ba a lokacin da ace zatayi tunane data gane hakan ga dan nata idan shi mai haline dayafi hakan gareta amma sai kawai nake tsuntar labari wurin Dije cewa ai har shige shige wurin malumma takeyi kan dan nata.
Banyi mamakin jin hakan ba don sanin ko waye inna a lokacin don akwai sauran kurciya da bin kawayen bazan da sunan zawarci waisu sun waye suke gani ga kuma jahilci a tare da ita don hakane abubuwan sukai mata yawa.
Sallah nayi na idar na jawo waya ina sake kiran ummah don hankalina dake tashe a lokacin wayan yanata ringing bata daga ba sai kamar zai katse naji ta daga.
Muka gaisa nake kara tambayan ta karfin jikin Abba din tace da sauki nake fada mata master ne ya fita bai dawo gida ba damun shigo lokacin tace aiku bari da safe kuzo yaji sauki yanzuma yasha magani ya kwanta ai.
Sai naji muryan Abba din na fadin maahmah ce kika kira ki barsu kada ki tayar mata da hankali aini naji sauki ga Abban naku to ku gaisa ta fada tana miko masa wayan.
Ya karba yace maahmah kuna lafiya ko kada kice zaki taso da daren nan naji sauki zuwa safe zan shiga asibiti idan Allah ya kaimu lafiya ai.
Idanuna na lumshe jin yadda Abban ke magana a lokacin cikin dauriya gashi kuma yana magana dani a cikin lumana ba yadda ya saba min ba yana hattarata kamar baison ganina.
Saina dauka hakan kamar ya riga daya tsameni ne a cikin diyansa baison wani hurda ta da da mahaifima a tsakanin mu shiyasa nake baya baya da lamarinsa ma.
Na kashe wayan ina masa fatan samun lafiya tare da lumshe idanuna ina tuno da baya yadda muke da Abba din yana ji dani sosai don sunan mahaifiyar shi da aka saka min lokacin.
Haka master ya shigo da ledojin shi a hannu ya sameni tun shigowan shi ya fahinci yanayina ya aje ledan yana fadin me kuma ya faru naganki hakan yanzu kuma ko innace tayi halin nata kuma bayan fitana.
Inna kan ai ba zata fasa ba don na fahinci namu baizo daya bane kawai da ita don haka take nuna min rashin kauna bama tare data san tanayi ba.
Wayace ummah ta bugo min wai Abba nanan yazo ba lafiya sosai shine kaganni hakan amma munyu waya dashi yace da sauki zuwa safe yake son sake zuwa asibiti adubashi.
Subbahanallahi da sauki ko ya tambaya cikin nuna kulawanshi nace yace da sauki amma muryanshi ne ba dadi da alama yana jin jiki sosai dai.
To ko mujene nace yace mu bari saida safe mu shigo yanzu dare yayi kada mu fito bawan Allah sai cewa yayi kodai mujene mu dubashi tunda kince kinji yana jin jikin .
Mu dai bari saida safen tunda yace mu bari din kuma kaima ai ba lafiyan ne dakai ba zaune a lokacin ya kai zaune yana fadin nina samu lafiya ai shima Allah ya bashi lafiya ya mike.
Mikewa nayi na amsa abinci na dauko a cikin kula na kawo mashi gaban shi tare da plates da spoons biyu na aje na koma dauko ruwa naji kara bude ledojin da yakeyi.
Kofa muka hadu yana fadin zankaiwa su Dije na dawo na amsa da to nashiga na aje na shige bandaki don in watsa ruwa a jikina nasan dana gama kwanciya zanyi tunda ba wutan nepa yanzu kuma ya daina tayar min da injin yadda yake min a farkon auren mu kuma ban masa magana don nasan halinda muke ciki.
Me muka samu Dije ta fada daya aje mata leda daya a gabanta yace saikin bude kinci ki tayani murna Dije ya juya zuwa wurin su inna da duk idonsu ke kan ledan daya shigo dasu din.
Ya mikawa Aisha ta karba tana godiya ya dawo wurin Dije yana fadin yanzun aka bugowa Zahra waya cewa mahaifinta baida lafiya wallahi.
Munso zuwa sai shi mahaifin nata yace mu bari harda safe muzo yanzun dare yayi kaida kai ciwo wayazo gaishe ka daga gidan nasu da har kake zumudin zuwa cikin daren nan dama ?
Inna data cika nama a bakinta take fadin hakan a tare suke fadin haba dai daya suke dashi shifa mahaifine dije ta kara da fadin keda kikai ciwo ai sau biyu mahaifiyarta na zuwa duban ki gidan nan ya kara da fasin kuma ga waya ga sako akai akai.
Dama komai na maikudi na gorine ai ban aika su zo ba dama dije tace toshi an aiko dole kuma yaje don albarkacin yarsu da yake zaune da ita kingako dole yaje.
Dije yi min murna zahra alherice gareni kina fadin hakan ban kara gaskantawa ba sai yau din nan wai kinsa aikin da dan uwan nan nata yake neman min a kasan waje ya fito sun daukeni aiki dasu kuwa.
Yanzu a can zan koma in zauna kasan turawa muyi aiki tare dasu kai kace Allah masha Allahu nayi farin cikin jin wanan labarin mai dadin ji a yau din nan Amadi kasan turawa bako nan gida najeriya ba ma ?
Wallahi inna ai nan gaba kadan dije sai makka zan kaiki insha Allahu dake da inna tunda ita zahra zuwan ta biyu gidan su kuma ta saba fita kasan wajen ita dama.
Lah inna yaya kace arziki ya zo ke nan wayaga hjy inna ai lokacin wani fadi zai tashi ke tafi can don Allah in gaskiyane aikin kwaraine su samo mashi aiko nan cikin najeriya mana.
Sallon a karasa jayeshi garemu ke nan yanzu yana nan ma tare damu yaya aka kwashe balle ya dauki matarshi sun fita aisai lokacin da muka ganshi kuma.
Haba inna na dauka godiya zakiyi da murna ba wanan irin maganan ba ai a bakinki su jayeni zuwa ina su suka haifeni halan da zasu jayeni gareku.
Kai nifa indai ta wanan yarinyar ne aiki zaizo ma ko wani abu ina bakin cikin hakan don gori yana nan wata rana yana jiran ka da zaran kace zaka kara aure nan gaba.
Aure kuma inna ana zaune kalau ita wanan ta gidan laifin me tayi min da har zanje karin wani aurecen yanzu kuma a dai muna addua da fatan samun zuria masu albarka tare da ita.
Kaji shasha wanan din da aka cunama ita halan nemanta kayi suka baka ita data kwaraice aba zasuko kalli tsayinka ba balle a baka ita din .
In kanawa kanka karatun ta natsu kaiwa kanka fada kasan abinda kake ciki har kana murna wai sun baka aiki don rashin sanin ciwon kai.
Kallon dije yayi irin kallon dake nuna tambaya ga mutum na kan inna daya kuwa take irin wanan maganan haka amma a fili baiyi magana ba mikewa yayi ya fice daga part din kawai.
Ya zauna yayi Shiru yana tunane yaya mahaifiyanshi zata din ga yi mai hakane wai kuma itace ta haife shi ya samu alheri haka ta nuna bakin cikinta a fili.
Sai gani na fito daga dakin muna waya da ummah yaji ina fada mata zancen samun aikin da brother bisi yayi mashi hanya yau sun kira suna sheda mashi ya samu aiki a wajensu.
Masha Allah masha Allah kai wanan labarin da dadi yake Allah ubangiji yasa iyakar wahalan ke nan naku Allah ya kara daukaka rayuwan ku daku dana bayan ku ubangiji Allah yasa ya rike amana tare da taimakon musulmin Allah ina karbawa da Amin zanko kirashi in masa murna nace ai gashima zaune ya dawo yanzu.
Tace bashi wayan har lokacin tana nuna farancikinta ga hakan ya karba tayi mai fatan alheri da dacewa da rahaman ubangiji sukai sallama kodaya miko min wayan ta kashe ko hakan yasa na dan kalleshi naga baiko bude ba balle ya diba hakan yasa na kalloshi.
Hawayene naga yana zuba a idonshi da sauri nace kaiko master dai ko adduan ne bai maka ba maimakon ya ban amsa sai kara hawaye yakeyi innalillahi na ambata.
Wai Master lafiya kuka haka lokaci guda dukar da kai yayi yana girgizawa kafin can ya dago ya kalloni inda nake ina zaune na kura masa ido ina kallon shi yace a cikin murya mai rauni.
Ina bakin ciki da mamakine har bansan lokacin da kuka yazo min haka ba wai ace yau mutum ya samu aiki irin haka amma mahaifiyarshi ce farkon nuna bakin ciki ga hakan don wani dalili nata na daban da baida tushe just saboda kiyayya ko tsana ni ban sani ba zahra.
Wai inna kake nufi dama tayi wani maganane kuma game da aikin naka yanzu na tambayeshi ina kallonshi yace yanzu naje ina fada masu azatona zatafi kowa murna.
Amma inna sai cewa tayi don ku kara mallakenine a gidanku kuka samo min aiki badon komai ba aidake abin kwaraice da iyayyen ki basu daukeki sun bani ke ba .
For god sake na rssa me kikayiwa inna haka raina ya baci don haka a ranan na labarta mashi komai da inna ke mun ina hadewa a gidan nasu ban kuma fadawa kowa.
Tambayan farko da yai min shine kona sanarda ummah komai nace wallahi ban taba fada mata komai ba game da hakan amma aiko ban fada ba ummah mace ce zata gane hakan ko wurin maganata wata rana.
Ki duba zahra yadda ummah take min fatan alheri da sakawa abin albarka amma wai ace mahaifiyata ita batayi farin ciki da lamarin ba yaya kike ganin zanji a raina don Allah.
Watarana zata daina wanan wani abune can na daban amma nan gaba zata rage gaskiya mu daiyi hakkuri a gama dasu lafiya kowa da halinsa ake zama dashi dama.
Yayi shiru kamar yana saurarena kafin ya nisa yace shike nan Allah yasa ta gane gaskiyan amma nina san hakan yana da wuya gaskiya ke kuma na gode da rufin asirin da kike min har kike danne zuciyan ki game da ita daba haka ba ban san ya abin zai kasance ba garemu gaskiya.
Da kyar yaci abincin muka kwanta ranan baiko shiga yiwa dije saida safe ba yadda ya saba mata idan yana gari haka ya kwana yana tunanen halin uwar nasa dole dai a karshe ya hakkura barci ya daukeshi.
Washe gari ko da fushi inna ta tashi ina sauri don banda niyar zuwa school ina son zuwa na diba jikin Abbane agidan mu ranan naji wayana yana ringing na dauka .
Ummah ce muka gaisa daga muryanta na gane babu lafiya take fada min cewa gasu asibiti tun da asuba jikin Abban ya kiya dole sukazo asibiti dashi kuma kusan kowa na wajen ma.
Jin hakan yasa na gagauta girkin na gama na zuba masu naje dashi don kazan da master ya sayo muna bacin rai ya hanna kowan mu cin kazan da dare don haka na juye amiyan gaba daya nagyara.
Karfe goma da rabi na isa asibitin nida master saman yar mashin dinshi tun daga nisa nake hango yan family din mu suna sintiri a haraban nan hankalina ya kara tashi shi ya dauko kayan abincin ya biyo bayana dashi.
Fuskokinsu babu dadi na karasa ina masu sallama muka gaisa sama sama yan gulma kuma duk da halinda ake ciki hakan bai hanasu muna kallon kwakwan ba a lokacin.
Kofan dakin da Abba din yake ciki yana rufe yan uwa duk suna waje nan na tsaya nake tambaya gwaggo uwa yar dakin mama ta kasa ta tsare duk wanda yazo a nan suke dakatar da mutum wai ba a shiga.
Muka karaso na gaidasu na tambaya yaya mai jikin suke fada min cewa da sauki na danyi shiru ina tunan shima master din ya gaidasu zuwa can dai naga shirun ba zai mun ba nace.
Wai likitane ya hana shiga sai matar baba Ado tace min muma tunda mukazo ba a bari mun shiga ba amma aisu hjy dasu Aisha suna nan cikin dakin dukkansu.
Gwaggo Uwa tayi saurin fadin hjy maimuna tace duk wanda yazo ko waye kada in bari ya shiga barci Alh keyi jin hakan na juyo na kalli master ina fadin mu shiga master.
Yace ba an hana kowa shiga ba ban tsaya sauraren shi ba na kama kofan na murda ta bude duk suka bini da idanu lokaci guda.
Suma na cikin dakin suka kallo mu nayi sallama nashigo ina gaidasu suka amsa harda hjy tsohuwa a wajen na