Showing 219001 words to 222000 words out of 304363 words
karbi layinsa din nace number ka kuma wa zanba layin ka kuwa sai zancen mahaifin nasa ya fado min take a zuciyana.
Nace da sauri oho na manta mahaifinka sunzo yau shiya karbi layin a hannuna da zasu tafi sai naji yace da sauri why zahra da zaki bashi layina ?
Mema yazo yi wurina a yanzu da ban bukatanshi ko kadan yanzun ne zaisan dani bayan na gama wullakanta a cikin mutane an gama goranta min da barina da yayi yayi tafiyanshi yanzu ya dawo yace shine ubana kuma.
Kai wani irin musulmine da baka yarda da kaddarankane master abin nan ya fada da bakinsa yayi laifi don Allah ku yafe mashi koda ace bashi bane mahaifinka ai ya kamata ka yafe masa din.
Ke zahra ya fada a cikkn wani irin murya da bansan yana da itaba yake fadin ki tsaya matsayinki kada ki kyatara layin da baki da hurumin shigansa daga yau sai yau akan wanan zancen.
Kayi hakkuri na iya furtawa a lokacin dkn nasan yakai iya hasala da zancen a yadda yake maganan dani lokacin.
Daga yau sai yau kada ki kara ba wani layina idan bani nace kiba mutum ba nace naji na kashe wayan na lafe a saman gadona ina tunane a lokacin.
Bai kara kitana ba tsawon kwana biyu da hakan ya faru tsakanin mu nima dama ba zan iya kirasa ba sai idan ya kira din Monday muka shiga school.
Nan nake fadawa hannatu zancen zuwan mahaifinshi din tare da yadda mukayi dashi ta waya kan numban dana bashi din take fadin shiko master ai hakkuri ya kamata yayi bawai ya rike mahaifin nasa ba haka.
Nima abinda nake fada mai ke nan ya hauni da fada har yau din nan bai kirani ba waishi yayi fushi ke nan nayi alkwari kuma ba zan sake masa magana kan zancen mahaifin nasa ba duk abinda zasuyi nan gaba kuwa.
Ya zakiyi wani abin aiba zaki san lokacin da zaki sa baki a ciki ba ke dai kawai kibi zancen a sannu tunda baison kina sa baki a cikin zancen.
Bayan mun tashine daga school din muka rabu a hanya da ita ni kuma na nufi gidan mu ummah tana ciki bata falo don haka na bita daki na sameta zaune a kasa tana waya.
Wuri na samu nima na zube a kasan ina ajiyan zuviya na fahinci da kawarta na Abuja aminiyar ta take waya a lokackn don maganganun da suke fada a wayan tasu.
Magana ce data shafi Abban mu da hjy karima kamat sunyi wani case da itane har da yan sanda a cikin zancen nasu lamo nayi ina sauraren su har yakai na fada wani tunane a lokacin.
Ta gama ta juyo tana fadin ke kuma daga ina haka ko mijin naki ya dawone a lokacin na dago ina kada ksi nace bai dawo ba ummah daga school nake na biyo nan in gaida ku.
Asha mahmah da ilimin ki zaki hakan bayan kinsan cewa wanan yana cikin babban abindake halaka mata a yanzu shine ke zaki hakan.
Mijjn ki baya gari ba waya kukayu dashi yace kizo ki dubamu ba amma sai ki dauko kafa kizo bada saninsa ba mahmah kada ki kara wanan halin da yawa mata ayanzu suna halaka kansu ta wanan hanyar bayan sun sani suke taka sanin.
Annabi yace dana miji yai tafiya ya dawo gida bai sami matarsa a gida ba gara akawo mashi gawanta ko nasa zaifi sauki haka kuma duk macen data tafi wani wurin bada umurtan mijinta ba duk rakon da takeyi mala,iku suna tsine mata.
Ina kikaga ina fita ba tare da sanin mahaifin ku ba maza ki mike ki koma dakinki idan ya dawo sai ki nemi izininsa kizo tafi min da inga zaki dauki hanyan halaka.
Ko kuma so kike ki koma irin yan uwanki da kullun suna gidan nan tun safe har dare ba a ma gane cewa aure sukeyi a yanzu ko hakan ke baki sha,awa kema ?
Na mike daga inda nake ina fadin ummah tunda yau nazo a bari naga su datti don Allah kan natafi dacewan kannena tace oh na kyaleki ki ci gaba da halaka ke nan ko ?
Haka na mike jkki a sabule ba don naso ba na fara shirin tafiya gida naji tace ko akwai wani abinda kikesone da sauri na dago kai nace a,a banson komai ummah kawai nazo nagaida kune dama.
Daga nan ki koma gida kada inji kinsake irin hakan idan ba haka ba ranki zai baci dani bandai yi magana ba na figi hijjab dina na saka a kaina na dago nace sai anja idan sun dawo a gaida min su.
Zasuji ranan asabar da safe zansa shehu ya kawo makisu wuni ina shike nan ko nace nagode ummah har nakai kofa lokacin ita kuma ta dago daga inda take zaune na juyo ina fadin .
Mahaifin shi yazo shekaran jiya shida yan uwanshi saidai basu samu Ahmed din a gida ba shine suka tafi amma idan ya dawo zai dawo yace.
Ikon Allah dama bai kasan ne ko kuwa ta tambayeni nace ummah bai fasan mahaifin nasa ba ko sau daya shima haka bai san dan nasa ba har yanzu.
Me ta fada da karfi cikin mamaki nace gashi kuma yazo bai gari amma yace zai dawo ikon Allah wanan abin da mamaki yake jeki dai wata rana idan kinzo makarasa hiran ki gaida tsohuwar nan don Allah.
Na kara mata sai anjima nasa kai mm a fice raina a bace don yadda ummah din tayi min taki in zauna a gida ni kuma naso indan zauna sai dare so kkmawa gidan amma taki hakan gareni.
Haka na juyo na dawo sukuku na bude part dina na shiga ba wanda yasan a lokacin na dawo gidan cup mm a fito waje da niyar na dauraye naji muryan inna da wata mace suna magana daidai kofan shigowa part din nawa suna fadin.
Ita wanan wani irin unguwane haka tun shigowa na gidan nan har yanzun bata dawo ba sai naji inna tace ke dai bari kawai inno ai ina ganjn abu gun yarinyar nan.
Da ace ita din wata me gatace ko a gidansu da bansan yadda zamu kwashe da ita ba ai saukin abjn ko a cikin gidan nasu uwarta borace bata da power.
Wai fa makaranta ta tafi tun safe har yanzun bata dawo ba kamar kantane aka fara boko abin dan yaune kawai da shirme ni ina namiji me zai kaini kwaso wanan na aje a gidana.
Abu haka da fari kamar zabaya babu dadin gani ko kadan wallahi tunda na farga irin diyan masu kudin nan ne marasa kunya na daure mata mara tam a gidan nan ko kadan bata ganin fuskana a gidan nan .
Daba haka ba sai yace mu muyi mata girki ita tana kwance haba dai keko Rashida ina hakan zai yuyu wallahi ko ina fada maki idan kinga abinda yaron nan yakeyi wallahi sai kin raina masa.
Keko dai rashida kika sani ko ubanta yana bashine gakufa yanzu baku cikin wahala duk garin nan abinda ake fada ke nan cewa mahaifinta yana taimaka maku yanzu.
Da sauri naji inna tace Allah ko zai saka muna ko kwandalan su bamu taba ci ba a gidan nan ke na fada maki diyar borace fa a gidansu din mena gaba yaci balle na baya.
Shine dai son a sani yake faman kashe kanshi a kanta ko kwanaki datayi ciwo bakiga rawan kan daya dinga yi ba sai kice yar gwal ya dauko muna.
Ni wallahi dana san yadda zanyi inga na rabashi da ita wallahi da nayi na aura mashi zabina kina da wata zabin ne akanshi matar ta tambayeta tace ga diyar kanwata nan tana mutuwan son shi kamar ta mutu.
Amma umma ta hana a tayar da zancen wai kada taji ko ta gani zamu batawa yaro tsarinshi a,a a kinfa san dama mutumin Dijene shi sosai .
Ai nasan maganin su jira nake ya gama wanan karatun daya saka kanshi sanan na bulo mashi da zancen don inga ko wace mace ce suke zagina da ita sai kawai na turo kofan part dina na fito.
Da sauri suka juyo suga ko waye sai suka ganni nace sannu ku ina wuni cikin iiiniya inna ke fadin dama kin dawone ashe nace eh na shiga sashen su na barsu a wurin ban dade da shiga ba naga inna ta shigo nasan dayan matar ta gudune lokacin.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
[6/19, 8:05 AM] Mmn Bibo: 🌱TUMFAFIYA UWAR KWANKWANMAI ,,,,,,,,,,
🌱TUMFAFIYA BAKI FITA A WURIN BANZA ,,,,,,,
🌱TUMFAFIYA SIRIN KI SAI ALLAH ,,,,,,,,,,
ZAINAB IDRIS MAKAWA
7️⃣6️⃣
ONLINE PAID NOVEL YARUWA KI BIYA KI KARANTA A CIKIN SALAMA DARI BIYAR NE DON KIRA 08036959257 KO BIYA KI AIKA 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KATIN WAYA MUN GODE UBANGIJI YA BAKI IKON BIYA AMIN,,,,,,,
Ranan na kwana da mamakin inna a raina na rasa menayiwa wanan matar tsana ya shiga tsakani da ita ban gano komai ba sai a karshe da nayi nazarin zancen da naji suna fadin a kaina.
Lokacin nagano cewa ba abinda nayi mata na rashin datacewa na farko dai jinin mu baizo daya bane dkn wani lokacin hakan yana faruwa kaji ka tsani mutum ba gaira ba dalili a banza.
Sai na biyu kuma ni din ba zabinta bace don na fahinci akwai zabinta data so dan nata ya aura sai Allah yayi dani.
Na uku hassada da bakin ciki yayiwa inna yawa akaina tana bakin ciki da gidan dana fito har yakai tana kiran uwana da mugun suna wai itace bora a gidan mu.
Wanan kalman na inna da kawarta da suka kira mahaifiyata dashi ya matukan tsaya min a zuciyana gaba daya girmanta ya zube min a idona daga wanan ranan.
Haka na kwana da zancen na tashi dashi da safe da wuri na shirya zuwa school kodana fita kamar in wuce bayan na rufo part dina amma wata zuciya tace min me Dije tayi maki ita ?
Da inna na fara cin karo a bakin murhunsu tana hura wutan abinda zasu karya dashi na safe Aisha na tsaye tana kallon madubi ta fara shirin fita school ke nan a lokacin itama.
Ina kwana kawai nace da ita cikin daure fuskana ba tare dana tsaya yadda na saba ina mata ladabin gaisuwa ranan sai bata samu hakan ba gareni don na wuce dakin dijene kai tsaye abina.
Nan ta dago ta bini da kallon mamaki Aisha ma dake tsaye kallon tabini dashi kafin taci gaba da abinda takeyi cikin rashin damuwa don tasan ruwa baya tsami banza ai.
Haka kuma na fito ban kalli kowa ba balle in kira suna cewa kawai nayi natafi sai na dawo duk suka bini da kallo don ban jira amsawan kowa ba a cikinsu.
Haka na fita ta bini da kallo sai a lokacin ta fahinci cewa naji komai da suka fada a kaina ke nan tunda na fara nuna hakan a fili abinka da mara mutunci sai cewa tayi aikin banza don an fadi gaskiya kike wani fisge fisge ga iska.
Inna anyi wani abin ne halan Aishan ta tambayi uwar cikin sonji daga gareta sai uwar tace in anyifa wa zata hurawa hanci tana wani busan iska wa mutane wai ita anzageta anzagi uwarta karya na fada ba yar bora gidansu bace ita.
Kai haba haba inna haba zagin uwarta kuma ke ki rabani kada in hada dake amma ke sakariyace ashe ban sani ba Rashida.
Har sakarcin naki yakai haka ashe ki zauna kina kishi da matar danki yar cikinki a cikin gidan nan ina ke ina zagin yar nan da ko kanta bata da lokaci balle na wani.
Kai umma zaki soma ke nan baki san kan magana ba sai dijen ta kalleta a hasale tace ba kaiba har kafan zancen na sani ba yanzun kika fada da bakinki ba cewa kinbzageta kin zagi uwarta tayi abinda zatayi din.
Zatako yi saidai ita da take yat halasne ta samu tarbiya daga iyeyyenta ba zata tankaki ba saidai ta nuna ranta ya baci kawai da wata yar banace aida yanzu kin raina kanki a gidan nan.
Allah bata sa,a ranan nima tasan kalata da kyau sannan Umma zagi ke nan don nace kawai uwarta borace tazo tana daga muna kai sai zancen suwaiba dana fadawa inno shi taji dai take fushi ko ?
Wai wata suwaiba kuma Asamau dake daki tana sauraren maganan su ta fito tana fada kedai inna baki iya fita zancen suwaiban nan wanan mai shegen kiba kamar tifa ita zaki kwasowa yayan mu wai.
Nace a bar zancen nan watau baki fita zancen ba ke don ki nuna min kece kika haifi danki ko Dijen ta fada a hasale tana juyawa zuwa dakonta tabar inna din naci gaba da maganan.
Koda na dawo ban bita kanta ba na dai shiga na gaidasu na gaida Dije na fito don ina son inyi girki saboda na kwana biyu ban girka abinci naba Dije ba gashi na kula girkina take ci sosai ita.
Zancen kuma munyi shi da hannatu a school tabani shawara kan na kiyayi inna don so take ta bata min suna kada kuma in fasa kyautata mata tunda ina tare da danta.
Wanan shawaran na hannatu na rike a raina yasa na dawo banwa kowa magana ba iyaka dai zan kara nisanta kaina da inna din don na fahinci dai bata kaunana kome zan mata kuwa.
Ranan sati ban fita school don haka na shaki barcina har tara na safe kodana tashi na shiga cikin gidan nasamu inna din ta fita nagaida Dije da kwana na fito na gyara part dina na dora girki dama na sayo icce fish tun a school na gyara nayi miya dashi don zuwan kannena da ummah tace zata turo min su.
Goma da yan mintoci na fito wanka na shirya ke nan naji sallaman su a gidan nayi masu oyoyo zuwan su ya dauke min hankali ga komai duk da rashin kirana da master baiyi a yanzu yana dan damuna nasan kuma fushi yakeyi dani kan zancen bada number wayanshi danayi ga mahaifinshi din.
Muna tsaka da kallo da kannena a MBC 3 wayata ta dauki kara nakai hannu na karba daga hannun datti kanina shine a layin yake kira kiri kiri harya katse naki daukan wayan nima na kuma kashe wayan na jefa jakata.
Mikewa nayi na shiga daki na kwasowa yaran kayan makulashe na zube a gabansu suka fara murna da ganin hakan na koma na debo na nufi cikin gida na samu su Aisha dukkan su tare da Dije a zaune saman tabarma na mika masu ledan suka karba suna godiya.
Nan nake fada masu zuwan kannen nawa don sai lokacin suka san yaran na gidan a lokacin don part dinane na farko nasu yana ta daga ciki.
Don haka shine yasa basu sanin wanda ya shigo wurin nawa gashi kuma wurin da katanga da kofa mai kauri dayayi kokari yasa lokacin auren mu.
Nabada baya naji Asamau na fadin kai kamar kinsan abinda nake son zuwa saye ke nan yanzu sai Dije tace ato ga yarinya da kirkinta amma uwarku nasom bata ta da mugun halinta.
Ita dai aka samu nikan babu uwar mijin da zata sakani a baki in kyaleta ban rama ba duk wadda tayi min ramawa zanyi ba ruwana da wata uwar miji.
Jin hakan baisa na tsaya ba na koma part dina wurin yaran na sanesu suna fada wai datti ya kwashe sweet ya basu kadan nace su bari na kara masu wani.
Na shiga na dauko zan fitone naji datti na fadin anty jiya anyi fada da mama da ummah har mama tace wai bamu samun komai saidai ummah tayi ta wahala damu yaranta sun gama kwashe komai.
Shi yaron abinda yaji shiya fadi a cikin shirmenshi ni kuma ya barni da nazarin me mamake nufi da hakan data fada garemu duk da shirmesa na yara ya fada na fahinci wani abu.
Watau tana ganin yarantane manya a gidan mu sun kwashe komai da Abban mu kedashi yanzu saidai ummah tayi tayin wahala akan mu ke nan.
Inko hakane Allah yafita yafi sherinta don Allah yasan da duk bawansa dake duniya nan fadan Abba da hjy karima da naji su ummah na magana a waya kuma ya sake dawo min a rai nake tambayan kaina komeya kawo fada tsakanin su oho ?
Wuni mukayi da yaran sai dare shehu yazo ya kwashesu zuwa gida naji kamar kada su wuce su barni a wanan gidan da nake zaman shi kamar na dole yanzu.
Anyi haka da kwana biyu Allah ya dawo da master lafiya a cikin dare sosai ya iso don zuwa lokacin kafin iso din har hakkurin yan uwanshi ya soma karewa a lokacin .
Don sun fara tambayan wai ina yajene haka har yake neman ya kwaahe wata baya nan itako inna cewa tayi cikin magana nidai Allah ya cece mu idan ba wani mugun wuri aka tura min shi ba don ya samu kudi ayi wadda akaso.
Dijece ta bata amsa a