Showing 69001 words to 72000 words out of 257873 words
yayi ƙorafi ba. Se da ya kammala ya dawo cikin falon kafin na matsa kusa dashi ina cewa
"Kuma ɗazu daka dawo se baka tashe ni ba"
Kallon rashin fahimta ya mun, ban damu ba naci gaba da cewa
"Yanzu saboda Allah duk yanda nayi maka magana baka haƙura ba se da kace ta tafi? Haba Bilal, a zato na ko can wata bare ce tazo gidan nan cin arziƙi ai beci ka koreta ba balle ƙanwar ka uwa ɗaya uba ɗaya ashe ma duk faɗar da kake tana da matsayi a gurin ka duk surutu ne
gaskiya baka kyauta ba kuma ban ji daɗi ba gashi na kira wayar ta ma bata amsa ba nasan fushi tayi".
Kanzil bece mun ba, abu da me ciki abu kaɗan ke hasala ni u duk hidimomin su shara mopping yayi shirin aiki ya fita. Se da ya tafi na tuna ban tambayeshi zan fita ba, a waya na kira shi nace masa zanje gida na duba Amirah dan tayi zazzaɓi se yace na bari idan ya dawo se muje tare. Na sake gwada kiran Fadila ta buɗe wayar amma haka ta ƙaraci ringing bata amsa ba se na kira Abubakar dan hankali na ya kasa kwanciya ina so na tabbatar da lafiyarta tunda ko babu komai daga gida na ta tafi. Abubakar yace mun ta koma can gidan su taje tana kuka ya tambaye ta meya faru taƙi gaya masa sanin da zeyi baze wuce ita da Bilal bane shi yasa ma be biyo kadin dawowar tata ba kuma yau da safen ta tafi gidan Anty Amina babbar yayar su. Ni dai tunda naji tana lafiya shikenan can su ƙarata da ɗan uwanta shi ya kore ta ba ni ba.
Kwana uku tsakani Hajja ta dawo, ita da aka ce zatayi sati biyu. Tun ana gobe zata dawo ɗin Bilal ya gaya mun dake naje gida na samo yan kuɗi se nayi amfani dasu nayo cafane nayi mata girki yan da naga Anty Labiba tana yi idan surukar ta tayi tafiya ta dawo zata mata girke girke ta kai mata. Da wuri suka iso dan asubanci suka yo kamar sanda zasu tafi, da la'asar bayan ya dawo aiki yayi wanka na kwashi kwanuka ya goya ni a mashin muka tafi gidan, rabon ayi. Da ace nasan abin da yake jira na a gidan da ban yi giggiwar zuwa mata sannu da zuwan ba. Da Yaya Uwani wadda Bilal yake bi muka fara cin karo a soro zata fita mu kuma zamu shiga, da fara'a na shiga gaishe ta, irin kallon banzan data watsa mun haɗi da tsaki yasa jiki na yayi sanyi laƙwas nabi bayan Bilal da dama be tsaya ba.
"Yanzu ke har kina da kunyar da zaki sake tako ƙafar ki cikin gidan uban Fadila?" Kalaman da Hajja tayi mun maraba dasu kenan. Nayi zukuɗi ina ƙoƙarin tantance in da maganganun ta suka dosa amma na kasa se kawai na zura mata ido ina jin irin fisaji da cin mutunchin data ke mun a maganganun nata nayi nasarar gano akan Fadila takeyi. Bani kaɗai ba hatta iyaye na dake can gida basu san wainar da ake toyawa ba se da suka amsa rabon cin mutunchi a gurin Hajjan,
"Daɗin abun tun kafin uban ki yasan zeyi arziƙi a duniya uban Fadila yayi da har zaki mata gorin gida gidan ma na ɗan uwanta da idan ya faɗi ya mutu yanzu tana da gadon sa. Ko da yake ba laifin ki bane, laifin sa ne daya barki kika bararraje har kike tunanin kin ci gida se wanda kika ga dama ze shiga ya zauna" ta faɗa tana kumfar baki.
Sautin kukan da na keyi ƙasa ƙasa ya ƙaru, a duniya ka mun komai karka zagi iyaye na ko kaci mutunchin su.
"Haba Hajja ki bari mana ya isa haka" naji muryar Bilal, se na ɗaga kai na kalle shi dan ban taɓa zaton yana ɗakin a tsaye Hajjan take mun wannan tijarar kuma yayi shiru ba.
"Yanzu kana tsaye kana ji ana tuhumata da laifin daka aikata?" Na faɗa cikin kuka, ya kalle ni yace
"Ban gane ba?"
Kan Hajja na juya ina kukan nace
"Allah shine shaida ta ban kori Fadila ba, idan kuma zata faɗi gaskiya ni ko kallon banza be haɗa ni da ita ba balle nace ta bar gida. Ina ruwa na da zaman ta? Shi me gidan ai gashi nan shi yace baya buƙatar zaman ta kuma Allah shaida sanda ya kore ta ma bana gurin kuma kana tsaye kana kallo ana tuhumata ba zaka faɗi gaskiyar abinda ya faru ba" na ƙarasa ina kallon Bilal daya tsuke fuska yana muzurai.
Hajja ta rafka salati ta shiga tafa hannu tana cewa
"Ba shakka yau naga in da ake bariki, kai Bilal uwarka Halima na magana se ka rufe ni da duka saboda ma mata ƙazafi". Maimakon ya kare ni se gani nayi ya juya ya fice daga ɗakin gaba ɗaya ita ko kamar an iza wuta taci gaba da maganganu tana faɗar duk abin da yazo bakin ta. Daƙyar ina ganin dishi dishi na miƙe jin tijarar bame ƙarewa bace, Allah ya taimake ni ina fita daga gidan na samu Napep kai tsaye na wuce gidan mu. Ina rusa kuka na shiga gidan ba tare da na ko sallami me Napep ɗin ba ya biyo ni yana tambayar kuɗin sa.
A ƙasa na zube ina cigaba da rusa kuka Mama dake kitchen ta fito kusan a guje tana tambayar waye? Gani na yasa ta ƙaraso da sauri ta ɗago ni cikin tashin hankali tana cewa
"Meya samu Bilal ɗin?". Se da naji numfashi na na neman ɗaukewa kafin na haƙura na dena kukan amma naƙi cewa komai tun Mama na tambayata harta tashi ta barni ta kira Abba a waya tace masa gani nazo ina kuka naƙi cewa komai yace mata karta kira kowa gashi nan zuwa. Ina kwance ina jan rai, wani irin azababben ciwon kai ya dirar mun lokaci ɗaya. Ina kwance riƙe da kai Abba ya dawo, tiryan tiryan na kora musu yanda akayi tun daga zuwan Fadila har zuwa yau ɗin. Mama ta zabga tsaki tace
"Tun wuri ki nemi yafiya ta dan wlh kin ɗauki alhaki na gaba ɗaya kin tada mun da hankali na ɗauka ma wani tashin hankalin ne ya afku" Abba ma miƙewa yayi yace
"Allah ya rufa asiri" daga haka ya fice daga ɗakin. Mama ta dira mitar ɗaga mata hankalin da kuka na yayi kafin ita ma ta fita ta bani guri. Se naga su abun ma be dame su ba kenan, ba ma wanda ya sake bi ta kai na se da akayi magriba Mama ta leƙo ni lokacin har baccin wahala ya fara fizgata kai na na ciwo sosai. Se da naci abinci nasha magani nayi wanka kafin na kwanta. Bilal be kira ni ba har kuma bacci me nauyi ya kawashe ni be zo ba se da safe Mama take cemun wai miji na yazo tayi ta tashi na ban farka ba shine yace a barni kawai.
"Se ki maza ki gama abin da zakiyi Mu'azzam ya kai ki gida dan jiya har gurin sha ɗaya yana nan se kace wanda aka ce za'a cinye ki" Mama ta faɗa. Nayi rau da ido nace
"Da yazo kin masa maganar abun da Hajjan su ta mun?"
"Ni kuma a wane hurumi? Wannan ai tsakanin ku ne kun fi kusa shikenan kuma saboda kinyi ba daidai ba maman mijin ki ta miki faɗa se na shiga na rama miki kike nufi ko me?" Mama ta faɗa. Se ko hawaye suka ɓalle mun ta miƙe tana cewa
"Kin so dai ki ƙarawa kanki wata damuwar banda haka wanda ya siyi rariya ai dole dama yasan zata zub da ruwa. Duk mutumin da Allah ya haɗa ka zama dashi se dai haƙuri da taka tsantsan kawai abinda ya rigada ya faru kuma ai ya faru se dai ayi rigakafin wanda be zo ba" ta faɗa tana ficewa daga ɗakin.
Ba dan raina ya so ba se dan rasa goyon bayan Mama na tattara Mu'azzam ya kaini gida da yamma na ringa share hawaye a hanya, an mun wulaƙanci na tafi gidan mu akan su shiga su ƙwatar mun yanci ba daraja sun koro ni yanda gobe ma za'a ji daɗin sake ƙala mun abin da ban aikata ba aci mun mutunchi da gangan. Yau na ga ranar Anty Labiba, ita kaɗai ce zata tsaya mun amma da nauyi abun daɗi be kaini gidan ta ba yanzu se na kwashi matsala naje mata.
A gida muka tarar da Bilal, Mu'azzam be shiga ba ya gama sauke mun kayan da ban san dasu ba a nan tsakar gida ya barsu yayi tafiyar sa. Ina ƙoƙarin saka key na buɗe ƙofar falo aka buɗe ta daga ciki Bilal ya fito a wani hargitse kamar wanda ya kwana be runtsa ba yana gani na ya wani rungume ni da ƙarfi se kace wanda ya shekara yana nemana se yau Allah ya bayyana masa ni, dana tuna yanda ya tsaya Hajjan su na zagi na ya bece komai ba take ido na ya kawo ruwa na shiga ture shi amma yaƙi saki na seka ɗauka ta da yayi cak ya wuce cikin ɗaki dani ina ƙoƙarin fizgewa be sake ni ba se da ya dangana ni da gado na fashe da kuka sosai ina matsawa baya ya biyo ni yana cewa
"Me kike yi haka Halims? kin san irin tashin hankalin da kika jefani jiya kuwa? Me yasa zaki tafi baki kira ni ba? Saboda Allah da kika je gidan me kika ce musu?"
Haɗe kai da guiwa nayi na shiga rera kuka, ya kaɗa ya raya nayi shiru na masa banza daya matsoni ze sakani jikin sa kuma zan fasa wani kukan na janye se ya haƙura ya barni yana cewa
"Ni dai karki jiwa kanki ko abinda yake cikin ki ciwo na barki bazan sake taɓa ki ba amma ki dena wannan kukan".
"Akan me zaka koreta kuma a ɗora mun laifi har azo ana zagin iyaye na da basu ji ba basu gani ba?" Na faɗa cikin shashsheƙa. Kamar wani na Allah yayi ƙasa da kai kafin ya kwaso rantsuwa yace
"Bani na koreta ba"
"Ni na kore ta kenan kaima ka sake tabbatar da hakan?" Na faɗa ina fashewa da sabon kuka. Se ya taso ya dawo in da nake ya jani jikin sa yace
"Ita tacewa Hajja kin barta da yunwa kuma da tayi miki magana ki bata abinci shine kika ce ba zaki bada ba ta koma gidan mijin ta ko ta tafi gidan uban ta taci wai tazo ta takura miki ta hana ki sakewa a gidanki. Tun kafin Hajja ta dawo ta kira ni ta gaya mun abinda Fadilan tace kin mata na kuma tabbatar mata ƙarya be nasan ba zaki mata haka ba ita kanta se da na same ta na ja mata kunne shine ma nasa ta tattara ta koma gidan ta kafin Hajjan ta dawo na ɗauka maganar ta mutu kin san Hajja ita kuma da ruƙon magana in dai ba ta amayar ba bata jin daɗi amma nasan tunda ta rigada ta miki faɗa yanzu shikenan maganar ta wuce musamman tunda ta tabbata hakan be faru ba ƙarya Fadila ta gaya mata". Haka ya ringa lallashi na yana gaya mun maganganu har seda ya wanke baƙin sa da na gani na maida laifin kacokam kan Fadila domin ita ta shirya komai na kuma yarda bashi da laifi abu ɗaya da naji ba daɗi da be tsaya mun ya fitar da gaskiya ta a gaban Hajja ba, amma kuma dana tuna ita ɗin bata da daɗin sha'ani be zama lallai ta fahimce shi a lokacin ba ta yuwu ma ta haɗa dashi yanda kuma take magana ba tare da tauna kalami ba se ta faɗa masa wani abun mara daɗi da ze iya tasiri a rayuwar sa tun da mahaifiyar sa ce.
Babu kunya kuma kwana biyu da yin haka da yamma ina zaune se ga Hajja da jikarta Mansura suka zo da kwanukan abincin dana kai mata waccen ranar wai ta rakota ta bani haƙuri, ni abun ma se ya bani kunya ya bani takaici. Ta ringa zagin Fadila tana cewa duk ita ta zugata se daga baya da Bilal ya zaunar da ita ya mata bayani ta gane gaskiya tasan bata kyauta ba data hau kan magana kawai ta zauna ba tare da bincike ba. Ni dai nayi ta Allah Allah ta tafi kafin ta sake samun wani abun da zata ce na mata laifi har raina kuma na ƙudire tsakani na dasu gaisuwar mutunchi babu dogon zumunchi tunda na fahimci abun a jinin su yake su rufe ido su ciwa mutum mutunchi idan abu ya haɗo ku daga baya kuma ba kunya su waske.
BAYAN WANI LOKACI
[5/19, 22:05] Buhainat: *KURA A RUMBU*
*(Based on true life event, some parts are fictional to spice up the story)*
*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WOMEN OF WORDS WRITERS ASSOCIATION (WOW)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*
*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya naira 800, biya a asusun*
*1840175439*
*Access bank*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*
*PAGE 18*
Haka rayuwa taci gaba da gangarawa; yau fari gobe baƙi. A yanzu da nake lissafa watannin aure na goma sha biyar da Bilal shekara ɗaya da wata uku kenan, tabbas a zaman da mukayi nayi karatu da yawa tattare da halayen sa waɗanda a baya ban san su ba. Babban abinda na fara naƙalta da Bilal shine mutum ne me son abinsa. Tabbas Bilal nada son abin sa kuma ya kan iya rufe ido ya cima koma wanene mutunci har idan ya shiga gonar sa, idan yayi wani abun se na shiga mamakin ta yanda har muka shafe tsayin shekaru shida muna soyayya ya akayi ban taɓa fahimtar shi ɗin haka yake ba. Da fari abun ya dame ni ko nace yana damu na, amma dana zauna nayi wani tunani na kuma yi amfani da maganar Hausawa da suka ce idan mutum ya nuna yana son abun sa ka taya shi, se ku zauna lafiya. Hakan nayi amfani dashi kuma nake zaune lafiya da Bilal.
Idan akwai abinda yake sosa mun rai wani lokacin be wuce yanda ni kullum na buƙaci wani abu a gurin sa da yake ganin be zama dole ba ze rufe ido yaƙi mun amma ina kallo ko da bashi ne ze ci ya yiwa yan gidan su. Tabbas ina jin babu daɗin hakan a raina; a ƙalla ko da ba a duk sanda na buƙata ba, na kan so ace yana kamanta kyautata mun nima. Amma kuma wani sa'in idan nayi tunanin sai naga hakan ba komai bane. Hajja mahaifiyarsa ce ita tilas ya hidimta mata suma kuma sauran yan uwan sa idan yayi musu zumunchi yayi wa da wannan nake danne kaina musamman kuma da alhamdulillah duk abin da na rasa a gurin Bilal na kan samu sama dashi a gurin iyaye na da basa gajiya da hidimta mun musamman Abba kusan ko da yaushe naje gida ko mukayi waya ko wani cikin ƙanne na ze zo se ya bayar da saƙon kuɗi ko abin amfani an kawo mun. Ita kanta Mama duk da yanda kullum Anty Labiba take cikin zugata akai na wani sa'in taji wani sa'in ta toshe kunnenta; musamman tun da ciki na ya fara girma, wani tausayi na take ji bini bini zata yo mun miya ta bayar a kawo mun se dai Bilal ya tafasa mana shinkafa ko taliya muci.
Nayi zaton tun da ciki na ya fara girma Bilal ze yi tunanin ya kamata mu fara siyan kayan baby muna ajiyewa, ban masa magana ba, saboda tun saɓanin da muka samu da babbar sallah akan naman layya nayi alƙawarin ba zan saka masa baki a duk wani abu daya shafe shi ko kuma ya zama dolen sa ba. Raguna guda biyu ya turke tun ana sallah saura kwana biyar wanda yace ɗaya Hafiz ne ya bashi ɗaya kuma shi da Abubakar suka haɗa kuɗi suka siyawa Hajja. Ranar jajiberin sallah Babangida ɗan ƙanwar Hajjan ne yazo ɗaukar Rago, guda ɗaya ya ɗauka ya tafi dashi ba'a rufa awa ɗaya ba se gashi ya sake dawowa ina cikin ɗaki kukan ragon ne ya fito da ni dan sam banji motsin buɗe get ba ban ma san daya fita be kulle mun ƙofar da kyau ba.
Ganin yana kici kicin kwance Rago yasa na dakatar dashi ta hanyar tambayar sa lafiya? Ina kuma za'a kaishi?
"Hajja ce tace duka biyun za'a kai can gidan, na leƙo ina ta sallama na zata ma bacci kike baki amsa ba" ya bani amsa. Mamaki ya kamani; me yasa za'a kai ragon kuma can gidan? Na tambayi kaina. Ban sake ce musu komai ba ina tsaye ya gama kwance shi yaron da suka zo tare ya ja shi suka fita waje in da ya bar mashin ɗin sa. Har na ɗauki waya zan kira Bilal a lokacin sr kuma na ce bari kawai se ya dawo, ina tsaka da haɗa masa abin shan ruwa kuwa ya shigo. Daga yanda naga be damu da rashin ganin ragunan ba na fahimci da sanin sa kenan aka kai can.
Se da aka sha ruwa bayan ya dawo daga sallar isha'i kafin na taso masa da zancen,
"Ni nace akai can dan nasan idan an bari a nan ke da kike fama da kanki ba iya aikin zakiyi ba ƙarshe ki tara mutane su cinye" amsar daya bani kenan. Dama cike nake da haushin ƙin yi mun ɗinki da yayi wannan sallar ma yace shi ba ɗinki ne a gaban sa ba ai ina da kaya na saka mana amma a gaba na ya shigo da atamfofi uku harda lace ɗaya na Hajja da Fadila wadda ta sake dawowa gida zama yaƙi daɗi se haushin ya zamar mun biyu ga wancan ga na ɗauke rago yanzu