Showing 129001 words to 132000 words out of 257873 words

Chapter 44 - KURA A RUMBU HAUSA NOVEL

23 Oct 2025

510

yake ɓoye mun ina fara karatun ya barni. Sai da aka kira sallah kafin ya fito ya wuce masallaci daya dawo ina lura da yanda ya kame fuska ta yuwu yayi zaton zan masa maganar waya da kuma yaji banyi ba har na shirya Al'amin zan fita kaishi makaranta yace na bari zai kaishi suka fita harda Sharifa kafin su dawo nayi maza nayi wanka nayi kwalliya.

Bayan mun karya ya ce mun ranar Alhamis zai tafi Abuja kuma zai iya yin sati ɗaya zuwa kwana goma acan ɗin.
"Anty Sa'ada bata da lafiya ɗazu dana fita mukayi waya da Hajja take gayamun har an kwantar da ita a Asibiti jiyan dan haka Fadila zata tafi can ta zauna da ita kafin ta samu sauƙi" ya faɗa. Cikin fuskar jimami na ce

"Allah sarki Allah ya bata lafiya shiyasa bata zo duba Hajja ba ashe" ya amsa da Amin kafin ya ce
"Kinga idan Fadila ta tafi gidan zai zama babu kowa sai Abubakar kuma itama Hajjan jikinta ga yanda yake kusan komai sai an taimaka mata takeyi saboda ciwon ƙafarta"

"Abinda zanyi magana kenan dama nace toh Hajja fa idan Fadila ta tafi tunda itama tana da buƙatar ta" na faɗa, ya goge hannunsa da tissue kafin ya ce
"Na gaya mata zata dawo nan gidan ta zauna kafin Fadilan ta dawo".
[5/19, 22:05] Buhainat: *KURA A RUMBU*

*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*Whatsapp 08142548705* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*

*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya naira 800, biya a asusun*
*1840175439*
*Access bank*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*

*PAGE 33*

Banji komai dangane zaman da ya ce Hajja zatayi ba dukda nasan ba jituwa mukeyi da ita ba amma kuma abinda yake so ne kuma wanda zai faranta masa ni kuma burina a koda yaushe kenan. Har ya fita ya kirani a waya yace na shirya gashi nan dawowa zamu fita tare, da nace masa Al'amin fa kar lokacin tashin su yayi bana nan sai ya ce ai ba jimawa zamuyi ba dan haka nayi maza na canza kayana na shirya Sharifa ina jin horn ɗin mota na fita. Raina fes na kame a gaban mota ina jin wani farinciki na ratsani.

Na daɗe ina hakaito irin haka nida Bilal ɗina mu ringa zagaya gari a mota nasan duk inda muka gilma sai an kallemu an kuma yaba dacewar mu dan sau tari na sha yin yunƙurin yiwa Abba magana akan ya siyamun mota sai kuma na kasa toh gashi lokaci yayi ya mallaka da kuɗin sa ma. Murmushi nayi ina kallon yanda yake murza sitiyari yayi irin zaman nan na yan birni sai ya ƙara kyau haɗi da kwarjini a idona. Na ƙara rungume Sharifa da ta fara bacci kafin na karyar da murya na ce

"To yanzu yaushe zaka fara koyamun mota?" Yi yayi tamkar nai ji ni ba har saida na sake maimaitawa kafin ya mun gajeran kallo haɗi da murmushi ya ce
"Ke da kika tashi gidanku cike da motoci har kyace baki iya tuƙi ba?"

"Idan da na iya ai tuntuni zaka sani" na bashi amsa ina kallonsa, sai ya ɗan taɓe baki ya ce
"Shiyasa ba'a haɗo miki da mota a gara ba kenan ko a siya miki daga baya". Yanda yayi maganar ya saka nayi shiru ba tareda na sake cewa komai ba tun kafin hirar ta canza akala zuwa abinda zai haddasa mana ɓacin rai. Ban sake crwa komai ba shima haka har muka isa Unguwar su Anty Labiba, sai da muka gota gidanta kafin murnar da na farayi ta koma ciki dan na ɗauka bazata zaiyi mun yau dai muje gidanta da ni da shi. Layin daya koma bayan su ya shiga na kalle shi na ce

"Na ɗauka gidan Anty Labiba zamuje" ba tareda ya kalleni ba yana ƙoƙarin tsayar da motar a ƙofar wani madaidaicin gida na masu rufin asiri ya ce
"Ai saiki sauke". Ban fita daga motar ba bayan ya sauka sai da ya mun magana dan ban san ina muka zo ba balle nayi garajen fita, ina tsaye ina ƙarewa layin kallo, duk gidajen gurin ƙanana ne na masu ƙaramin ƙarfi ba kamar can kan layin su Anty Labiban ba. Kofar wani gida mai ɗan dama dama akan sauran ya nuna na rufa masa baya, ya jera sallama sau biyu kafin daga ciki aka amsa tareda bayar da izinin shiga sannan ya shiga na bishi a baya ina ƙarewa gidan kallo.

Ƙaramin gida ne dan gaba ɗaya ɗakuna uku ne a ciki falle falle sai banɗaki da kitchen duka a tsakar gidan da rijiya amma tun daga waje zaka yabawa tsaftar mazauna cikinsa domin hatta da kwatar su tsaf take an yasheta haka tsakar gidan daya sha fasassun tiles tsaf yake babu ko tsinke banda tabarmar da wata mata mai matsakaicin jiki take zaune sanye da hijabi tana jan carbi da alama sallar walaha ta idar.

Cikin fara'a ta shiga yi mana maraba, na zauna gefen tabarmar Bilal kuma yaja kujerar tsugunno dake gefenta ya zauna yana sunne kai tamkar wanda yake a gaban surukai.
"Sannunku da zuwa" ta sake nanatawa cikin fara'a na gaisheta ta amsa tana jan Sharifa amma taƙi zuwa Bilal ma ya gaisheta haɗi da tambayarta ya ƙarin haƙuri hakan ya saka nima nabi bakinsa nayi gaisuwar dukda bani da masaniyar mace ce ko namiji ma wanda ya rasun.

Tashi tayi ta kawo mana ruwan pure water da biscuit ta bawa Sharifa, bayan ta zauna ta ce
"Amma bata san da zuwanka dan bata yi zancen ba kuma yanzun nan basu ma jima da fita ba". Ji nayi ƙirji na ya buga ras na ɗaga kai na kalli Bilal da cikin sa'a muka haɗa ido shima ni yake kallo kafin ya ɗauke idonsa ya bata amsa da cewa
"Eh ban gaya mata zanzo ba gaskiya munyo ta nan haka ne nace bari mu ƙaraso Halima tayi muku gaisuwa".

"Allah sarki aikuwa mungode Allah ya bada lada" ta faɗa ya amsa da amin ni dai ina sauraron su cikin kaina kuma ina ƙoƙarin tantance wacece itan da suke magana akai?
Shiru ya gifta na kusan minti biyu shi kansa yana ƙasa sai ita matar dake jan Sharifa da har sannan taƙi yarda da ita sai ya miƙe yana laluba aljihun sa yace
"Bari mu wuce Umma"
"Har zaku tafi?" Ta faɗa, na miƙe nima sai itama ta miƙe tsaye tana cewa
"Shikenan toh ku gaida gida Halima nagode Allah yayi albarka na amsa da "Amin" ina yin gaba. Ta gefen ido naga ya duƙa ya ajiye mata kuɗin da ban san ko nawa bane na ƙarasa ficewa ina jiyota tana ta jera masa addu'oi, na jingina da jikin mota ina sauraron fitowarsa gaba ɗaya kaina ya cika da tunanin nan ɗin ina ne dan dai ban taɓa ganin matar ba balle nace danginsu ce kai ko a labari bai ma taɓa cemun suna da yan uwa a nan unguwar ba dan da ace yar uwarsu ce tun sanda yake zuwa hira gurina gidan Anty Labiba zan san da zamansu.

Sai da ya ƙara kusan minti biyar ina hangosu tsaye a soro suna magana kafin ya fito yana wani ɗauke kai kamar baya so mu haɗa ido ya buɗe motar muka shiga, ban ce masa ƙala ba har saida naga yana ƙoƙarin sake wuce gidan Anty Labiba kafin na ce
"Amma na ɗauka zamu shiga ai ko a tsaye ne mu gaisheta".

"Sauri nakeyi zan wuce gurin aiki" ya bani amsa sai nayi saurin cewa
"Sai kayi tafiyarka idan mun gama mu wuce gida"
"Shi kuma Al'amin ɗin wa kika barwa shi?" Ya sakw faɗa cikin tsare gida, zan sake magana ya ce
"Da Allah ki kyaleni in kin shirya zuwa ki saka rana kije amma yanzu babu inda zaki shiga". Haushi yasa ban sake ce masa komai ba, ƙarin takaici na ɗauka gida zai mayar damu da ya hanani shiga gidan nata amma sai gani nayi ya faka a junction ya zaro dubu ɗaya daga aljihun sa ya miƙa mun, ina kallonsa ya cilla kan mota yayi gaba abinsa bayan mun sauka haka na tare Adaidaita muka wuce gida.

Yinin ranar da tunanin gidan da mukaje na yi shi, bai dawo da wuri na sai bayan sallar isha'i ya taho da jakar kayan Hajja da wasu abubuwan buƙatarta. A ɗaki na ajiye mata kayan, saida ya zauna cin abinci na kasa daure tunanin daya addabeni na ce masa
"Ni kam gidan su waye mukaje ɗazu ne?".

Yi yayi kamar baijin ba ni kuma na sake maimaitawa, ya wani haɗe rai ya ce
"Gidan Umma Zaliha ne ƙawar Hajja ce mijinta ya rasu sati biyu kenan". Kwata kwata ƙwaƙwalwata bata kama maganar ba musamman a yanda ya wani tsare gida kamar mara gaskiya, nima haɗe fuska nayi nace
"Wannan ɗin ce ƙawar Hajja matar da daga ganinta ba zata wuce sa'ar Anty Amina ba ma idan ma zata girmeta da kaɗan ne"

"Ƙarya na miki kenan?" Ya faɗa yana aje cokalin da yake cin abinci, na kalli gefe na ce
"Ni bance ƙarya kayi mun ba amma kuma nasan ba gaskiya ka faɗa ba tunda kake zuwa unguwar gurina ya akayi baka taɓa faɗa mun akwai ƙawar Hajja a gurin ba sai yau"

"Bana son hauka da shashanci Halima. Wato saboda kinga na sake miki kwana biyu shiyasa har kika samu damar ki ajiyeni kina tuhumata kamar wani ɗan cikinki ko? Uwata ce ke ko me da kike zaton zan miki ƙarya?" Yayi maganar cikin ɗaga murya. Sai na waiga na kalli cikin falon inda Al'amin da Sharifa suke duk su biyun sun zubo mana ido da alama hargaginsa ne ya janyo hankalin su dan haka na sauke murya na ce

"Da dai kayi haƙuri ka dena wannan ihun kaga yara suna kallonka". Ai ina wuta y jefani a ciki wai mahaukaci ma na ɗauke shi kenan nace yana ihu, ya ringa surfa mun tijara kafin daga ƙarshe ya fice daga gidan gaba ɗaya garin sauri kuma ya manta wayarsa dake kan dining bai kula da ita ba. A gurin na zauna na rizgi kuka Al'amin da Sharifa suna tayani, ganin suna kukan ya saka na rarrashi kaina daƙyar nayi shiru na goya Sharifa Al'amin kuma ya kwanta akan cinyata.

Muna zaune shiru a falo kamar marayu naji ƙarar wayarsa a gurin dining, kamar kar na kula amma zuciya da shaiɗan suka ingizani ko babu komai zan samu amsoshin zarge zargen da suke mun yawo a ƙwaƙwalwa sai na janye Al'amin na miƙe kafin na kai gurin kiran ya katse na ɗauki wayar na danna. Password ɗin sa da na sani na saka suka ce wrong. Naja kujera na zauna na sake gwadawa ko ban shigar daidai bane still bata buɗe ba, tagumi nayi ina ƙoƙarin tuna wata number mai muhimmanci da zai iya sakawa a matsayin password ɗin sa daidai nan kiran ya sake shigowa gabana ya yanke ya faɗi da ganin sunan dake yawo akan screen ɗin wayar "DUNIYA TA".

Cikin son in tabbatar da cewar Hajja ce ko ba ita ba domin kuwa a zatona ita kaɗai ce zata iya samun matsayin wannan sunan a wayar Bilal tunda ni dai na san da HALIMS yayi saving number ta. A speaker na saka wayar bayan dana amsa kiran, daga can naji muryar mace cikin sautin da ban tantance haka take magana ba ko kuma shagwaɓa take masa tayi sallama take kaina ya sara, zuciyata ta shiga bugawa da sauri haka gaba ɗaya ilahirin jikina ya ɗauki rawa zufa ta shiga keto mun tamkar wadda nake a gaban murhu dukda kuwa falon a wadace yake da iskar fanka da Ac dan akwai wuta amma lokaci ɗaya naji na fara ɗigar da zufa.

Dukda a zaune nake kan kujera amma sai na ringa jin kamar a tsaye nake har jiri yana neman kayar dani dan haka na dafe table ɗin gabana da hannaye biyu muryar budurwar na cigaba da yi mun amsa kuwwa tana tana nanata "Hello, Yah Bilal kana ji na kuwa?"

Allah ne ya taimake ni ta katse wayar daga can zuwa lokacin ba wani gane komai nakeyi sosai ba dan ji nayi tamkar an ɗora mun gingimemen dutse a kaina ya danne mun ƙwaƙwalwa ya hanani tunani. Ƙarfin halin sake ɗaukar wayar nayi, tunanin gwada shekarar daya gama secondary school nayi dan yana yawan faɗar shekarar nada tarihi a rayuwar sa dukda ban san ko tarihin menene ba cikin sa'a kuwa ina sakawa wayar ta buɗe kai tsaye na dirarwa Messages ɗin sa.

Number JALILAH da na fara cin karo da saƙon ta wanda bai jima da shigowa ba dan bai ma karanta ba na buɗe. Zan iya cewa tunda nake a rayuwata ban taɓa shiga tashin hankali makamancin wanda na tsinci kaina a lokacin ba, na ringa buɗe idanuwana da suka mun nauyi suna neman rufe kansu amma naƙi basu damar hakan burina na karanta abubuwan da nake gani wanda duk kalma ɗaya nake jin ta tamkar ɗigon dalma a zuciyata. Saƙon ƙarshe da tace ya duba Whatsapp ta ajiye masa saƙo na karanta dan haka na fita daga message ɗin na koma Whatsapp.

Na miƙe tamkar wadda tasha tayi mankas ina tangaɗi goyon da nayi yana rinjayata, da bin bango na isa ɗaki na maido ƙofar na kulle da muƙulli kafin na kwance Sharifa nayi zaman dirshen a ƙasa na buɗe Whatsapp ɗin nasa. Unread messages biyar na gani wanda Jalilar ta aiko da alama kuma hotone, saboda yanda zuciyata take bugawa ji na ringayi tamkar zata fito ta bakina wani irin tsoro da ban san dalilin sa ba ya lulluɓe ni amma haka nan na buɗe chat ɗin nasu da nake jin wata murya a ƙwaƙwalwata tana ƙoƙarin hanani buɗewa sai dai aikin gama ya rigada ya gama.

Da ƙarfin gaske na runtse ido na bayan dana saki wayar daga hannu na cikin furucin da babu sauti na shiga nanata Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un sakamakon mugun ganin da nayi, nafi minti biyu ina ƙoƙarin tattare hankali da ƙoƙarin na gane a zahiri ne abubuwan da suke faruwa ko kuwa hallucination nake yi? Tamkar mai taɓa kunama haka na sake ɗakko wayar na buɗe idanuwa suka sake yin arba da mugun hoton da na gani wanda ya sake tabbatar mun zahiri ne ba wai tunani nake ba, a hankali na sake kife wayar a jikina na shiga sauke ajiyar zuciya tamkar wadda tayi gudun tsere, ratar minti ɗaya zuciya ta sake ingizani na ɗaga wayar, nayi scrolling har zuwa farkon chat ɗin su kafin na fara tilawa ina karantawa tareda sauraron muryoyin da sukayi musaya a tsakanin su duk da wata muryar tafi ƙarfin kunnuwa na su saurara ba murya ba wani rubutun kansa ya girmi ƙwaƙwalwa ta da ta karanta shi.

Na ga tashin hankalin da ko bisa kuskure wani ya alaƙanta Bilal da wannan muguwar ɗabi'ar tabbas mai rabani dashi sai Allahn daya halicce mu. Ashe dalilin daya saka ya koma kwana a ɓangaren sa kenan shine kuma dalilin zaryar da yakeyi tsakanin Kano da Abuja ya kife ni da sunan aiki yake zuwa ashe alaƙar da take tsakanin sa da JALILAr kenan?

Kasa cigaba da bin chats ɗin nayi saboda yanda abinda nake ji da gani ya ƙazanta, na kife wayar a cinyata na fashe da kukan da ni kaɗai da na ci karo da wannan baƙin cikin sai kuma wadda ta taɓa tsintar kanta wanda ta bawa dukkan yardarta a cikin irin wannan yanayin kaɗai zata iya hakaito abinda nake ji. Tabbas Bilal yaci amanata ya kuma ci amanar yarda da SO.

Tambayar da na ringa yiwa kaina dame na rage shi da har ya zaɓi wannan hanyar? Ashe ban ishe shi ba? Duk yanda nake ƙoƙarin ganin na kare masa haƙƙin sa ta yanda bazai ga haram a waje ta burge shi ba ashe shi ba haka bane a gurin sa? Da nake masa kallon wanda mace bata dame shi ba har wasu lokutan nake ganin kamar ina matsa masa da fitina ashe ni duk haukan banza na nakeyi ni ɗin ce ban isa ba ban kai macen da zai ringa nuna zalamarsa akaina ba yana tareda ni ne kawai amma hankalinsa yana kan wasu?

Na rintse ido na hotunan tsiraici JALILAH suka shiga gilma mun. Tabbas a inda mace kamarta take ni ɗin ban isa komai ba sai dai kuma a yanzu na tabbatar da Bilal ƙasurgumin munafuki ne kuma maƙaryaciya saboda yanda yasha faɗa mun shi cikar jikin Mace bata wani burgeshi yafi son komai daidai irin nawa ba wanda zai rasa yanda zaiyi dasu ba amma gashi yanzu na kamashi yana tarayyar haram da mai irin jikin da yake faɗar baya burge shi har yana faɗa mata kalaman da tunda nake dashi ni matarsa ta sunna ko kusan bai taɓa furta mun ba.

Nayi kuka tamkar raina zai fita, sai da naji numfashi na ya fara yi mun sama sama kafin na fara ƙoƙarin tsayar da kukan sai dai na kasa saboda yanda muryoyi da hotunan da suka samu mafaka a ƙwaƙwalwata suke sake jefani cikin wani yanayi. Allah kaɗai yasan ire irenta nawa yake tarayya da su tunda nata kaɗai na gani yanzu. Waya sani ko itama waccen da yayi saving da DUNIYAR SA itama irin mu'amalar da take tsakaninsu kenan?

Ina nan zaune tamkar mara rai, kukan zahiri ya tsaya mun sai na zuci da na cigaba da yi, na yunƙura daƙyar saboda buga ƙofa da kuma kukan da na jiyo Al'amin yanayi. Daƙyar na buɗe masa ƙofar dai dai lokacin kuma Bilal ya shigo falon idanunmu suka faɗa cikin na juna nayi masa kallon da ko a mafarki ban taɓa zaton zanyi masa irin sa ba, kallon tsana mai cike da dana sani da nadamar kasancewa a duniyar sa. Gurin da na taso na koma na zauna haɗi da mayar da kaina baya na ɗora akan Gado, Al'amin ya kwanta kusada Sharifa yaci gaba da baccin sa ina jiyo motsin Bilal a falo da alama wayar sa yake nema kafin na jiyo yana kiran sunana cikin sautin da ban tantance ba dan sai naji kamar muryarsa a sanyaye take.

A yanzu

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login