Showing 228001 words to 231000 words out of 257873 words
tarkon Ahlan ba, ko da ya fara kiranta ta yaƙi zuciyarta akan ba zata zake amsawa ba dan har blocking layin tayi sai dai yana canza wani layin ya kirata ya kanainayeta da daɗin baki akan shi ba wata mu'amala mara kyau yake so su ƙulla ba kawai ta burgeshi ne yana so su zama yaya da ƙanwa shikenan ta biye masa suka fara waya.
A hankali kuma tunda dama biyu ce ta haɗu kafin ta ankara ya mayar da ita ruwa, dukda waya kawai sukeyi amma tun bata biye masa harta fara suke zantukan da basu kamata ba, ganin kuma ko hoto bai taɓa nema ta tura masa ba iya zancen wayar ne ya saka ta saki jiki ga kuɗi yana tura mata kamar bai san zafinsu ba dama kuma ta farayin broke ta kuma lura da take-taken Bilal shi ɗin ma dai irin sauran mazan da ake bayar da labari ne.
A waje kamar zasu tsinke kansu su bawa mace saboda ƙauna da zarar sun sameta kuma sai a fara zaman haƙuri, tunda sukayi aure watanni kusan huɗu kenan naira biyar bata shiga tsakaninsa da ita ba. Zai yi cefane duk abin buƙata zai siyo ya ajiye mata yana ƙorafi yana mita amma dai ba zai bata kuɗi a hannu ba, toh hakan ma bai dameta ba tana son sa a hakan kuma zata zauna dashi sauran buƙatunta kuma zata nemi kuɗi tayiwa kanta ita wannan ba zai zama matsala tsakaninsu ba tunda dai baya saka mata ido akan harkokinta ko abubuwan da yake ganinta da su.
A bazata taji saukar muryarsa; lokaci ɗaya kuma ta daskare a gurin da take tayi luf a kwance kamar matacciya dan hatta zuciyarta bata bugawa da kyau. Yaushe ya shigo gidan har ya shiga ɗakin bata ji ƙarar buɗe get ko dirin motarsa ba? Ta san dai dama a buɗe ta bar ƙofar falon dalili kuma saboda tana jiransa dan tayi duk yanda zatayi jarabar dake cinta taƙi ta kwanta, yana fita kuma ta koma ɗakinsa ta bincike tsaf amma bata gano abinda ya ɗauke mata ba dan tun ranar data dawo taga an gyara ɗakin tana dubawa bata ga abun ba ta san shi ya ɗauke su kuma tun ranar ta cewa Suby ta sake siyo mata wani amma wai ya ƙare a gurin matar sai an sake kawowa tayi baƙin ciki matuƙa dan ta lura ba zata taɓa samun haɗin kansa yanda take buƙata ba idan bada abun ba sai dai kawai ya jagwalgwalata ya barta da wahala.
Yanzun ma rasa yanda zatayi ya saka ta kira Ahlan ɗin da kanta, a falo suka fara wayar tsoron kada ya shigo ya saka ta dawo ɗaki sai gashi tayi gudun gara ta tarar da zago. Sunanta daya sake kira da takunsa da taji alamar yana matsawa kusada gadon ga Ahlan da shima yake ta Hello Hello jin tayi shiru, lokaci ɗaya ƙwaƙwalwarta ta kawo mata mafita cikin abinda bai wuce seconds biyar ba ta aiwatar, ta latse wayar ta kasheta gaba ɗaya kafin ta turata tsakanin kan gadon da katifa tayi juyi kamar a cikin barci ta cigaba da sakin maganganun da suka fi wanda ya fara ji girma.
Tsayawa yayi yana cigaba da kallonta a hankali kuma harzuƙa da fushin da ya taso masa lokaci ɗaya suka fara sauka kafin ya ya matsa ya shiga buga ƙafarta yana kiran sunanta amma kamar wacce yake zugawa sai ma wani motsi data farayi kamar wacce take tareda Namiji. Duka mai zafi ya ɗana mata a cinya, taji dukan har ƙwaƙwalwarta ba shiri ta wartsake ta tashi zaune zumbur tana sosa gurin idanuwanta suka kawo ƙwalla, Bilal dake tsaye a kanta ya ce
"Menene haka kike yi?"
"Kai zan tambaya akan me kawai ina bacci na zaka zo ɗana mun duka irin haka?" Ta faɗa yaye rigarta gurin daya doke ta ɗin, gefe ya ɗauke kansa dan har pant ɗinta sai da ya fito saboda janye rigar da tayi ya ce
"Bakiyi addu'a ba da zaki kwanta baccin sai wasu sambatu kikeyi marasa kan gado ga ƙofofi kin bari a buɗe kuma ko ina shara" ya nufi ƙofa. Ajiyar zuciya ta sauke a fili kafin ta bi shi da harara haɗi da yin ƙaramin tsaki ta koma ta kwanta tana shafa in da ya doketa. Yanzu da ace ya gane mai takeyi yau ina zata saka kanta? Gaskiya dole fa ta ringa takatsantsan kar taje kwaɓarta tayi ruwa tun ba'a je ko ina ba.
Tashi tayi tabi bayansa jin yana harhaɗa ledoji da kwalayen da suke falon, a nan ɗakinta ya kwana; tun kuma yanayin na son rai har dai yaga ita bata da geji ya tashi ya koma falo bayan yayi wanka ya barta tana tsaki bai kuma san yanda ta ƙare ba bacci ya kwashe shi.
Washe gari da wuri ya fita saboda tunanin daya kwana dashi a ransa, store ɗin da suka ajiye kaya yaje bai kuma ɓata lokaci ba dan a gurin ya tarar da wanda zai karɓi kayan ya buɗe suka ɗiba babu bata lokaci kuma suka tura masa da kuɗinsa cis yanda sukayi ciniki. Jin kuɗaɗe masu nauyi a account ɗin sa ya saka nutsuwa ta saukar masa duk wasu tunani da zullumi da yake fama dasu a kwanakin suka kama gabansu ya shiga sharholiyarsa, 1M ya bawa Fadila gudummawa wanda daƙyar Hajja ta karɓa tana zaginsa tana faɗar maganganu amma ya toshe kunnensa sauƙin daya samu gyaran daya tayar ayi mata kafin bikin Fadila nan da kwana goma da angon da kowa bai sani ba daga ita sai Hajja da Anty Habiba sai Anty Ladidi su suke shirin biki dan ko Abubakar da yake kwana a gidan ya ce bai san komai ba balle sauran.
HALIMA
Da wuri na tashi daga aiki ranar Alhamis, ƙarfe tara nake zuwa mu tashi ƙarfe biyu amma yau ɗin saboda monthly clearance da zanje ya saka na tashi karfe 12. Ina tsaka da wanke hannuna bayan na fito daga banɗaki, Juwairiyya wacce muke service a gurin tare ta shigo ta kalleni ganin na cire lab coat ɗina ta ce
"Ba dai guduwa zakiyi ba Halima?"
"Guduwa kuma sai kace wata ke?" Na bata amsa cikin raha tayi murmushi tace
"Ai da alama yau zaki zama ni ɗin sai dai kinyi wrong timing dan yanzu Dr Sa'id ya shiga lab ɗin mu ya ce kowa ya zama cikin shiri CEO yana hanya".
Ido na zare jin abinda ta faɗa na ce
"Kuma ya rasa ranar da zai zo sai yau da nake da uzuri? Tun fa last week aka ce zai zo?" Tana gyara fuskarta da powder ta ce
"Ai kuwa dai sai yau kuma wlh har waɗanda basu da duty yau gashi can Dr Sa'id yace a kirasu a waya duk kuma wanda bai zo ba ya ce babu ruwansa dan haka kiyi haƙuri kawai ki jira na san ba jimawa zaiyi ba".
Kamar zanyi kuka haka na koma office na zauna, tun last week aka ce zai zo Dr Sa'id kuma ya jaddada har ranakun da bamu da duty mu kasance cikin shiri za'a iya cewa mu fito saboda yace yana so ya gana da duka staffs ne idan ya zo. Ina duba agogo ina zabga tsaki, mutumin da aka ce an ɗakko daga Airport tun 12 gashi har ɗaya ta gota basu iso ba ko dai dama basu taso daga can Abujar bane lokacin da aka tafi ɗakko shin sai Allah. Da wannan mitar na tashi nayo alwalawa ganin zaman ba zai fissheni ba nayi sallah, ina addu'a Dr Sulaiman ya shigo office ɗin yana ganina ya ce na fito da sauri dan haka na shafa na miƙe shaf na manta ban mayar da Lab coat ɗin ba na fita da Abayar dana saka nayi sallah.
A reception na tarar da duka staffs harda cleaners anyi layi na tafi inda naga sa'annina da alama tsayuwar matsayi aka bi, yanda kasan waɗanda zasu tari wani Gwamna ko Shugaban ƙasa haka muka nutsu muna kallon ƙofa kusan minti uku kafin suka shigo, Dr Sa'id ne a gaba sai wasu mutum biyu da ban sansu ba da alama tare suka zo da CEO ɗin sai kuma shi Dr SALMAN ABDULLAHI AGI da wasu mutum biyun a bayan sa, ɗaya daga gani PA ɗin sa ne sai kuma ɗayan da yayi kama da security.
Fuska ba yabo ba fallasa ya ringa kallonmu suna tayi masa sannu da zuwa banda ni dana zuba masa ido ina ƙare masa kallo kamar mai neman wani abu a jikinsa. Duk yawan shekarunsa ba zasu kai 40 ba yanzun ne na sake tabbatar da haka dana ganshi a zahiri. Dogo ne sosai dan har ranƙwafawa yayi, a kallo ɗaya kuma dukda suit ce a jikinsa zaka fahimci yana da kirar ƙarfi irinta masu ɗaga ƙarfe.
Bashi da wani shahararren kyau kuma baƙi ne mai ƙananan ido amma akwai wani abu a tattare da idanuwansa da bai zai barka kayi masa kallo ɗaya ba tareda ka ƙara ba, gayu da iya ɗaukar wanka ya saka ya ƙaƙalo kyawun a dole amma ba dan asalinsa mai kyau ɗin bane irin su Bilal da aka haife su da kyan su, amma maganar gaskiya a ture duk wani ƙaƙale-ƙaƙale, Dr Salman ya haɗu; ga kuma tarin ilimi abin ba'a cewa komai.
Yanda nake kallonsa shima haka ya tsayar da idonsa a kaina sanda ya kallo ɓangarenmu, naga sanda laɓɓansa suka motsa alamar magana yayi amma kunnuwana basu jiye mun sautin mai ya faɗa ba ganin kuma mun haɗa ido ya saka nayi saurin sadda kaina ƙasa ina jin haushin irin kallon ƙurillar daya kamani ina yi masa. Juwairiyya ta zungureni na kalleta da son jin ƙarin bayani, da ido ta nuna mun CEO ɗin da har sannan ashe ni yake kallo na zare masa ido cikin rashin fahimtar dalilin kallon da yake yi mun.
"Tambaya yayi wai baƙuwa akayi?" Juwairiyya ta raɗa mun a kunne, still ban fahimci kan zancen ba sai da Dr Sulaiman ya ce
"Sallah tayi garin sauri kuma ta manta ta fito a haka". Sai lokacin na lura ashe ni kaɗai ce a gurin babu lab coat a jikina cikin yan Lab, nayi ƙasa da kai ina kallon takalman ƙafarsa kafin na ɗaga kai a hankali jin yana cewa kowa ya gabatar da kansa. Sai kace za'a gudu ba zai bari aje a zauna ba tukunna. Da ɗai-ɗaki kowa ya ringa gabatar da kansa da kuma position ɗin sa har aka zo kan coppers mune kuma ƙarshe, Juwairiyya dake kusa da ni tayi tana gamawa na buɗe baki zan fara magana wayarsa tayi ƙara sai ya ɗaga mun hannu alamar na dakata ya karɓi wayar daga hannun PA ya amsa kafin ya fara tafiya suka shige Elevator shida muƙarrabansa suka barmu a tsaye musammani, ni ce fa kaɗai na rage banyi introducing kaina ba maimakon ya bari nayi sai su wuce gaba ɗaya yanzu ko mai yake nufi sai Allah, zamu tsaya ne yaje ya dawo ko kuwa shikenan taron ya watse? Wai dama iya dalilin daya saka aka tsayar damu kenan ko da saura?
Dr Sa'id ne ya dawo ya ce zamu iya tafiya wai amma gobe kowa ƙarfe takwas tayi masa a gurin za'ayi meeting. Haka muka fita ina mita ga rana ta take babu lallai kuma na tarar da masu clearance ɗin suma tunda ƙarfe biyu ta rigada tayi amma haka nan na biya tunda idan na ce na bari gobe Friday kuma ban san sai ƙarfe nawa zai sake mu ba. Da haushin rashin samun clearance ɗin na wuce gida dan munyi waya da Anty Labiba tace mun suna gidan Mama.
Ban san ɗaya matar da muka hau Adaidaita tare cikin unguwa za'a shigar da ita ba tunda tace Sabon titi kawai na ɗauka a bakin hanya zata sauka ni kuma ya wuce dani sai da muka je naga yana ƙoƙarin shiga layin Gidan Ƙanƙara layin su Bilal kafin nayi masa magana.
"Ba ciki sosai bane Hajiya kuma kan hanya ne inda zata sauka sai mu fita ta baya Hajiya" mai Adaidaitan ya bani amsa. Ƙoƙarin mayar da kaina kan wayata da nake dannawa nayi amma na kasa sai na zurata cikin jaka na shiga kallon hanya ina tuna zuwana gurin na ƙarshe ranar da muka zo duba Hajja bayan mun dawo daga gidansu Duniyarsa.
A kan layinsu Bilal ya tsaya, na leƙa ina hango ƙofar gidansu daya sha sabon fenti ga mata suna ta shige da fice kamar ana wata hidima a gidan,
"Ko mai akeyi sai Allah" na faɗa a fili kafin na ɗauke kai na koma kallon mai Adaidaitan dake irgawa matar data sauka canji.
"Gadon ƙaya" muryarsa ta sauka a kunnena tamkar dirar aradu kafin ƙamshin turarensa da tunda na sanshi bai taɓa canzashi ba ya mamaye iskar da take yawo yawo a gurin, na ɗago; har ya zauna a gefena. Dukda na razana da ganinsa amma ban bayyanar da hakan a kan fuskata ba sai na mayar da hankali na kan mai Adaidaitan na ce
"Malam drop fa na ɗauke ka, itama saboda naga hanya ɗaya zamuyi kuma abin hawan yana wahala shiyasa na bari ka ɗauketa"
"Kiyi haƙuri Hajiya, Malam yi haƙuri ka sauka ba can zamuyi ba" mai Adaidaitan ya faɗa, sai lokacin Bilal ya kalleni idan kuma nayi rantsuwa na san ba zanyi kaffara ba tsabar wulaƙanci ne ƙarya yakeyi ya ce bai san ni bace a ciki sai a lokacin.
"Halima" ya faɗa muryarsa da idanuwansa suna bayyanar da mamaki, na ɗauke kai a raina ina cewa
"Ƙaryar banza wlh ka san ni ce" kafin kuma na saita fuskata na kalle shi da irin yanayinsa na ce
"Au Bilal, kai ne?"
"Kun san juna ma ashe? Toh mu ɗauke shi ko zai sauka?" Mai Adaidaita dake kallonmu ta cikin mudubi ya faɗa, shiru nayi dan har ga Allah ƙarfin hali kawai nakeyi sai Bilal ɗin ne ya ce masa
"Bari sai na sauka a titi tunda ciki zaku shiga" ya tayar da mashin ya juya sai lokacin na ƙaƙalo murmushi ganin yana kallona na ce
"Ya su Hajja?"
"Amma baki faɗa mun zaki ringa fita wani guri ba, ko kin manta har yanzu ina da iko akanki tunda kina cikin iddatah?" Ya faɗa yana kallona cikin sauti mai kama da raɗa dan nima ba dan shi nake kallo ba bai zama lallai na ji abinda ya faɗa ɗin ba. Na saki murmushin irin na tura takaici wanda ni kaina ban san na iya ba kafin nima na sauke murya yanda yayi na ce
"Da alama amarci ya sa ka faa manta lissafi, ko dai in saka ayi maka babbar calendar da zaka ringa duba watanni da ranaku saboda gudun manta abubuwa masu muhimmanci irin haka?"
"I'm serious Halima, 28th of this month ya kamata ki fara cycle ɗin ki na uku" ya sake faɗa, ganin mum kawo kan titi mai Adaidaitan na neman cigaba da tafiya ya saka nace masa
"Ya sauka a nan" sai ya dakata, na kalli Bilal da shima ni yake kallo kafin na ce
"An zo titi Malam", kallona yakeyi kamar wanda yaga wata halitta ta daban dan haka na kaɗa yatsuna akan fuskarsa ina sake maimaita masa cewar an zo titi,
"Ki fara shiri, na mayar dake ɗakin ki" ya faɗa yana sauka daga Adaidaitan, bansan lokacin dana fashe da dariyar da har mai siyar da ƙanƙara a inda kuka tsaya da mutanen dake gurin saida suka kallemu ba, da hannu na nuna kaina ina cewa
"Da alama kayi hauka ko?"
Ya miƙawa mai Adaidaitan gudar dubu ɗaya yana cewa
"Za'a ga wanda yake hauka tsakanin ni da ke" ya wuce ya tsayar da wani Adaidaitan ba tareda ya tsaya karɓar canjinsa ba, abun nasa yayi bala'in bani dariya; lallai bansan Bilal mahaukaci bane sai yanzu. Wato shi yana can yana mun lissafin Iddah kenan? To da bai haɗu dani ba yanzu wa zai aikowa da saƙon ya mayar dani ɗin?
Ni kaɗai na ringa dariya mai Adaidaita dai sai satar kallona yakeyi da alama magana ce fal bakinsa amma ya kasa furtawa har ya saukeni ƙofar gida nayi wucewara tunda Bilal ya biya mun, lallai yau kam za'ayi ruwan sama harda ƙanƙara Bilal ya biya mun kuɗin mota.
❤️ *ƊANLARABAWA INVESTMENT! Kyau Da Ƙima A Hannunku!* ❤️
*Ku sauka lafiya zuwa masarautar ƙayatarwa!* 👑
*ƊANLARABAWA INVESTMENT* na kawo muku:
*Atamfofi masu kyau na zamani*
*Shaddodi da Laces masu ɗaukar ido*
*Takalma & Jakunkuna masu ladabi da ƙima*
*Hijabai, mayafai da dogwayen riguna masu salon zamani*
*Yari da sarƙa da kayan ado masu ban sha’awa*
*Akwatuna masu kyau don tafiya ko haɗa lefe*
*Turaruka masu ƙamshi da kayan kwalliya na garari*
*Nau'in kayan kicin na alfarma da kayan ɗaki*
*Zannuwan gado da labulaye na kashe kala*
*Da dai sauran su*
*Muna tura kayanmu ko'ina a fadin Nijeriya da ƙasashen ƙetare. Cikin mutuntaka da cika alƙawari in sha Allah*
*Location: Kano, Ƙofar Waika, Layin Malam Sani Shawus.*
*Lambar waya domin tuntuɓa*: 08080049548
*Ko ku shiga zaurenmu na manhajar WatsApp ta wannan link kamar haka:*
https://chat.whatsapp.com/Loht5sGuLJO3LXYE9OkqNs
*Za ku more da kallon kayayyaki na ƙawa bisa ingantaccen farashi da rahusa mai kama da kyauta. Sayen nagari, mayar da kuɗi gida.*
*KURA A RUMBU*
*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*
*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya naira 800, biya a asusun*
*7061838488*
*Opay*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*
*PAGE 57*
BILAL
Yana kwance a gida Hajja ta kirashi wai ya kawo musu kayan miyan da za'ayi tuwon ɗaurin auren Fadila da za'a ɗaura a gobe Juma'a. Da yake a tsini suke yayi mata laifi shiyasa bai musa ba ya tashi ya tafi kasuwar Yankaba ya yiwo musu cefanen ya tafi ya kai. Zagayewa yayi yaje ya samu Kawu Ɗayyabu, Yayan Hajja ne da suke uba ɗaya da yake mutum ne mara ɗaukar raini shiyasa duk rashin mutunchin Hajjan take shakkarsa ko da wasa kuma bata bari wani abu ya gilma a tsakaninsu shi Bilal ɗin yaje ya samu ya gaya masa zancen auren Fadilan da yanda ita da Hajja suke shirya komai basu saka kowa a ciki ba.
Kawu Ɗayyabun ya ringa faɗa