Showing 153001 words to 156000 words out of 257873 words

Chapter 52 - KURA A RUMBU HAUSA NOVEL

23 Oct 2025

492

tambayar ko Halima ta dawo shiyasa ko za'a fasa ƙofar saboda bugu yana ciki ba zai taɓa amsawa ba balle ya buɗe. Shi yanzu ko mazan layin ma ba duka yake gaisawa dasu ba, sai kace akansa aka fara samun saɓani da mace har tayi yaji kowa da dogon bakinsa sai ya tare shi yace zai masa faɗa wai bai kyauta ba ganin suna nema su raina masa wayau ya saka ya dena tsayawa idan zai fita a mota glass ɗin sa a sama haka idan ya dawo in kuwa tafiyar ƙafa ce ko zuwa masallaci nan ma zai haɗe fuska ta yanda ko ka masa magana zaiyi kamar bai ji ba ya share.

Yau ɗin ma sai da akayi magriba kafin yayi wanka ya shirya cikin wata sabuwar shadda yayi kyau sosai kuwa ya hau mota ya fito. Jin sa yake kamar wani sabon mutum musamman daya kunna wayar sa saƙon Kawu Sani ya shigo yana sanar masa an ɗaura aure idan ya kunna wayarsa kuma ya kira shi ko kuma yaje gida ya same shi, itama Zulaihan ta yiwo masa text mai nuna zallar farin cikin ganin wannan rana a rayuwarta da kuma ƙorafin rashin halartarsa gurin ɗaurin auren.

Gidan Kawu Sanin ya fara zuwa, a waje suka haɗu zai tafi sallar isha'i dan haka suka wuce masallacin tare sai bayan da aka idar kafin suka keɓe Kawu Sani na kallon sa yace
"Munje an ɗauro aure amma fa wannan Kawun nata yaso ya mana hauka wai sai mu jira mu taho da ita su ba za'a bar musu ya a gida ba bayan an ɗaura mata aure".

Ido ya buɗe da mamaki kafin ya ce
"Sai kuka ce masa me Kawu?"
"Mai zamu ce masa kuwa? Muma buɗe masa ido mukayi tunda munga abinda yafi ganewa kenan dan waliyyin ɗaya yaron ma cewa yayi sai a warware auren tunda abun nasa ya zama da iya shege a ciki idan yaso in an shirya gaba ɗaya sai a dawo ayi". Bilal ya shafa kai yana murmushi Kawu Sani ya cigaba da cewa

"Ni wlh duk sai jiki na yayi sanyi da al'amarin, anya kuwa ba gidan ƙananan mutane ka nemo auren nan ba Bilal?"
"Shi ɗin shine me matsala Kawu dan baka san irin wahalar da suke sha a hannun sa bane wlh mutumin bashi da kirki amma mahaifinsu ai kace k sanshi mutumin kirki ne haka mahaifiyar su ita kanta yarinyar na gaya maka munfi shekara goma tare tun tana yar yarinya dan haka halayyarta babu wacce ban sani ba babu wata matsala wlh" Bilal yayi saurin faɗa, Kawu Sani ya gyaɗa kai ya ce
"Toh Allah ya tabbatar da Alkhairi ya sa anyi a sa'a, gobe idan Allah ya kaimu zanjw in samu Hajjan in mata bayani".
Sosai yayi masa godiya kafin ya cika shi da kuɗaɗe sukayi sallama ya wuce yana jin farin ciki na ratsa shi ta ko ina.

Gidan su Zulaihan ya wuce dan bashi da wani buri kuma a yanzu illah ganin fuskarta kuma a matsayin matarsa. A kan kwana sukayi clashing da Alhaji Saleh da Anty Labiba, fes ya gansu kamar yanda suma suka ganshi sai da yaji kamar yayi reverse ko yayi layar zana ya ɓace ɓat kawai daga gurin. Tun da suka dawo unguwar duk ranar da zaizo gurin Zulaihan tunda aka tashi hanyar da ake shigowa ta can baya sai yayi doguwar Addu'ar Allah ya saɓa haɗuwar sa da duk wani wanda ya sanshi a unguwar kuma yana cin sa'a addu'ar sa tana karɓuwa dan sau ɗaya ya taɓa haɗuwa da Alhaji Salen har suka gaisa a lokacin ya ce masa gurin wani abokinsa ya zo can ƙasansu bai kuma damu ba dan ya san ba lallai ma ya ce mata ya ganshi ita ɗin ma sau ɗaya ya taɓa hangen motar ta lokacin ma da mashin yake zuwa ya kuma gota gidan sosai ya waigo ya hango ta fito ya san kuma bata ganshi ba amma a yau ɗin sai yake jin kamar duk wanda ya kalle shi zai gane abinda yake faruwa.

Haka yaja mota jiki ba ƙwari ya wuce yana hangensu ta mirror, ita kuwa yi tayi tamkar ma bata ganshi ba har sai da Alhaji Saleh yace mata
"Kamar Bilal ne ya wuce a waccen motar ko?"
Ta ɗan juya ta kallo bayan motar tace
"An ya kuwa? Bilal ai bashi da mota".
"Ina ganin sa jefi jefi a wannan motar, a nan ɗin ma mun taɓa gaisawa sau ɗaya yace gidansu wani abokinsa yazo can ƙasa". Cikin rashin mayar da hankali tana danna waya ta ce
"Allah sarki".

Bilal kuwa ganin Zulaiha ya mantar dashi haɗuwar su dasu Anty Labiba. Sun daɗe a mota suna hira cikin shauƙi dan basu farga da lokaci ba har sai da Ummansu ta turo Nuratu ta buga musu glass lokacin sha ɗaya har da rabi da wasu mintuna kafin ta wuce ta barshi yana ƙoƙarin saita nutsuwarsa kafin ya tayar da motar ya wuce gida. A hanya yana tafe shi kaɗai yana tunani, so yake ya kori waswasin da shaiɗan yake ƙoƙarin cusa masa amma kuma tunanin yana nema yafi ƙarfin sa.

Bai tsammaci yanda Zulaihan ta sake dashi a tashin farko da irin haɗin kan da ta bashi ba. Sai ya tuna irin wannan haɗuwar tasu ta farko da Halima, yanda ta ringa rawar jiki a lokacin har ƙarar bugun zuciyarta ya ringa ji numfashinta yayi ɗumi baka buƙatar a faɗa maka a matuƙar tsorace take lokacin. Sun fi ƙarfin wata shida kafin ta fara gane kan harkoki sosai dan ko kiss bata iya ba shi ya koya mata fara tarayyarsa da Jalilah kuma ya sake fayyace masa tsakanin macen da ta saba da maza da yawa da kuma wacce namiji ɗaya ta sani, akwai banbanci sosai domin duk ƙwarewar matar aure ba zata kamo ƙafar macen bariki ba.

Guri ya samu yayi parking abubuwan da suka gabata suka fara dawo masa daki daki. Ita ta fara kawo hannu jikin sa, shi bai ma yi niyyar yi mata wani abu ba a yanzu ba bayan riƙe hannunta amma ta ringa shige masa ƙila da bai kama kansa bama ya biye mata da a motar zasuyi mai gaba ɗayan. Ji yayi zufa ta fara tsattsafo masa duk da sanyin AC da ta cika motar, can wani ɓangare na zuciyarsa ya ayyana masa ba abinda yake zato bane Zulaiha ba zata taɓa zama irin waɗannan matan ba. Ya santa tun ƙuruciya ya kuma yarda da tarbiyyarta hakan ba zai taɓa kasancewa halinta ba. Da wannan tunanin ya ringa tausar kansa har ya samu nutsuwa duk da ba wai tunanin ya barshi gaba ɗaya bane ya kasa cire kokonton gaba ɗaya amma ganin idan ya bari shaiɗan yayi galaba akansa ya saka masa wasi wasi na banza wanda ba gaskiya ba dole ya kore komai ya tada mota yaci gaba da tafiya.
[5/19, 22:05] Buhainat: *KURA A RUMBU*

*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*

*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya naira 800, biya a asusun*
*1840175439*
*Access bank*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*

*PAGE 39*
Ko da ya koma gida daƙyar tunanin yanda Hajja zata karɓi zancen auren daya ɗaura ba tareda saninta ba ya danne waswasin da zuciyarsa ta dasa masa akan Zulaiha. Wayarsa ma kashewa ya sakeyi bayan daya shiga gida bai kuma kunnata ba sai washe gari gurin ƙarfe goma bayan daya shirya zuwa gidan Hajjan in da daga can kuma yake so ya biya gurin Halima. A tsakar gida ya tarar da Hajja tareda Fadila suna duba kayan da kallo ɗaya ya musu ya fahimci daga gurin Jalilah suka fito dan yanzu ta lalata Hajjan da suturu masu tsada. Yana shiga kuwa ta ɗago baki washe tana amsa masa sallama ta ce

"Kinga ɗan halak, yanzu muka gama zancenka ashe ma kana tafe". Kan kujerar tsuguno ya zauna yana gaisheta ta amsa cikin murna ta tura masa kayan tana cewa
"Ka ga abin arziƙin da yarinyar nan ta aiko da safen nan tayowa Fadila waya tace aje tasha a karɓo saƙo, ni har na rasa ma abinda zance gaskiya uwayen yarinyar nan sunyi sa'ar haihuwa kai dai Allah ya cigaba da haɓaka arziƙin kawai" ta ƙarasa tana ɗaga wani ɗanɗasheshen leshi da kana gani kasan an kashe kuɗi gurin siyan sa. Fadila ce ta fizge shi daga hannunta tana cewa

"Ni zan ɗinka wannan Hajja" sai ko ta maka mata harara tace
"Tunda ubanki ya bani ai sai ki ɗinki ko kuwa an rubuto sunanki a jiki? Ai na gaya miki na gaji da shuka dusa wlh, duk wata suturar arziƙi da ake kawowa ke kike ɗinkewa ki gama zaga garin ki dawo amma ko kare baze biyoki da sunan yana sonki ba" ta juya kan Bilal tace
"Kaima na rasa baƙin ciki ne ko menene ya saka nayi nayi ka tallatawa yaron nan Hafizu ita ai ba ƙi zaiyi ba amma ka ƙi, to wlh na fara gajiya da ganinki a gabana in sabon yaƙi samuwa sai ki nemo Sani ku sulhunta ki koma tunda dama ai ke kika ce sai ya sakeki ba wai son ransa bane".

Fadila ta miƙe tana zumɓuta baki ta wuce ɗaki tana cewa
"Allah ya rufa asiri ai ba jaka bace ni da zan maimaita aji". Shi dai Bilal bai ce komai ba Hajja taci gaba da ɗaga kayanta tana santi ta kimanta kuɗinsu, can ya nisa ya ce
"Hajja Kawu Sani ya zo kuwa?"

"Bai zo ba, ya dai kira ɗazu yace yau zai zo akwai maganar da yake so muyi. Ni dai na faɗa masa idan ma kuɗi zai roƙa babu dan dama nasan yanzu tunda akaga taurarinka sun fara haskawa Allah ya rufa mana asiri kuma za'ayo mana rubdugu to babu wannan maganar kuwa" ta bashi amsa. Sai ya shafa kansa ya ce

"Nasan ma ba zancen kuɗi bane ai kin san Kawu Sani bashida wannan halin"
"Lallai kai zaka gayamun halin Sani ashe, to idan ba maula zata kawo shi ba menene? Naga dai zancen tambayo aure ance sai nan da wata biyu to kuma me ze kawo shi?"

"Idan ya zo ɗin dai ai zakiji koma menene" ya bata amsa yana miƙewa, sai ta aje atamfar hannunta tana kallon sa tace
"To ko kasan dalilin zuwan nasa ne?" Da sauri ya girgiza kai ya ce

"Aa, kawai mun haɗu masallaci ne jiya yace mun yau zai zo nan gidan". Kuri ta masa da ido tana kallonsa kamar me son gano gaskiyar zancen sa kafin tace

"Da ganinka baka da gaskiya, to dan kaji da kunnenka idan ma zancen waccen yarinyar zaka turo shi ya mun kar ma ya ɓata lokacinsa dan zama kam kun gama gara ma ka bata takardarta tun da mutunchi".

Komawa yayi ya zauna yana fuskantar ta ya ce
"Amma Hajja wai mai yasa kike so sai ma rabu da Halima ne? Ni fa ba tayi mun komai ba hasalima ni na mata laifin da ya saka tayi fushi har ta tafi gidan sai kuma kawai in bita da tukuicin saki ai hakan ba adalci bane ba". Kamar bata ji shi ba ta shiga tattare kayanta tana mayar wa cikin leda, ya sake kwantar da murya yace

"To yanzu idan kika saka na saketa ya zanyi na zauna har wata biyu babu mata?"

Da sauri ta kalle shi kafin ta sauke kai tana sake tamke fuska tace
"Kai bana son iskanci da ɗiban albarka fa". Gyara zama yayi ganin kamar zai samu kanta ya ce

"Wlh ko yanzu da zan fito sai da maƙwafcina na jikin gidana ya tareni yana mun magana amma kinga ai ba zance mahaifiya ta bace tace kar na dawo da ita".

"Saboda dama ni nace ka koreta ko ya akayi da zaka sakani a bakin duniya?" Ta katse shi, sai ya marairaice ya ce
"Yanzu dai kiyi haƙuri Hajja ta dawo, ni da nake tunanin ma in ƙara wata kafin wata biyun ta cika sai in kulle ƙofa da Jalilah yar gaban goshin ki". Kallon baka da hankali tayi masa kafin tace

"Saboda ka zama namamajo ko baka da wani lissafi a rayuwarka sai na aure? To ban yarda ba kuma bada yawuna ba Halima dai ko da kaca aka ɗaura aurenku sai ka datse ka sallameta can Allah ya haɗa kowa da rabon sa abinda akayi a baya ma ya isa Allah ya sa albarka".

"To yanzu idan na saketa zaki barni in auri wata kenan?" Ya faɗa cikin ɗar ɗar, ta balla masa harara kafin ta miƙe ta shige ɗaki ta barshi a zaune. Jiki babu laka ya fita daga gidan suka ci karo da Abubakar dakw shirin shigowa, kallo ɗaya Abubakar ɗin ya masa tamkar bai ganshi ba ya wuce ciki sai Bilal ɗin ne ya dakatar dashi yana cewa

"Kai baka ganni bane? Yaushe kuka fito daga camp ɗin?" (Aikin custom ya samu sunje training). Cikin ko in kula yace masa
"Na ganka mana, jiya na dawo" ya shige gida. Sai ya bishi da kallon mamaki domin ko da wasa magana mai shige da raini bata taɓa haɗa shi da ƙanin nasa ba balle ya masa irin haka, to menene dalili?

A jikin motar sa ya tsaya duk ya rasa ina ya kamata ya dosa, ya kamata ya leƙa office ɗin su dan an tura masa da query akan rashin zuwansa aiki dukda ya ɗauki leave amma hutun ya ƙare tuni kuma bai koma ba haka nan bai tura saƙo abinda ya sa bai wani damu yanzu da aikin ba saboda harkokin da ya kama yana ganin in ya cigaba sun isa su riƙe shi dama jira kawai yake shagon da Jalilah take shirin buɗewa a nan Kano ya tabbata zai yi resigning saboda harkar fita waje da zai ringayi na shigo musu da kaya.

Wayar sa ce tayi ƙara ya zarota daga Aljihu, sai da gabansa ya faɗi ganin Hafiz ne yake kira a ƙalla kusan sati uku kenan rabon da suyi waya balle su haɗu. Kamar kar ya amsa sai kuma dai ya ɗaga. Daga can Hafiz ya ce

"Ranka ya daɗe yau na ci sa'a waya ta shiga an amsa kenan?"
"Tuba nakeyi yallaɓai wlh tafiya ce ta sameni ba shiri mun tafi da Hajja can yakin Nijar gurin wani mai magani jiya muka dawo dama yanzu ka ganni nake shirin fitowa zan kiraka naji gida zanzo ko office sai kuma ga kiranka" ya shato ƙaryar da shi kansa sai da ya jinjinawa kansa. Cike da Jimami Hafiz ɗin ya ce

"Jikin ne har yanzu kuma? Amma me ya sa maimakon a mayar da ita Asibiti zaku tafi kuma gurin wani mai maganin gargajiya?"
"Ai ka santa ko kwanciyar da tayi a Asibitin da yaya? Ai dan an fi ƙarfinta ne ita dai tafi ganewa masu maganin gargajiya shiyasa ma na bita ɗin gudun kar a samu wata matsala kuma Alhamdulillah gashi jiki yayi kyau ta warware harma ta aje sanda yanzu tana taka ƙafar lafiya lau" ya sake rattabo wata ƙaryar har zufa ce ta tsattsafo masa yana yi kuma yana zare ido haɗi da duban gefensa ko da wani a kusa yana sauraronsa.

Hafiz ya ce
"Toh masha Allah Allah ya ƙara lafiya ya tsare gaba in sha Allahu zan shigo sai na dubata, ashe shi yasa Madam ta koma gida ni duk Suhaila ta tayar mun da hankali wai taje ta ganta a wani irin yanayi jiya kai kuma gashi ina ta kiran layinka bana samu". Da sauri ya ce

"Taje gurin Halima? Me tace mata toh?"
"Babu abinda ta gaya mata ko akwai wata damuwa ne naji yanayinka ya canza?" Cewar Hafiz, sai yayi saurin daidaita nutsuwarsa ya ce
"Babu komai naji kace ta ganta cikin wani hali ne ni kuma bata ce mun bata da lafiya ba amma bari yanzu in je gidan in ganta kawai hankalina zai fi kwanciya" kafin Hafiz ya sake magana ya katse wayar. Mota ya shiga ya kunna haɗi da kunna Ac dan zafi yakeji kamar wanda yayi gudu dukda garin akwai iska sosai tana kaɗawa.

Yanzu da gaske Halima bata gayawa Suhaila komai ba ko kuwa dai kawai rufe masa yayi yake so ya bigi cikinsa? Wayarsa tayi ƙara alamar shigowar saƙo ya duba Hafiz ɗin ne ya turo masa saƙo yana cewa
"Ka samu ka shigo office dan za'a iya samun matsala gaskiya" ganin saƙon ya saka ya tayar da mota ya kama hanyar office ɗin a ransa kuma yana ayyana daga can gidan su Halima zai biya. Sau biyu Zulaiha ta kirashi yana hanya amma bai amsa ba dan yana ganin sunanta maimakon yaji farin ciki irin yanda ya saba sai kawai tunanin jiya ya faɗo masa daga ƙarshe ya kife wayar bayan ya sakata a silent ya cigaba da kokawa da tunanin da ke neman ɓata masa yanayi.

HALIMA

Ina kwance rigingine akan gado ina amsa wayar Hansa'u, na gyara kwanciyata ina sauraronta tana cewa

"Kusan sati huɗu fa kenan ace babu waya babu zuwa balle aike kuma wani nasa bai biyo sahu ba iya wannan ai ya isa ya shaida miki amsarsa akanki Halima". Ajiyar numfashi nayi kafin nace

"Da wahala idan yan uwansa sun san abinda ya faru tunda dama ba wai zuwar mun sukeyi yanzu ba balle su san bana gidan, shi kuma nake ganin harda kunya ta hana ya zo"

"Ashe har yanzu akwai sauran uzurin da zaki masa Halima? Gaskiya da sauranki, duk abinda ya faru ace kin cigaba da kare shi to gaskiya ban kuma ga wani abu da zai buɗe miki ido ki kalli gaskiya a yanda take ba kuma ɓata yawun baki na kawai nakeyi da lokaci na ina miki magana shiga suke ta kunnen dama su fice ta hagu" Hansa'u ta faɗa cikin ƙunar rai, nayi murmushi na ce

"Haba y zakice haka? Ai wlh duk wata shawara da kike bani na ɗauka kuma ina ganin amfaninsu, kawai na faɗa miki nawa tunanin ne na wai lallai hakan bane ba".

"Dole kuwa ki canza tunani ko in ce ki bawa ƙwaƙwalwarki da zuciyarki dama su ringa tunanin daya dace ba wai iya abinda kike so suyi tunani a

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login