Showing 237001 words to 240000 words out of 257873 words

Chapter 80 - KURA A RUMBU HAUSA NOVEL

23 Oct 2025

486

ina sake nanata karanta saƙon,
"Ni da kika ganni ina tarayya ne da mutanen dana san zasu mun amfani a rayuwa, da zarar amfanin mutum ya ƙare kuma zan ajiye shi dan ni bana son liability" maganganunsa na wani lokaci suka shiga dawo mun. A fili na furta

"Tabbas na shaida hakan, ya watsar dani a lokacin da yake ganin amfanina ya ƙare a gurinsa ashe kuma da saura". Blocking ɗin number na sakeyi dan dama nayi ban san dalilin daya saka na buɗe daga baya ba. Da naga tunanin yana neman ya hanani sukuni sai na ɗakko system ɗina na tura research proposal ɗin da Dr Sulaiman ya tura mun akan idan ina sha'awa na shiga ayi dani. Wannan ya ɗauke mun hankali har zuwa sanda na gaji na kwanta bacci.

BILAL
A tunaninsa ɓatan dabon da yayi shine mafita, Minjibir shine in da yake ganin zai iya zama na wani lokaci kafin abinda yake jira ya samu ya koma gida. Abinda kuma ya saka ya zaɓi can ɗin kasancewar gurin wajen gari ya sani da wahala ace ya haɗu da wata fuskar sani saɓanin idan hotel ya kama a cikin gari. Yayi tunanin ko dai ya kira Zulaiha ne yace ta taho? Amma kuma daya tuna Zulaihan ba wacce ya sani a baya bace sai ya fasa, baya zaton zata rufa masa asiri koda ya faɗa mata gaskiyar halin da yake ciki, ba ita ba ko yan uwansa ya san ba zasuyi shiru ba a yanzu a duniyar nan kaf Halima ce kaɗai wacce yake da tabbacin ko mutum ya kashe zata rufa masa asiri.

Ya kunna wayarsa amma ya barta a flight mode, tunani ya ringayi anya kuwa bayan duk abinda ya faru Halima zata sake dubansa? Zuciyarsa ta bashi ƙwarin guiwa akan fushin Halima akansa ba mai dogon zango bane, dukda shi da kansa ya tabbatar da yaga canji amma ko a shekaran jiyan ya hangi ɓurɓushin soyayyarsa da bata ida mutuwa ba a ƙwayar idonta.

Ya san mai take so, soyayyar sa da kuma tattali da kulawa da zarar kuma ta same su zata manta komai. Da wannan ƙwarin guiwar ya ɗora wani tsohon Data sim da ya siya bai zaci ma yana aiki har lokacin ba yayi recharging nasa kafin ya cire layukansa biyu da aka sanshi dasu ya zuba a zip ɗin jakarsa sannan yayi sub ya buɗe sabon Whatsapp da layin ya tura mata saƙo.

Tun yana tsammanin samun amsa har ya fitar da rai dukda cewar ta buɗe saƙon, ganin har tara ta gota bata ce komai ba ya yanke shawarar kiranta voice call amma cikin rashin sa'a bata online cikin jin haushi ya kashe wayar gaba ɗaya kafin ya kwanta yana juyi akan gado cikin rashin sanin madafa.

Kwanciya yayi yana lissafin mafita, ya sani ƙarshe Jalilah ta nemi ya biyata kuɗin kayan daya ɗiba dan bayan su duk wani abu daya mallaka masa daga haɗuwarsu zuwa yanzu kyauta ce ba kuma roƙarta yayi ba dan haka bata isa ta nemi wani abu daga ciki ba. Kuɗin kayanta kuma da kuɗin Alhaji Lawan basu wuce chicken change ba idan abinda yake jira ya sauka

Life time saving ɗinsa ya tattara, duk kuɗaɗen daya ringa samu a hannun Hafiz da Jalilah harda kadarorin daya siya duk ya siyar ya haɗa kuɗin ya zuba a hakar fitar da kayayyaki ƙasashen waje.

Tun kafin ya auri Halima akwai abokinsa Yahya ne da sukayi University tare shi Yahya yana harkar Import and Export na kayan noma irinsu Citta, Barkono, Riɗi da su Zoɓo.

Akwai tarin alkhairi a cikin harkar musamman idan ka shigeta da jari mai ƙarfi supply ɗaya idan kayi sai ka samu riba kusan ninkin jarin daka zuba. Tun bayan da suka gama Jami'a a lokacin yana ta fafutukar samun aiki shi kuma Yahya ya fara harkar a sannan ma kayi nayi yakeyi ya nemo kayan wa masu siya a sallame shi har ya samu jarin daya fara siya shima Allah ya saka masa albarka a abun ganin kuma ya fara fasowa gari ya saka Bilal shiga shima.

Yan kuɗin daya fara dasu ba wani na azo a gani bane amma dukda haka ba laifi idan an siyar ana samun riba dan da kuɗin ya fara ginin gidansa kafin harkar birni da ɗawainiyar Zulaiha suka sa ya dakata kafin daga ƙarshe ƙwadayinsa da son zuciya suka rabashi da Yahyan. Cewa yayi sai Yahyan ya bashi jari mai ƙarfi tunda yanzu Allah ya buɗa masa ya faso gari shi kuma ya ce sai dai ya bashi aro idan ya yarda zai ranta masa ko nawa ne amma kuma ba zai ringa karɓar riba ba har sai ya gama biyansa. Nan fa ya yi masa rashin mutunchi har yana ce masa maƙetaci, bayan duk abinda ya masa sanda suna Jami'a shine yanzu ba zai iya bashi wasu yan kuɗi ba sai dai bashi.

Ya akayi kuma ya koma yana bashi haƙuri sannan kuma ya yarda zai karɓi bashin shi kuma a lokacin Yahya ya canza shawara ya ce ya fasa ba zai bashi ba, a bashi bai shiga tsakaninsu bama ya rufe ido ya masa cin mutunchi ina kuma ga ya tambayeshi kuɗi dan haka ya fasa. Sukayi kaca kaca suka rabu.

Ya riƙe abun a ransa wata rana sai ya bawa Yahya mamaki shiyasa ya ringa tara kuɗaɗe har saida suka kai yanda yake ganin zai shiga harkar da ƙarfinsa. Bai koma ta hannun Yahyan ba sai ya nemi wani abokinsa daya san tare suke komai Yusuf, shi ya bar fitar da kaya ya koma noman shinkafa kamar yanda ya gayawa Bilal ɗin.

Shi yayi hanyar wani kamfanin a Turkiyya da suke siyan Citta da Zoɓo. Kusan wata shida kenan da aka tura kayan, yau ne gobe ne zasu isa shiru yana ta jira domin ba ƙananan kuɗi ya narka ba haka ribar da yake tsammanin samu ba yar kaɗan bace sai da Yusuf ɗin ya bashi shawara daya rage kuɗin yayi yawa ba'a zura jiki a kasuwanci musamman shi da zai fara yanzu amma yaƙi,

Yayi tunanin kayan zasu iya isa a ƙasa da wata biyu kamar yanda aka ce masa da zarar kuma an sauke zasu bashi kuɗinsa cas haɗama ta saka bai dubi za'a iya samun akasi wata matsala ta faru ba ya tattar kuɗaɗe kawai ya narka sai gashi an tafi rabin shekara shiru kaya na kan ruwa sai a cikin satin daya mutu aka ce kaya sun isa amma ba'a sauke su ba.

Yanzu zaman da zaiyi a nan na jiran a sauke kaya ne su tura masa kuɗinsa ya biya Alhaji Lawan ya samu yanci ya warwasa ya taka duk wanda yaga dama. Neman shiri da Halima kuma da yakeyi saboda ko da ace an samu akasi an ja lokaci har asirinsa ya tonu an gano maɓoyarsa a ƙalla ya samu wanda zai tsaya masa dan ya tabbatar duk fuffukar da Abba yakeyi sai dai idan Haliman bata birkice masa ba sai yayi mata abinda take so.

BAYAN SATI ƊAYA
Hajja na zaune tsakar gida ita da Anty Amina da Anty Habiba, kiransu tayi kamar yanda tace tun ranar Juma'a rabon da taji daga pBilal da Fadila. Bilal bai ko shiga gidan ba gurin ɗaurin aure an ce mata ya hau mota ya wuce ita kuma Fadila washe gari da tayi aike a kdagai mata wasu saƙo data sa aka karɓo mata aka tarar gidan a rufe, ta kirata kuma suna fara magana tace tana zuwa zata kirata toh fa har yau kwana bakwai kenan idan an kira layin nata ma a kashe kuma cikin ikon Allah su duka babu mai number angon balle a kira aji ko lafiya.

Anty Habiba tace
"Nima nayi ta kira bana samunta, zuwansu Hajar biyu kuma gidan a rufe amma kuma da alama akwai mutane a ciki dan sunce rariyar gidan da ruwa, abinda ya sa hankali na bai tashi ba ai lafiya itace take ɓuya. Kuma dama tace ya gaya mata idan ta tare sai sunyi sati biyu kafin su fara buɗe gida dan baya so mutane su damesu su hanshi cin amarci".

Hajja ta janye tagumi tace
"To dai ko bunsuru ne shi dai ai ba zai kwana ya wuni yana abu ɗaya ba dole za'a tsaya a huta a ci abinci a lokacin hutun kuma a kunna waya ai a gaisa da yan uwa kowa ya san halin da ake ciki, kuma shi baya sallah ne? Ko kuwa sallar ma a cikin gida yake yinta da ba zai buɗe ƙofa ba?"

"Ni yanzu ya za'a yi na sani Hajja?" Habiba ta faɗa. Anty Amina sai dai ta kalli bakin duk wanda yayi magana bata ce musu kanzil ba, Hajja ta sake cewa

"To shi kuma Bilal ɗin fa? Ko da yake dama shima tunda ya auro wannan tsinanniyar yarinyar sai ya shafe satin ma bai zo ba bai kuma kirani ba nima ɗorawa kai ne ya saka na damu da shirun nasa na manta ya saba dama. Ita Fadilar dai nafi damuwa gaskiya dan haka ƙalau na san ba zata ki kiran waya ba ni dai jikina yana bani akwai wani abu, dan haka yanzu abinda nake so dake da Amina ku tashi kuje gidan ku gano da kanku, zancen yayan nan naki masu azabar ƙarya ba abin kamawa bane. Ku tambaya har maƙwafta kuji ai in dai da mutane gidan ba za'a rasa jin motsi ba".

Haka suka kama hanya a motar Anty Aminan, Anty Habiba ce ta kwatanta mata dan ita bata je kai Amarya ba dare nayi ta kaɗa yayanta masu aure suka wuce gidajensu ta kwashi sauran suka tafi gida. Cikin sa'a suna isa suka tarar da get a buɗe za'a fito da mota, Anty Habiba tace

"Ahaf, ai na faɗa suna nan ga angon nan, tsiyarsu suke shukawa kawai shiyasa suka kulle gida amma Hajja duk tabi ta damu kanta". Gefe sukayi parking sai da ya fito da motar ya sauka zai kulle get kafin suka fita, tsayawa yayi yana kallonsu sama da ƙasa, Anty Habiba ta washe baki ta shiga gaishe shi, yanda ya amsa yana ƙare musu kallo ya saka Anty Amina cewa

"Yayyen Fadila ne, baka gane mu ba ko?"
Ba yabo ba fallasa ya ce
"Ayya ban gane ku ba wlh, toh ya akayi?"

Daga Anty Habiba dake murmushi kamar sokuwa har Anty Aminan buɗe ido sukayi suna kallonsa da mamaki, cikin dakewa Amina tace
"Ban fahimci ya akayi ba? baka ji abinda nace maka bane mu yayintane ko kuwa ba zamu zo gidan ƙanwarmu ba sai da dalili?"

Kwarjini tayi masa dan haka ya matsa yana cewa
"Bismillah" tayi tsaki ta wuce Habiba tabi bayanta tana waigen Ahlan daya zaro waya daga aljihunsa yana dannawa. Anya kuwa shi ɗin ne saurayin Fadila da kamar zai kwanta mata tsabar biyayya idan yaje zance Fadilan na gidan? Kofa a kujera baya zama idan zasu gaisa ƙasa yake sauka amma shine yau yake cewa bai ganeta ba lallai akwai ƙatuwar matsala toh.

Ƙwanƙwasa ƙofar falon Anty Amina ta shiga yi a fusace a ranta kuma tana ayyana dama ta san za'ayi haka, amma kuma Tsuntsun daya ja ruwa shi ruwa zai doka. Yanda ta buɗe ƙofar zaka san a tsorace take, su biyun suka zuba mata ido cike da son tabbatar da Fadilan ce ko kuwa wata mai kama da itace aka samu.

Cikin yanayin tsoro da kuma murna a haɗe ta ƙaƙalo murmushi ta shiga kiran sunansu tana cewa
"Kune? Ku shigo mana" ta juya ciki suka bi bayanta. Ga dai gida har gida, falonta tamkar na wani babban attajiri ko ɗan siyasa amma a kallo ɗaya zaka fahimci matar gidan tayi hannun riga da kwanciyar hankali. Zama sukayi suna kallon Fadilan dake ta murmushin yaƙe tana musu sannu da zuwa kafin ta zauna a shiga gaishe su cikin ladabin da basu san yaushe ta koyeshi ba.

Sukayi jugum jugum bayan gaisuwar, Anty Amina na ƙare mata kallo tana karantar canzawar da tayi a cikin sati ɗaya, rama har a fuska Fadila dake da cikakken jiki dukda bata da kiɓa amma jikinta irin me luf-luf ɗin nan ne haka fuskarta cike take da kumatu musamman dab da bikin kayan matan data ringa sha suka sake cikata amma a sati duk ta zaizaye sai kace wacce tayi amai da gudawa, ga dai haske tayi irin na mai zama guri ɗaya musamman kuma ga Ac amma fa duk tsokar data zo da ita a jikinta t zaizaye.

Ta sauke ajiyar zuciya jin Anty Habiba data gama ƙarewa falon kallo na tambayar ruwan sha, sai ta miƙe da sauri tana cewa
"Kuyi haƙuri, murnar ganinku ta saka ma manta" ta wuce kitchen ba jimawa ta dawo da ruwan faro ƙwara biyu akan try sai kofuna suma biyu ta ajiye musu.

"Yanzu idan baƙin kunya ne suka ce ki basu ruwa haka kuwa zaki dakko tsurar ruwan ki basu Fadila sai kace wacce taba jin hausa?" Anty Habiba ta faɗa, kafin ta bata amsa Anty Amina tayi saurin katseta da cewa

"Dama Hajja ce tace kwana biyu ta jiki shiru ko a waya shine tace muzo mu duba mata ke, tunda kuma kina lafiya shikenan mu zamu wuce" ta miƙe, yanda kasan a ƙaya Fadilan take itama ta miƙe tana cewa

"Ai wayar ce ta faɗa ruwa amma zan kirata nagode ku gaida gida". Habiba zata sake magana dan abin ya ɗaure mata kai Anty Amina ta katseta, ganin kuma Ahlan ɗin ya fito daga kitchen dukda basu san sanda ya shigo ba ya saka tayi shiru suka tashi suka fita tana musu Allah ya kiyaye daga inda take tsaye bata ko ƙara taku ɗaya ba.

Duk su biyun sunji ƙarar marin daya kifa mata da ihun data fasa kafin ƙofar ta ƙarasa rufuwa, da yake window duk a rufe suke kuma basu ji cigaban abinda yake faruwa ba, Anty Habiba taci burki tana cewa
"Amina kinji abinda naji? Kamar fa marin ta yayi?"

"Sai ki koma ki rama mata tunda dama dake aka haɗu aka tura motar" Aminan ta bata amsa tana nufar get, Habiba tabi bayanta tana cewa

"Na shiga uku, wlh mutumin nan shigo-shigo ba zurfi yayi mana daga ganin Fadila tana cikin tashin hankali wlh kuma a haka zamu tafi mu barta?"

"Ni dai kin san bakuyi shawara dani ba sanda zata aureshi, hasalima sai ranar ɗaurin aure naji sunansa na kuma fara ganinsa dan haka yanzu kada wanda ya tsomoni a cikin shawarar yanda za'ayi dan ban zan hawa ba ba za'a nemi gangara dani ba" ta faɗa tana buɗe motarta. Har suka isa gida kuwa da kunne take sauraron Habiba dake ta amma bata tanka mata ba, sai da suka je ƙofar gidan Hajja kafin tace mata

"Kinga idan kika gayawa Hajja na ɗaya zaki tayar mata da hankali ƙarshe hawan jininta ya tashi sa'annan ita kanta Fadilan ki ƙara jefata a wani taskun dan dai ganin idonki kinga alamar baya buƙatar kowa yaje masa gida itama kuma ta yarda da hakan domin da tsarin bai mata ba ai tana da ƙafafu ba kuma kulleta yakeyi ba zata nemi hanyar gida da kanta, ke ko kulleta yakeyi har idan taga zaman bai mata ba zata nemi mafita dan haka ki kama bakinki kawai.

Hajja ta washe baki jin sun samu Fadilan kuma sun ce lafiyarta ƙalau kafin tace
"Ja'ira wato ita miji daɗi, toh ya na ganku hannu na dukan cinya? Bata bayar da komai a kawo mun bane ko kuwa a mota kuka manta?"

"Tace zasu zo a cikin satin nan ai" Anty Amina tayi saurin bata amsa ganin Habiba ta buɗe baki, sai ta taɓe baki tace
"Ai shikenan Allah ya kawo su lafiya". Ta ɗaga pillow ta zaro takardu ta miƙawa Amina tana cewa

"Kuna fita waccen yarinyar matar Bilal tazo, to dai itama tace tun ranar Juma'a tana gidan kai amarya ya kirata yace daga can ta wuce gidansu wai tafiyar gaggawa ta kamashi idan ya dawo zaije ya ɗakko ta, toh mayyar bata tafi ba ta zauna. Ni nafi zaton Abuja ya tafi gurin waccen ɗaya shaiɗaniyar Bilal dai ba zai daina sakani magana ba".

Su kuma takaddun na menene?" Anty Amina ta tambaya tana juya takardun hannunta, Hajja ta watsa hannu tace
"Na iya karatu ne ni balle ki tambayeni? Shiyasa ai na ajiye su ina jiran Abubakar ya shigo tunda kun rigashi sai ki buɗe ki gani ƙila sakinza tayi".

Anty Amina da Habiba suka kashe da dariyar maganarta, wai ƙila sakinsa tayi, Hajja kenan ko a ina mace take sakin namiji sai Allah.
Dariyar Anty Amina ta katse ta ɗora da salati tana duba takardar Hajja da Habiba suka zuba mata ido da son jin ƙarin bayani dai dai lokacin kuma Abubakar yayi sallama tareda Abdullahi babban ɗan Anty Aminar duk suka shiga sahun masu tambayar mai ya faru?

Abubakar ta bawa takardar, ya gama karantawa ya ninke yana cewa
"Allah ya rufa asiri amma dama na san sai anyi haka?"

"Sai anyi haka dame? Wai mai aka rubuta dan ubanka ka wani ninketa ba kai mana bayani ba?" Hajja ta zaburo masa, ya zauna yana cewa

"Sammaci ne daga kotu, gidan da wannan budurwar tasa ta siya ya siyarwa da wani mutum ba tareda ta sani ba, yanzu kuma ita ta siyarwa wani dan haka wanda ya siyarwa ya makashi a kotu bisa zargin damfara. Ɗayar takardar kuma ita budurwarce ta yi ƙararsa itama akan zargin sata, da kuma yaudara da zamba cikin aminci".

"Amma Allah ya tsinewa wannan yarinyar Jalilah, dama ashe ta shigo rayuwarmu ne dan ta jefa mu a masifa ta lalata mun ɗa shine yanzu zata masa sharri ta haɗashi da hukuma saboda bai aureta na ko me?"

"Wlh na sharri ta masa ba duk abinda ake zarginsa ya aikata da bakinsa duk ya faɗa mun, yanzu dai ku nemo shi kawai dan wannan sammacin ma na biyu ne kuma da gargaɗi kotu zata iya ɗaukar kowanne mataki idan bai bayyana gabanta nan da kwana biyu ba" Abubakar ya sake faɗa yana duba takardar. Hajja ta fashe da kuka tana salallami duk sai jikin Anty Amina yayi sanyi tace

"Ba kuka zakiyi ba Hajja addu'a ya kamata kiyi"

"Yana zaman-zamansa yana lallaɓa rayuwarsa da yar matarsa haka kawai ya rakitowa kansa masifa, ina amfanin tarayya da wannan shaiɗaniyar yarinyar gashi yanzu tana nema ta tozarta mu ta jefa

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login