Showing 225001 words to 228000 words out of 257873 words
dab da buɗe ƙofa ya ce
"Amm an daɗe ba'ayi amfani da gurin ba muje can ɗakina" ta masa kallon daya saka yaji kamar ya fasa kuka dan gani yayi kamar ta gane komai kafin kuma ta saki murmushin daya kasa gane dalilin sa ta juya ya bita a baya suka fice daga falon. Sai da tayi wanka Bilal na tsaye a ɗakin kamar dogari ya kasa zaune ya kasa tsaye har wani zazzaɓi yaji yana neman saukar masa saboda tashin hankali.
A ƙasa ta saki towel ɗin bayan ta fito ta buɗe akwatinta ta shiga shafa mai shi dai tunda ya kalleta sau ɗaya bai sake ba ya mayar da idonsa ƙofa yana amsa mata maganar da takeyi masa da Eh ko Aa kawai harta gama shiryawa lokacin aka kira sallar magriba ta kalleshi ta ce
"Ka shirya zaka rakani wani waje ne"
"Toh bari nayi sallah" ya bata amsa da sauri kamar yana jira. A ɗakin yayi sallah ya jirata itama tayi kafin suka fita ta shiga mota bayan ya kunna yace mata yana zuwa ya koma ciki da sauri. Akwatinta ya ɓoye cikin wardrobe da sauran kayan data bari akan gado.
Sai da suka hau titi kafin ta faɗa masa in da zasuje, Calido suka zauna jiran mutumin da zata gani ɗin shi dai Bilal ya samu guri ya zauna fuskarsa har ta rame saboda tashin hankalin bazata daya sameshi ita tayi musu order abinci tana danna wayarta tana kallon Bilal jefi jefi tana sakin murmushin da ita kaɗai ta san ma'anar sa. Sai da suka fara cin abincin kafin mutumin suka iso su biyu, hannu suka bawa Bilal suka gaisa kafin suka zauna tace suyi order suka ce Aa a ƙoshe suke sun gode.
"Wannan Ahlan kenan, kuma shine wanda na siyarwa da gidan nan na Rijiyar Zaki, amma kuma ɗazu da safe yaje gidan wai ya tarar da mutane a ciki kuma mutumin ya tabbatar masa da siyan gidan yayi ba wai aro aka bashi ko haya yakeyi ba" Jalilah ta faɗa tana nuna mutumin da tun zuwansu Bilal yake jin kamar ya sanshi a wani gurin. Bilal dake zuƙar lemo yayi saurin furzar dana bakinsa saboda yanda ya tasarma bi masa ta hanyar wucewar iska, ya shiga tari kamar ba gobe gaba ɗaya suka rufu kansa suna yi masa sannu. Kusan minti uku ƙafin ya lafa masa idanuwansa sunyi jazir sau ajiyar numfashi yakeyi yana zare ido.
Jalilah ce ta sake kallon mutumin data kira da Ahlan ta ce
"Wannan shine Bilal kuma shine caretaker gidan, kamar yanda na gaya maka ka kwantar da hankalinka babu wata matsala zai yi bincike duk abinda yake da akwai zaka ji mu yanzu sai kuyi exchanging contact ko?" Ta ƙarasa tana kallon Bilal daya zama hoto a gurin daƙyar ya iya miƙawa Ahlan ɗin wayarsa ya saka masa number yayi dialing kafin sukayi musu sallama suka wuce.
"Yanzu ya akayi har wani ya shiga gida ya zauna har yana iƙirarin siyan gidan yayi kai kana nan baka sani ba?" Jalilah ta faɗa bayan wucewar su Ahlan. Bilal dai shiru yayi dan zuwa yanzun ya gane kawai so takeyi ya tona kansa da kansa amma ta rigada ta san komai dukda bai san zurfin abinda ta sani ɗin ba, ƙaramin tsaki yaji tayi kafin ta miƙe tana kallonsa ta ce
"Muje ka kaini Hotel"
"Kayanki fa?" Ya tambayeta da sauri ta ɗan kalleshi kafin ta ce
"Oh, to muje na fara ɗauka sai mu dawo". Suna dab da fita daga gurin idonsa ya hango masa wata kamar Zulaiha tareda mutum biyun da suka rabu da su yanzun nan, tsayawa yayi yana kallon su da yarinyar ta juyo kuma sai yaga ba Zulaihar bace dan kayan jikinta ma ba wanda Zulaiha ta fita dasu bane kawai shaiɗan ne ya haska masa take kuma ya tuna a inda ya san fuskar mutumin wanda ya biyo Zulaiha ne ranar da sukaje siyan Shawarma.
Sai da suka shiga layin gidan kuma yaji daya sani fara kaita Hotel ɗin yayi kafin ya dawo ya ɗaukar mata kayan yanzu idan Zulaiha ta dawo gida fa?
A mota ya barta ya shiga, ganin ƙofar falo a buɗe ya tabbatar masa ta dawo dan haka take sau dubu zai rufe mata ƙofar sai ta buɗe halayyar yan ghetto dai ga fanka ga Ac amma wai iska take sha. Kamar ɓarawo haka ya ringa sanɗa har ya shiga ya ɗakko akwatin, yana kaiwa Get yaji muryar Zulaihan a bayansa tana tambayar yaushe ya shigo, bai kulata ba ya fita itama ta taɓe baki ta koma ciki abunta.
Sau sha biyu saura ya baro gurin Jalilah kuma har suka rabu bata sake tayar masa da maganar gida ba ta dai ce ya zo da safe da wuri, ya wuce zuciyarsa fal tambayoyin daya kasa yi mata. Bashida tabbacin ta san shi ya siyar da gidan ko ba haka ba sannan kuma in dai ita ta siyar da gidanta da kanta kenan tana sane ta bashi fake takardu idan haka ne kuma na Shago ma ita ta canza su, toh zarginsa takeyi dama ko me?
Yaji daɗi da Zulaiha bata je ɗakinsa ba dan bai ko kwanta ba kwana yayi yana safa da marwa idan ya gaji ya zauna tunani kamar ƙwaƙwalwarsa zatayi bindiga yanzu yaya zaiyi? A ina zai nemo Miliyan Hamsin da biyar ɗin da zai biya Alhaji Lawan kuɗin sa? A ina zai samu kuɗin da zaiyiwa Fadila kayan ɗaki ya gujewa fushin Hajja? Ya zaiyi da batun aikinsa wanda a yanzu ne ya fahimci kasassaɓar da yayiwa kansa da yayi wasa da shi? Sannan duk bayan wannan ya zasu kwashe da Jalilah?
*KURA A RUMBU*
*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*
*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya naira 800, biya a asusun*
*7061838488*
*Opay*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*
*PAGE 56*
Kwana uku Jalilah tayi a Kano ta wuce Abuja bayan ta bar alhakin sauke kayan da suka fara isowa a hannun Bilal. A tsakanin kwanakin har rama yayi; duk wanda ya sanshi kallo ɗaya zakayi masa ka fahimci yana cikin damuwa matuƙa, duk in da yake tunani zai buga lissafi ya fita abu ya gagara, idan ya haɗo nan sai can ya rushe ga Alhaji Lawan ya taso shi a gaba da zancen kuɗinsa dan tuni ya kwashe kayansa ya bar gidan kamar yanda ya ce har Ahlan mamallakin gida na asali ya saka an sake gyara ko ina sai jiran shigar amarya kawai.
Yana kwance idanuwansa a rufe kamar mai bacci amma a zahiri idonsa biyu, Zulaiha ta shiga ɗakin tun kafin kuma ta isa gareshi ya shaƙi kamshin turaren da yake jansa gareta tamkar mayen ƙarfe duk sanda ya shaƙe shi, bai motsa ba dukda yanda lokaci ɗaya hankalinsa ya fata tashi kuma jikinsa ya amsa har ta iskoshi ta zauna gefen ƙafafunsa cikin salo ta shiga shafa sangalalen ƙafarsa tana kiran sunansa a hankali, duk yanda ya so ya daure amma ina sai da taci galaba akansa.
Haka ya ringa aiki da iya ƙarfinsa tsayin lokaci har saida ya gaji kafin ya saketa ya kwanta a gefe yana mayar da numfashi. Cikin hayyacinsa dai bai taɓa irin wannan daɗewar ba sai fa sanda take saka masa wannan abun daya ɗauke ya kuma yi mamakin yanda bata tambayeshi ba ko da yake ai da kunya.
Tsaki mai ƙarfin da Zulaihan ta saki ya saka ya juya ya kalleta da mamakin dalilin tsakin, ta tunzura ƙaton bakinta gaba kafin tace
"Wai wane irin wulaƙanci ne haka Bilal? Yau kwana nawa baka ko shiga ɗakina ba balle ka sauke mun haƙƙina? Sannan yanzu ni na kawo kaina babu wani dogon wasa ba komai ka faɗa mun kalli ko minti 5 bakayi ba ka wani jibge kamar wani kayan wanki toh wlh ni ban gamsu ba, dama na san kai lusari ne shiyasa nafi gane inyi da kaina amma kaƙi; toh wlh ka tashi dan ni ban ma fara jin komai ba" ta ƙarasa tana ƙoƙarin hayewa jikinsa.
Bilal dake kallonta cike da al'ajabi yayi saurin janyewa kafin ya kalli agogo dan ya tabbatar da minti biyar ɗin da tace, karfe takwas da minti goma t shigo ɗakin yanzu agogo yana buga takwas da rabi har da mintoci a sama a ƙalla suk ɗauki sama da minti 15 tare amma shine take cewa minti 5 tsabar ta raina ƙoƙarinsa?
Ganin da gaske takeyi tana neman danneshi da ƙarfi ya saka ya buga mata tsawa kafin ya tashi zaune yana kallonta ya ce
"Mai yake damunki? Me kika sha?"
"Ni babu abinda na sha kuma lafiya ta ƙalau lafiyar ce ma ta kawo haka kai zan cewa mai yake damunka? Malam ka nemi maganin sanyi da basir kawai dan ni ba irin tsohuwar matarka bace" ta faɗa tana wani juya ido. Sai ya kasa ce mata komai kawai ya zuba mata ido yana kallonta, shi dai tunda yake da Halima bata taɓa raina ƙoƙarinsa ba kullum cikin kwarzantashi takeyi tana nuna masa shi ɗin sadauki ne nagaske amma yau shi Zulaiha ta kalla ido da ido ta kirashi da lusari?
Ya sha tsallake Halima a lokacin da shi da kansa ya san tana buƙatar kasancewa tareda shi amma bata taɓa ƙorafi ba, sau da yawa zata iske shi amma ya ce mata bacci yakeji kuma haka zata barshi bai ko taɓa damuwa da wane hali zata shiga ba amma yau ga wata bayan ya biya mata buƙatar ta raina har tana ƙoƙarin danneshi da ƙarfi
"Ni dai ban yafe ba wlh" ya tsinci kalaman Zulaiha kafin ta sake sakin tsaki ta fice daga ɗakin ta barshi a tsaye cikin maɗaukakin mamaki. Wanka ya shiga tun yana ciki kuma yaje jiyo ƙarar wayarsa dan haka yayi sauri ya fito a zatonsa Hafiz ne dan ya kirashi yana so ya masa zancen salaryn sa ko akwai yanda zai taimakeshi sai dai bayan daya fito ya duba wayar ya tarar Alhaji Lawan ne ya kirashi. Tsaki yayi ya ajiye wayar ya shiga shiryawa dukda dare ya farayi amma dole ya fita.
Sai da ya hau titi kafin ya sake duba wayar, saƙon daya gani ya buɗe, ƙirjinsa ya huga dum kansa ya sara, gefen hanya ya samu yayi parking ya shiga ƙoƙarin neman layin Nasir amma cikin rashin sa'a akace a kashe yake. Gidan Nasir ɗin ya nufa kai tsaye, Nasir yayi shiru yana saurarensa har yayi shiru kafin ya ce masa
"Ya kirani tunda yamma ya faɗa mun idan ya kiraka baka ɗauka dan haka ya yanke shawarar kai maganar gurin shari'a, tun farko Bilal sai da nace maka ka haɗa kuɗin mutumin nan ko da ace basu cika ba ka rage masa wani abu a zauna ayi rubutu ka faɗi nawa zaka ringa bashi kuma zuwa tsahon wane lokaci amma kaƙi, yanzu ga abinda nake guje maka nan yana shirin faruwa".
Tsaki Bilal yayi ya ce
"Ban gane in biya kuɗi ba saboda me?"
"Au saboda me ma kake tambaya?" Nasir ya faɗa cike da mamaki, tsaki Bilal ya sakeyi kafin ya ce
"Look Nasir, ni fa ba wasu kuɗi da zan biyashi. Gida ya siya kuma d shaidu da komai ya biya kuɗi an bashi takardu akan me yanzu zai zo da wani rainin wayau? Nima fa gidan nan siyan sa nayi kuma na siyar masa, ai kamata yayi ya nemi wanda ya zo ya ce shima ya siyi gida idan ma shari'a ce dashi ya kamata yayi"
"Toh idan aka je gaban shari'ar na tabbatar in dai ba mahaukacin Alƙali aka samu irin ka ba abu na farko da za'a farayi shine kowa ya zo da wanda ya siyi gida a gurinsa nan kuma wa zai kawo?" Nasir ya faɗa yana buɗe murfin motar, Bilal ya watsa hannu alamar Oho, Nasir ya girgiza kai cike da takaici ya ce
"Shikenan sai da safe" daga haka ya fita daga motar.
Daga gidan Nasir Bilal gidan Hajja ya wuce, fuska ba yabo ba fallasa ta karɓe shi abinda bai zata ba dan tun waccen ranar bai sake zuwa gidan ba a waya ma sau biyu ya kirata kuma duk bata amsa ba shiyasa daya ga fuskarta a sake yanzun abin ya bashi mamaki ya kuma sha jinin jikinsa dan ya san da wahala idan ba tarko zata masa ba.
"Ka ji ɗan albarkan yaron nan yace ba sai ta tafi da komai ba ya rigada ya zuba abunsa" Hajjan ta faɗa masa, yayi ɗan murmushi ba tareda ya ce komai ba sai Hajjan ce ta sake cewa
Asabar ta sama ɗaurin aure"
"Amma Hajja wai a gurin wa akaje neman auren da har aka tsayar da lokaci?" Ya faɗa yana kallonta ta zabga masa harara tace
"Kai a gurin ubanwa aka nema maka naka auren?"
"Amma ni Hajja mun daɗe da yarinyar, na santa na san iyayenta na kuma san duk halayyarta sa'annan ni namiji ne shari'a ta yarjemun da na wakilci kaina a neman aure. Gaskiya ya kamata ace anyi bincike asan wanene wanda zata aura ɗin asan asalinsa da kuma menene sana'arsa, zamanin nan da mugaye sukayi yawa mutum yazo yana wasan kuɗi irin haka ai ya kamata a saka masa alamar tambaya" ya faɗa kansa a ƙasa.
Banza Hajjan tayi masa kusan minti biyar kafin tace
"Sai ka saya mata ɗankunne da sarƙa da kuɗin kayan ɗakin"
"Ni fa wlh Hajja bani da wasu kuɗi yanzu, kafin lokacin idan na samu zan bata amma ban ɗauki alƙawarin siya mata Gwal ba" ya bata amsa, ta watsa masa wani kallo kafin ta kai ga magana ya rigata kamar zai fasa kuka ya ce
"Wlh Hajja ina cikin matsala. Duk yan kuɗaɗen da suke hannuna sun ƙare a harkar bikin nan waɗanda na saka ran zan samu kuma abin bai yiwu ba yanzu haka account ɗina wlh ko dubu ɗari bani da ita".
"Wannan kuma kai ta shafa ba ni ba, wato ni da wuyar naƙuda da shan wahalar raino harka girma sai da ka zama abin moro sannan zaka koma bawan can wata ƙatuwa da iyayenta ko? To wlh baka isa ba ko sata zakayi kaita shafa ni dai na gaya maka ka siya mata sarƙa da ɗankunne" Hajjan ta bashi amsa cikin ko in kula. Har kusan sha biyu yana gidan, sai da Abubakar ya shigo har ya kulle ƙofa ma ya tarar da Bilal ɗin a falo shi kaɗai dan tuni Hajjan ta shige ɗaki ta kwanta Fadila kuma dama tana gidan Anty Habiba wai ta fara gyaran jiki.
Kamar Abubakar ɗin ba zai kula shi ba dan har ya juya ko mai kuma ya tuna sai ya koma ya shiga falon yana kallon Bilal ya ce
"A nan zaka kwana ne?"
Agogon dake ɗaure a hannunsa ya duba ya buɗe ido ganin lokaci kafin ya ce masa
"Ban san lokaci ya tafi haka ba"
"Ya kamata ka tashi toh dan naji iska tana kaɗawa kamar hadari ne yake tasowa" Abubakar ya sake faɗa, sukayi shiru kafin ya ce
"Kana aikawa da yaran can abubuwan buƙata kuwa?"
Kallon rashin fahimta Bilal ɗin yayi masa dan haka ya ce
"Su Al'amin, kana aika musu da kuɗin abinci da na sauran buƙata? Sannan kuɗin makarantarsa da sauran abubuwan duk kana kulawa da su?"
"Ai ita ta matsa na saketa kaga kenan ta shirya kula da su" ya bashi amsa ba tareda ya kalle shi ba. Abubakar yayi murmushi ya ce
"Ai sabon abu bane, ko a sanda take gidan naka ma ai ita take ɗauke da nauyin kanta da na sun kaga ba zai zame mata sabo ba dan taci gaba. Wlh Yaya Bilal kayi babbar asara, samun mace tamkar Anty Halima a zamanin nan sai sa'a kuma tunda ka rabu da ita ba zaka mai da irinta ba ko mace dubu zaka aura wlh ba dai ka samu irin Halima ba
Ta soka saboda Allah, ta wahalta maka da jikinta da aljihunta amma ka biyewa duniya ka yi mata sakayya da sharri, wlh ko bata buɗe baki ta nemi sakayya a gurin Allah ba haƙƙinta ba zai taɓa bari ka zauna lafiya ba ga kuma haƙƙin yayan daka barta dasu, baka san cinsu ba baka san shan su ba sutura, rashin lafiya, karatunsu babu wanda ka damu dashi.
Bana zaton tun ranar da suka bar gidanka ka sake sanya su a idanuwanka, idan baka dubi Allah ka sauke haƙƙinsu daya ɗora maka na dole ba ai ya kamata ko dan duniya da gobenka ka jiƙansu ta yanda kaima gaba lokacin da ƙarfinka ya ƙare zasu tausaya maka".
Har ya isa gida yana tilawar maganganun Abubakar kamar karatu, har ya wuce falon Zulaihan sai kuma ya koma a ransa yana jin babu daɗi dukda bai san dalilin hakan ba. Ƙofar a buɗe take dan haka ya tura ya shiga da sallama, Tv na kunne amma an yi muting volume falon kaca kaca daga gani baƙi tayi kuma bata ji zata iya gyara gurin bayan tafiyarsu ba ta tsallake ta barshi a haka.
Kayan dake zube ya tsaya yana kallo, kwalayen pizza, ga raps ɗin shawarma, ragowar kaza sai kwalaye da gwangwanayen lemo d sauran kayan ciye-ciye dai iri iri. Kayan daya gani a freezer waccen ranar suka faɗo masa dan haka ya wuce ɗakinta,
"Haba mana Babe" ya tsinkayi muryarta tana faɗa haɗi da ƙaramar dariya, burki ya ci a bakin ƙofa dan a buɗe ɗakin yake ya shiga kallon kan gadon ta cikin ɗan hasken da yake shigowa daga falo dan ta kashe fitulun ɗakin.
"Yes Babe cigaba I'm enjoying" ta sake faɗa tana sakin nishin daya saka gabansa faɗuwa, yanayin da tayi maganar da nishin da tayi sai ya zo masa tamkar ire-iren lokutan da suke phone sex da Jalilah. Nishin data sakeyi ya saka shi kiran sunanta da ƙarfi lokaci ɗaya kuma ya kunna fitulun ɗakin gaba ɗaya haske ya gauraye ko ina.
Zulaiha dake cikin bargo suna waya da Ahlan, guy ɗin data haɗu dashi ranar da sukaje siyan Shawarma da Bilal, har ga Allah tunda aka ɗaura mata aure tayi alƙawarin barin duk wasu abubuwa da takeyi kuma ta daina ɗin amma ita kanta bata san dalilin daya saka ta kasa tsallake