Showing 201001 words to 204000 words out of 257873 words

Chapter 68 - KURA A RUMBU HAUSA NOVEL

23 Oct 2025

478

tana ta ce mun

"Babu komai ki kwantar da hankalinki komai kika ga ya faru a rayuwa da sanin Allah addu'ar da muke yi muku kuma a kullum in sha Allahu ba zata faɗi a banza ba kada ki wani saka danuwa a ranki".
Allah sarki ni, ana baƙin ciki da mutuwar aure amma nawa kowa aka faɗawa sai dai yayi hamdala haɗi da yi mun barka, ɗaya daga cikin fargabata na kar ayi mun dariya ta kau domin dai da alama tausayi na ma ake ji a maimakon kuma a zageni yanda nayi tunani sai barka ake mun kamar wacce ta fito daga hannun kidnappers.

Hankali na ya sake kwanciya ganin har sati ya ƙare Bilal bai sake turo mun da wani saƙo ba sannan babu wanda ya zo ko yayi waya daga ɓangarensa akan yara, dama fargabata ta biyu kenan ace za'a rabani da su sai dai na samu nutsuwa dan Abba da kansa da na ce masa Anty Labiba ta ce za'a mayar masa da su Al'amin ya ce Aa in kwantar da hankalina wasa take babu wanda ya isa ya rabani da yarana.

BILAL

Allah Allah ya ringayi Asabar tayi Zulaiha ta tare ko zai huta da masifar mita da bani banin da suka tasashi gaba, shi gaba ɗaya ma ya kasa ganewa al'amarin, naira miliyan uku ya bata kuɗin lefe da hidimar biki amma daga kan kayan gadon da suka ɗora masa zuwa sauran abubuwan da ta sake bijiro masa da su sai da ya sake kashe wata miliyan ukun harda ɗori akai.
[5/19, 22:05] Buhainat: *KURA A RUMBU*

*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*

*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya naira 800, biya a asusun*
*7061838488*
*Opay*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*


*PAGE 51*

Ranar Alhamis suka je jere ko ya ce ganin gida tunda dai shi yayi jere, yan buhun hunan da suka je da abinda suka kira kayan kitchen tsabar takaici kallo ɗaya ya musu ko gaisuwa mai kyau basuyi ba ya fita ya barsu da yayyensa banda Anty Amina da sukaje tarar masu jere. Bai san munafukin daya gayawa Hajja shi ya siya mata kayan ɗaki ba ai kuwa ya sha tijara wannan kuma ya sake ruguza ɗan shirin da suka farayi ta kuma ja masa kunne akan ba fa zata saɓu ba, ita da wahalar haihuwa da raino can wasu a gefe da cin moriyar arziƙin sa dan haka daga wannan idan ya kuskura ta sake jin magana makamanciyar wannan tabbas za'a ji su a rana.

Kayan kitchen dai tarkace suka jera yanda ka san a ƙauye, shi rabon da yaga Risho wlh ya manta amma sai gashi wai shi aka kawowa Zulaihan. Tunani ya ringayi a ransa a ina ma za'a samu kalanzil dan bashida tabbacin har yanzu ana siyarwa. Yanzu banda tsiya ina laifi ko camping gas ne ko 1kg su siya mata kai shi wlh gara ma a haɗota da murhun kurfoti ya fi wannan Risho ɗin da suka kawo masa gida.

Ta ce masa suna da labule dan ita ta faɗa masa kalar labulen ma da zai zaɓi kujeru ta kuma ce akwai carpet, fridge, Tv harma da gas ɗin amma bai ga ko ɗaya ba haka yan jere suka zo ziƙau daga su sai tagayyararrun kayan kitchen ɗin su.

A haka kuma bayan sun koma ta kira shi murya ba walwala tana masa ƙorafi wai an ce mata gidansa na Goron dutse zata zauna.
"Kai da ka ce mun a Rijiyar zaki gida na ya ke ya akayi kuma yanzu akace in da Maman Al'amin take zan zauna?" Ta faɗa, a sama yake dan gaskiya lamarin jeren nasu ya ɓata masa rai yanda baiyi tsammani ba. Duk miliyoyin daya kashe mata ace wannan abun za'a kawo masa tsabar rainin wayau?

Abinda ya ringa sake hasalashi yanda zuciyarsa ke ta hasko masa zamanin Halima, sai da akayi sati ana mata jere idan ya shiga gidan a lokacin har baya son ya fita ga yanda Abokanansa suka ringa kambama abun yana masa daɗi gidansa kamar gidan wani sarki amma yanzu ko gado da kujerar daya siya da kansa a can gurin ya gansu masu kyau amma da aka kawo aka zuba sai ya gansu kamar bola, kujerun sukayi wani yan tsurut a falon ba kwarjini irin na kujerun Halima haka ɗakin ji yayi ransa ya baci daya kalli kayan sai ma ya gansu kamar tsofaffi toh ya saba ganin Made in Turkey a ɗakin, katako da gilasai suna dalle masa ido da hasken su.

Kitchen ɗin kansa da yake shiga yayi ta ɓuruntu ga utensils kala kala yanzu sai tsalli tsallin multi colored kwanuka da rabinsu na roba ne.

"Eh na canza shawara a nan ɗin zaki zauna" ya bata amsa. Ta ce
"Lallai, a gida ɗaya zaka haɗa mu? Gaskiya ba zai yuwu ba tun wuri ma ka sake shawara dan ba haka mukayi da kai ba tun farko".

Kamar ya ce mata
"Ke kika sani" amma gudun ɓacin ranta da yakeyi dukda haushinta da ya cikashi haka ya kanne ya ce

"Wa ya ce miki gida ɗaya zaku zauna?"

Acan ɓangaren Zulaiha da tana sane da cewa Haliman bata gidan kawai so takeyi taji gargar ɗin maganar ta ce

"Gashi kuwa an ce a gidanta aka mun jere"

Wai aka mata jere, tsaki yayi ya ce
"Kuma suka ce miki tana gidan ko sunga kayanta a ciki?"

"Ni ban tambaye su ba wannan, kuma sun ce wai gado ɗaya aka saka kuma ɗaki biyu ne kuma ba'a saka labulaye ba" ta sake soko wata maganar. A hasale ya ce

"Kina ji Zulaiha, nayi iya yina abinda yake haƙƙina da ba nawa ba duk na haɗa na miki. Daga yanda suka ga gidan duk abinda babu ko bai muku ba wlh sai dai kuyi da kanku amma tsinke ba zan sake siya in saka ba".

Muryar Ummansu ya ji daga gefe tana salati kafin ta rufeta da faɗan da bama gane mai take cew yake ba dan haka ya katse wayar sannan ya kasheta gaba ɗaya. Duk Halima ce ta janyo masa, idan da bata kwashe kaya ba ai da bata tona masa asirin gida ba, gurin da yake jin sa kamar Villah, baya shakkar kawo ko wanne irin baƙo, su Hafiz da Jalilah da suka juƙu da naira suke kuma shiga gidaje na alfarma sai da suka yaba kyau da tsarin jeren Halima amma yanzu gida ya koma kamar wani sansanin yan hijira a idonsa. Yayi tsaki a fili ya furta

"Wlh sai kin gane kurenki, sai kin san kin ɓata mun rai".

Rana bata ƙarya aka ce sai dai uwar ɗiya taji kunya in ji hausawa, haka ne kuwa domin Asabar ɗin da ake ta kira ta zo a ranar kuma yan uwansa suka ɗan yi yini a gidan Hajja itama amarya a can gidansu ranar sukayi yinin wanda dukda rantsuwar da yayi akan ba zai sake kashe mata ko sisi ba sai da ya karya ya kai musu buhun shinkafa dan kusan azahar sukaje zai nunawa Abokinsa Alhaji Sani da zasu je ɗakko amarya gidan ya tarar da mata har ƙofar gida suna ta zuba hamma ga yara nata koke koken yunwa wata nata bala'i an san ba'a da abinda za'a girka akan me aka kai musu goron gayyata su ba'a barsu sun dafa a gidajensu sun ci ba an kawo su nan ana musu izaya da yunwa.

Kunya da takaici suka sake turnuƙeshi amma haka ya koma bayan ya sauke Alhaji Sani da ya kasa shiru ya ce
"Kai kuwa Bilal wane rufa ido aka maka kaje irin gidan nan neman aure? Ka san fa akwai banbanci tsakanin Talauci da kuma Tsiya, to kai dai da alama gidan matsiyata kayo aure wlh da matarka ta rufin asiri yar manyan mutane haka kawai ka jajibowa kanka abinda zai dameka".

Shiru ya masa zuciyarsa na kumbura da fushi har suka rabu tsabar rainin wayau daya sauke shi sai ce masa yayi ya tuna ma yana da uzuri ba zai samu zuwa ɗakko amaryar ba amma zai kwatantawa Lamin gidan su sai su je. Haka ya wuce ya je ya siyi shinkafa da kayan cefane ya koma ya kai babu kunya kuma suka karɓe kamar dama ana jiransa ba ko arziƙin godiya kuwa sai ma wata tsomararriyar mata da yaji ama cewa Habi ce take ce masa wai ai da ya haɗo da ko ƙashi ne abincin ya fi zaƙi.

Daga nesa ya hango amaren sun fito daga wani gida, Nuratu kallo ɗaya ya mata kuma ko kaffara ba zaiyi ba ya san Faruk ne ya ɗinka mata leshin jikinta daga zubinsa har ɗinki ya san ba siyayyar waccen matar da Zulaihan ta ringa cewa wai ta san gayu da ita suka so siyayyar lefenta bane abin baƙin ciki tasa amaryar ko da daga nesa yake hango su atamfar data saka da aka yiwa wani ɗan iskan ɗinki da ko a mafarki ba zai yarda Zulaiha zata saka irinsa ta fita ba kallo ɗaya ya mata ya fahimci roba ce ko ma leda.

Cikin fushi ya taka mota ya bar gurin yana gani kuma ta ringa kiransa amma yaƙi amsawa ƙarshe ya kashe wayar ya wuce hotel ɗin daya kama tun da aka kashe kayan Halima.

Bayan sallar isha'i aka kai Amarya, gidan Hajja suka fara zuwa da ita abun dai ba girma balle arziƙi ko ɗan abincin da akeyi na yan kawo amarya hanawa tayi a basu balle kuɗin siyan baki haka suka wuce suna zagin Hajjan aka garzaya da ita gidan Bilal.

Yan kawo Amarya dai sukayi ta santin gida domin a gurinsu Zulai fa tayi goshi. Dama kuma ai gida da kyansa kuma ko kayan da aka saka a ciki sunyi kyau kawai dan an saba ganin wanda suka fi su ne shiyasa yake ganin gurin bai yi masa yanda yake so ba.

Da suka ga Bilal ɗin da gaske yake ba zai ƙara komai a gidan ba kamar yanda ya ce dole safiyar Asabar ɗin suka yanko labulayen da su Fadila suka ce tsofaffi ne aka kafa, ya dai fi babu dukda basu wadaci gurin ba a winduna biyu kawai suka saka da yake kuma an saba ganin gurin cike da labulaye sai yayi haske fayau yan uwansa suka ringa taɓe baki suna kallon gurin babu wannan haɗaɗɗun kujerun da carpet na alfarma da frames da aka ƙawata bango dasu balle Cinema TV irin ta Halima haka suka bar gurin ga dai Tv stand da yake haɗe da kujerun da Center table amma ko center carpet babu alamar sun kawo tunda ko da ba'a shimfiɗawa saboda kar a tattake yayi datti amma dai ana ajiyewa a gefe yanda kowa zai san dashi.

Dama kulle kitchen sukayi sai kace wani abin arziƙi suka zuba ta window wanda suka sawa ransu sai sun ga komai suka ringa leƙawa. Haka aka watse yan uwan Bilal suka tafi da gulma ana ta yi masa Allah ya ƙara. Kowa cewa yake da matarsa ta rufin asiri kuga jarabar daya kwaso wannan amarya kana kallon idonta kasan kunya bata isheta ba amma maganin Hajja kenan har da shi kansa ɗin dama kuma ai haƙƙin Halima baiwar Allah ba zai barsu ba.

Wanda ma basu san Haliman bata nan ba lokacin suka sani anan kuma labarin sakin ya fita amma su Fadila suka ringa ƙaryatawa suka ce tana dai gidansu tayi yaji amma bai saketa ba Huwaila wacce take auren Kawun Halima a Galadanci kuma ta ce aure fa babu shi dan taji labari a cikin gida an ce saki biyu ma ya mata ga kuma babbar shaida har ya saka wata a gidan idan yaji kawai tayi ai ba zata kwashe kaya ba balle a saka wata matar a ɗakinta.

Sai gurin sha ɗaya kafin ya shiga gidan dan a yanda ya wuni cikin ɓacin rai ji ya ringayi ma kamar karya koma amma daga ƙarshe dai ya tattara ya tafi babu rakiyar aboki ko ɗaya ya shiga gidan bayan ya tsaya ya siya mata tsire da yoghurt sai lemuka dan sanda ya je gurin mai naman kaza ta ƙare shi kuma ya gaji bai ji zai iya tafiya wani guri nemo mata kaza ba.

Tsakar gidan kaca kaca kamar anyi yaƙi, ga ƙofar falon a buɗe sai uban hayaniyar ƙawayenta da yake jiyowa mamaki ya kamashi har sai da ya duba agogon hannunsa sha ɗaya har da rabi ta gota, basu da hankali ne? Ko a gidan suke nufin zasu kwana da har suka kai wannan lokacin?

A waje ya bar motar ya shiga ya ɗauki tsintsiya ya fara share gurin dan ba zai iya kwanciya bacci gidansa da wannan bolar ba kuma ya ajiye motarsa a ciki, ya gama ya jona mesa a famfo ya hau wanke gurin a ransa yana ayyana yau zaiga ƙarshe haukan ƙawayen Zulaihan da ita kanta. Yana wanke gurin suka fara fitowa harda ita duk sukayi turus suna kallonsa, wata mai shegen kauɗi ta ce

"Dama na ce muku naji an buɗe get kuka ce babu wanda ya shigo ai". Bai ko kalle su ba ya cigaba da abinda yakeyi sai da ya ji muryar Zulaihan cikin fushi tana cewa

"Yanzu tsabar wulaƙanci ka shigo gidan kana jin ƙawaye na kuma ka san ku suke jira amma ba zaka iya shigowa ku gaisa ka sallame su ba shine zaka hau wani aiki sai kace boyi boyi?"

Kallo ɗaya ya mata ya wuce ya kashe famfo dan ya gama abinda yakeyi. Gurin ya masa yanda yake so dukda hancinsa yana jiyo masa wari wanda ya tabbatar daga banɗaki dake tsakar gidan ne amma yanzu ya gaji sai da asuba zai bi ta kansa. Fita yayi zai shigo da mota ya hango masu gadi sun tsayar da wasu motoci biyu sun hana su shiga layin suna ganinsa Iliya ya nufe shi Basiru kuwa ɗauke kai yayi sama dan ko yanzu da zai shigo a wanda ya ce masa komai a cikin su tun ma waccen ranar idan ma basu ga dama ba wani lokacin sai yayi ta horn kafin zasu buɗe masa ya fita ko ya shiga layin.

"Wai yammatan da suka kawo amarya zasu ɗauka" Ilyas ɗin ya faɗawa Bilal, sai ya koma ciki ba tareda ya ce masa komai ba suna tsaye curko curko murya kamar wanda aka cusawa tsumma a baki ya ce
"Ana jiranku a waje" ya juya abunsa.

"Lallai ma Bilal, wato wulaƙanci ka tasarma yi mun a daren nan kana nufin ba zaka basu kuɗin siyan baki ba ko me?" Zulaiha ta buɗe murya bata ko duba dare ba balle kasancewarta amarya, ƙawarta Suwaiba da suke kira Suby ce ta jata suka koma cikin falo ta ce

"Ke fa banza ce Zulaiha, so kike ki ruguzawa kanki shiri kenan a wannan daren? To wlh kibi a hankali karki tunzura shi ki ɓallowa kanki ruwa bayan kin san dama a ruwan kike"

Tsaki Zulaiha tayi ta ce
"Kin san bana ciki da abu ta kazan uba, na gaji da pretending wlh gara in warware masa tun wuri ya shiga hankalinsa ya kuma kama kansa"

"Ai sai ki bada himma, ni ba wannan ba kin dai saka abun nan ko?" Suby ta sake faɗa ta kuma yin tsaki ta ce
"Na saka mana"
"Toh asha amarci lafiya karki manta kuma ki rage mana kaza dan da wuri zamu zo" suka tafa kafin suka fito lokacin sauran har sun fita Bilal ya shigo da mota yana ƙoƙarin rufe gida da muƙulli. Harda rusunawa Suby tayi ta gaishe shi amma bai ko kalleta ba ya buɗe ƙofa ta fita ya mayar ya rufe. Kai tsaye ɗakin sa ya wuce bayan ya shiga falon da ba ya ko son ganinsa a yanzu ya zube mata ledojin daya shigo dasu.

Zulaiha kuwa dama ɗaki ta wuce abunta ta fara shiri a ranta tana ayyana yanda zata ci kan uwarsa a faɗarta tunda ya rigada ya zo hannu zai san bashida wayo. Ta gama shiri ta fito falon ta zauna tana ƙarewa gurin kallo tana tsaki, da ta san ba zai saki jiki ya mata irin jeren data zata ba wlh da bata biyewa Umma ba kuɗi zata cire tawa kanta abu na birgewa tunda tana da shi. Tsaki ta kuma ja mai ƙarfi, sai lokacin ta lura ashe ko Tv ba'a saka mata ba. Wayarta ta buɗe ta lalubo wata number babu fargaba balle tsoron komai ta danna kira kamar mai wayar kuwa yana jira ya ɗaga daga can ya ce

"My baby, irin wannan kiran ba zata haka kamar kin san kewarki ce ta hanani bacci wlh"

"Ƙaryar banza, to karka manta dai matar aurece ni yanzu kuma ba shashanci na kira muyi ba" ta faɗa a wani dake, daga can ya sheƙe da dariya ya ce

"Su matar aure manya, to ina angon naki kike waya ƙarfe sha biyun dare?"

"Tv nake so" ta faɗa masa dalilin kiran ya tambayeta inchi nawa ta faɗa masa bata bari ya ja hirar kamar yanda ya so ba ta katse bayan ta gaya masa da safe Suby zataje ta karɓa ta taho mata d ita idan zasu zo.

"Ina son fridge da cooker gas ma amma su ba gobe ba sai an kwana biyu" ta sake faɗa yayi ƙasa da murya cikin barikanci ya ce

"Wannan sai kin kawo mun ziyara tukunna sai ki zaɓi waɗanda kike so ki tafi da su".

Motsin taɓa ƙofa ya sa tayi saurin katse wayar ta kasheta gaba ɗaya ma ta gyara zama yanda tayi kuma ba zaka taɓa hasaso alamun rashin gaskiya ko wani abu a tattare da ita ba.

Bilal ya samu guri ya zauna kamar mara lafiya yana kallonta, ya rasa abinda ya sa ya kasa jurewa ya zo, sonta yake kamar rai can ƙasan zuciyarta yana raya masa ya shareta amma ya kasa har ya kwanta haka ya taso ya taho wai yaga taci abin da ya ajiye mata ko bata ci ba?

Murya ba amo ya ce
"Kinci abincin ne?"
"Ka bani ne?" Ta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login