Showing 210001 words to 213000 words out of 257873 words
ji a tsakiyar kansa. Ya tashi zaune yana matse fuska, zazzaɓin daya kwanta dashi ya sauka amma kuma jikinsa sam babu ƙarfi ga hayaniyar data cika gidan daya rasa ta mecece, tashi yayi a hankali ya fita falo, yayi turus a tsaye ganin mata sun bararraje kamar a ɗakunansu suna cin abinci suna hayaniya sai kace masu cin kasuwa.
Wacce take saitin ƙofa ce ta ankara da tsayuwarsa tayiwa sauran alama duk suka juya suna kallon sa, kallon sa kafin waɗanda daɗin hira ya saka suka cire kallabinsu suka shiga ɗauka suna yafawa. Shi dai tsaye yayi yama rasa abinda zaiyi, yanzu ace duk girman falonta da ɗakuna biyu ga tsakar gida bai ishe su suyi didimarsu ba sai sun dangana da ɗakinsa? Tukunna ma mai suka zo yi?
"Baby ka tashi ashe" Zulaiha data shigo falon da ƙaramar kula a hannunta ta faɗa tana masa murmushi. Kallo ɗaya ya mata ya juya ciki haɗi da rufo ƙofa sai ta ajiye kular hannunta ta bi bayansa ɗaya daga cikin ƙawayenta ta ce
"Amma Zully baki da M, dama yana ciki shine kika kawo mu nan gashi mun saki baki muna ta zuba har Billy tana cewa zata shiga tayi kashi ashe Allah ya rufa mata asiri"
Dakatawa tayi tana ware ido ta ce
"Hirar me kukayi?"
"Ke labarin duniya ne kawai ba wani abu ba" wata mai kama da yan sholisho ta faɗa. Sai ta sauke numfashi ba tareda ta sake cewa komai ba ta shiga ɗakin.
Ƙarar ruwan da taji yasa ta zauna tana jira ya fito, ya mata kallo ɗaya ya wuce gaban mirror bayan daya fito daga ɗakin baƙin ciki goma da ashirin, shigen atamar jiya ce a jikinta, ashe ba leda bace kawai munin da atamfar tayi a idonsa ne ya sa ya ganta kamar ledar. Tashi tayi ta matsa kusa dashi ta rungume shi ta baya tana cewa
"Wai me ya faru ne kake ta ɓacin rai Baby?"
Ya tureta, bata haƙura ba ta ƙanƙameshi tana shinshinar jikinsa kamar wata mayya tana cewa
"Baby haba mana, kasan dai babu gurbin fushi a fuskar sabon ango"
Janyeta ta sakeyi bayan daya juya ya fuskanceta, so yake ya tuhumeta akan daren jiya. Ya zura mata ido, tabbas shi shaida ne Zulaihar dake gabansa a yanzu ba Zulaihar daya sani a baya bace akwai sauye-sauye da yawa a tattare da ita amma bai taɓa zaton bayan sababbin ɗabi'u da halaye da ya fuskanta a tareda ita ba harda na mutunchi da tarbiyyar da ya santa da su tun usuli. Gefe ya ɗauke kansa kafin ya buɗe baki ya fara magana sai dai a maimakon kalaman da suke kan harshensa sai yaji wani sautin daban, ya ɓige da cewa
"Wane irin raini da wulaƙanci ne ya sa zaki kawo mun wasu banzaye ɗaki Zulaiha?"
Ta haɗe fuska ta ce
"Ba banzaye bane ƙawaye na ne, kuma walima suka zo mun can falo na ya cika kuma su ɗin ko cikin ƙawayena na daban ne shiyasa na kawo su nan" ta bashi amsa tana kallon idonsa babu shakka balle tsoro.
Duk sai ya zama confused, ba abinda yake so ya tambayeta ba kenan bai kuna san sanda ya canza shawarar yin hakan ba amma kuma amsar data bashi a yanzun ta sake kashe shi da mamakinta har ya rasa abinda zai sake ce mata. Daƙyar ya iya cewa
"Su fita, ba su kaɗai ba ki sallami duk wata mace da kika tara mun a cikin gida kar na fito na tarar da ko mutum ɗaya idan ba haka ba" ya mata kallon data fahimci tsaf yana nufin zai yi rashin mutunchi ne.
Guri ta samu gefen gado ta zauna tayi ƙasa da kai kamar dagaske ta shiga cewa
"Tun daka shigo jiya kake ɓacin rai tamkar wanda zai shiga kabari, bama jiya ba, tun bayan da aka ɗaura mana aure ka canza. Gaba ɗaya ka zama wani abu daban da yanda na sanka, duk tarin alƙawarurrukan da ka yi mun na farinciki da kulawa idan na zama taka babu ɗaya daga ciki da naga yiwuwar faruwarsa sai wulaƙanci da ƙasƙanci da kake nuna mun.
A daren farkonmu Bilal haka ka tsallakeni kayi tafiyarka falo ka kwanta baka damu da wane hali nake ciki ba tunda ka rigada ka samu biyan buƙatar ka shikenan duk kuma nayi haƙuri na jure duk hakan bai yi maka ba yanzu so kake yi ka tozarta ni a gaban ƙawaye na ka ƙarasa nuna musu cewar bani da mutunchi ko daraja a gurinka ko?
Ni ba zan koresu ba amma kai ban hanaka ka fita ka koresu ba sai dai kafin nan ka fara sallamata dan ba zan iya wannan rayuwar ba" ta ƙarasa tana fashewa da kukan da ya jishi har tsakiyar ransa. Bai san sanda ya durƙusa gabanta ba dukda ya kasa ce mata komai ita kuwa kamar wacce ya saka bulala yana duka haka ta ringa kuka irin me shassheƙar nan tana nanata sai ya saketa tunda dama ya aureta ne dan ya wulaƙantata ba sonta yakeyi ba.
"Mai yasa kika ɓoye mun kin rasa budurcinki a waje?" Ya tattaro duka ƙarfin guiwarsa ya amayar da abinda yake cikinsa. Lokaci ɗaya kukanta ya tsaya ta ɗaga kai da sauri ta kalle shi da firgicin da ta kasa ɓoyewa kafin kuma ta sauke kai kamar munafuka ta sake fashewa da kukan daya fi na farko tausayi da narka zuciya. Cikin kukan muryarta na rarrabewa ta ce
"Ban sani ba"
"Kamar ya baki sani ba?" Ya faɗa cikin fushi sai dai kuma sautin muryarsa a ƙasa. Ta kife kai jikin gado tana cigaba da kukan da wanda bai san dawar garin ba dole ya tausaya mata kafin ta ce
"Ina shekaru bakwai a duniya wata rana Ummanmu ta aike ni da daddare siyo maganin sauro ruwa ya sakko na fake a wata rumfa, ban san wanene ba ban kuma san mai ya faru da ni ba amma Umma ta ce sai da akayi nemana na kwana uku kafin aka sameni a Asibiti kuma ma'aikatan Asibitin sun ce wata mata ce ta kaini tace musu tsintata tayi suka ce ba zasu karɓe ni ba sai ta zo da yan sanda shine ta ajiyeni tace zataje ta dawo daga nan basu sake ganinta ba kuma basu san daga wace unguwa ta kawoni ba balle a bayar da cigiya. A dalilin haka har lalurar yoyon fitsari na gamu da ita daƙyar da taimakon Allah na samu lafiya" ta sake rushewa da kuka.
Bilal da jikinsa yayi laƙwas yayi shiru yana kallonta tausayinta mai tsanani ya shiga ratsashi. Har ransa yaji ya yarda da abinda ta ce ya faru da ita, ya ɗagota jikinsa yana cewa
"Me ya sa baki taɓa faɗa mun ba?"
"Umma ce tace ba sai na faɗa maka ba, wai abun ya daɗe kuma ina yarinya lokacin"
Ya ɗago ta yana cewa
"Shikenan, amma ya kamata muje asibiti gaskiya a dubaki dan.." sai kuma yayi shiru, ta ce
"Saboda me?"
"Bana tunanin an dubaki da kyau a wancan lokacin ta yuwu kina buƙatar ɗinki" ya ƙarasa a hankali.
Kusan minti goma ya ɓige da rarrashinta dukda har ransa yaji ya gamsu da maganarta amma kuma ƙuncin da yake ji a zuciyarsa bai ragu ba dannewa kawai yakeyi yana rarrashinta. Ganin tana nema ta canza musu akala daga rarrashi ya saka ya tureta yana ɓata fuska. Bata ja ba itama ta kama kanta ta bar masa ɗakin babu kowa a falon dan suna shigewa ɗakin suka tattara suka koma can falonta.
"Kinga abinda na faɗa miki ko? Sai da nace kiyi ɗinki kika ce ba haka ba, anyi ɗinkin ma ya Allah ya cika wanda ma basu taɓa aure na suke ganewa balle shi toh yanzu mai kika ce masa?" Suwaiba ta faɗa taba zare ido bayan da suka shige banɗaki Zulaihan ta faɗa mata yanda sukayi da Bilal.
Sai da ta yarfe gumin da ya tsattsafo mata kafin ta labarta mata ƙaryar data shirya masa, Suby ta buɗe ido da mamaki ta ce
"Kuma ya yarda?"
"Hmmm ya yarda mana, wlh ni kaina nayi mamaki yanda ba jeka ka dawo lokaci ɗaya ya sakko bakiga yanda tausayina ya rufe shi ba" cewar Zulaiha. Suby ta zauna kan WC tana cewa
"Taɓ, kuma ba dai kawai shiru ya miki ba Zully?"
"Ke wlh ya yarda, in sa bai yarda ba na sani ba zaiyi shiru ba sai ya sake cewa wani abun ko kai tsaye ya ce ƙarya nakeyi. Yanzu dai ya ce zamuje Asibiti ayi mun ɗinki shine ma naji tsoro kar na je ko setup zai yi mun su tona mun asiri" Zulaiha ta faɗa muryarta da fuskarta suna nuna damuwa. Suwaiba ta ce
"Sai ta yuwu, amma ai ba zaki bari haka ta faru ba idanma niyyarsa kenan. Yanda kikayi wasa da hankalinsa a farko haka zaki ƙarasa wasan, ke zaki faɗi Asibitin da zakuje ko ma kawai ki kira Nurse Binta tazo gida ta miki baki alaikum idan ya nuna ba haka ba kice masa idan kukaje Asibiti ai zai zama kamar tonon asirinku in ma kuma Asibitin dai za'aje ba za'ayi a gidan ba to kuje in da take aiki asirinki a rufe babu wanda zai ji bare ya gani".
"Shiyasa nake sonki ƙawata haka za'ayi" Zully ta faɗa tana bata hannu suka tafa Suby ta ce
"Toh sai ki kama kanki ki kuma dakata karki sake shafa masa maƙale mata in ba haka ba wlh ya harbo jirginki da wuri"
"Yo ko baki faɗa ba dama ai ba zan sake ba" ta bata amsa.
Kafin la'asar ta sallami jama'ar data tara duk niyya sukayi har dare su sha budurin da basu samu sunyi ba ita da ƙawayenta a gidan dan dama bata gayyacesu yinin da akayi jiya ba tace su bari sai yau ɗin sa zo gidan tayi order abinci mai rai da lafiya kuwa ga snacks da lemuka iri iri suka ci suka sha sunata iya shegensu duk a zatonta Bilal ya fita dukda motarsa tana nan amma jin shiru tun bayan data kai masa kayan kari ya saka ta ɗauka ya bar gidan ne.
Su Suby ne Zahra kaɗai sukayi saura sai da suka tayata suka gyara gidan tsaf kafin suma suka mata sallama suka wuce lokacin Bilal ya fito zai tafi sallar la'asar suka gaisa har sannan dai fuska ba yabo ba fallasa ya ce mata zai je gidan Hajja daga can wannan ya sa su Suby suka fasa tafiya suka zauna ƙulla yanda za'ayi kar bomb ya tashi.
"Amma fa ko wannw Malami ya miki aiki wlh ya iya Zully bai ci miki kuɗi a banza ba" Zahra ta faɗa. Zulaiha tayi murmushi ta ce
"Kin san dai bana harkar Malamai"
"Haba Hajiya, a wannan karon dai ƙarya kike wlh rufe masa baki kikayi" Zahran ta sake faɗa Zulaiha ta rantse tana cewa
"Har Umma haka take cewa wai da asiri na samu Bilal kuma wlh tallahi ke ni ko a sallah bana addu'a a akansa kawai ikon Allah ne".
BILAL
Yana dab da gidan Hajja wayarsa da sai a lokacin ya kunnata tun daren jiya ta shiga ringing, ya cirota ya duba ganin Hafiz ke kira ya saka ya gangare gefen hanya ya ɗaga dan dama so yakeyi idan ya fito daga gidan Hajjan ya wuce gurinsa su ƙarasa zancen shaguna da suka fara.
Sai da Hafiz ɗin ya zolaye shi ya tambayi amarya kafin ya ce masa
"Dama maganar takardun gurin can ne, na bawa Barrister ya duba ya ce ba original bane, idan original ɗin suna kusa ka kai masa please sai ka turawa da Turad account ɗin da za'a saka kuɗin idan kuma a wanda yake da shi ne sai ka kirashi a waya ka gaya masa kawai".
Mamaki ne ya rufe shi jin abinda Hafiz ɗin ya faɗa, takardu ba Original bane kuma kamar yaya? Cikin duburburcewa ya ce
"Kamar yaya ba Original bane? Anya ya duba su sosai kuwa?"
"Ka dai san in dai aiki ne Barrister Umar ya san aikinsa, so tunda ya ce papers ɗin nan ba original bane na yarda, amma idan kana da ja akan hakan kaje ka same shi idan ya so sai kuje tare gurin waɗanda ka siya idan ma kuskurensu ne duk za'a gane" Hafiz ya sake faɗa daga nan kuma ya masa sallama.
Ajiye wayar Bilal yayi y dafe stirring zufar tashin hankali na keto masa. Ya ma za'ayi ace takardun shago ba original bane bayan da shi akayi komai akayi sealing deal, shi ya biya kuɗin kuma a hannunsa ya karɓe su ko Jalilar gani kawai tayi amma daga na gidan har waɗannan ɗin a hannunsa suke bata taɓa riƙe su ba.
Wayar ya ɗauka ya shiga kiran Kamalu wanda ya musu hanyar shagunan cikin rashin sa'a aka ce wayarsa a kashe. Fasa zuwa gidan Hajjan da yayi niyya yayi ya juya ya tafi gurin Barrister Umar, yayi shiru yana kallon takardun daya baje masa, nasa da wasu yana nuna masa banbancin original takardu da kuma nasa da ya ce forging ɗin su akayi.
"Shiyasa ake cewa idan zakuyi cinikayya ku ringa saka expert da suka san kan abun amma saboda ɗan kuɗin da zaku biya sai ku gwammace kuyi daga ku sai dillalai bayan dillalan nan wasu marasa tsoron Allahn property ɗaya sai su siyarwa sama da mutum biyar sai dai wanda yafi ƙarfi ƙarshe yayi nasara akai. Yanzu dai gaskiya waɗannan takardun naka da su da takardar tsire basu da banbanci tun wuri kuma kayi abinda ya kamata kafin su sake siyarwa da wani su bashi takaddun gaske" Barrister Umar ya faɗa.
Da wannan sabuwar damuwar Bilal ya koma gida dan gaba ɗaya ya rasa mai ya kamata yayi gashi wayar Kamalu a kashe ya kuma je har inda yake zama an ce baya nan wai yayi tafiya kuma basu san lokacin da zai dawo ba.
Gida ya wuce ya birkice takardunsa ya fito da na gidan daya siya bayan ya siyar da asalin gidan Jalilah. Zama yayi ya duba takaddun tsaf yana tuna abubuwan da Barrister ya nuna masa da suke nuna banbancin original da fake takaddun, ya sauke ajiyar zuciya mai ƙarfi bayan daya tabbatar na hannun nasa original ne. Tunani ya shiga yi to na gidan daya siyar fa? Suma fake ɗin aka basu ko kuwa na gaske ne? Sai kuma ya taɓe baki a fili ya ce
"Oho koma wannene can su ta shafa tunda ni dai na rabu dasu" wannan ya ɗan samar masa da nutsuwa har ya shiga gurin Zulaiha da yana shigowa ta taho tana masa oyoyo amma ko kallonta bai yi ba ya wuce ɗakinsa bata yi zuciya ba kuma ta bishi ta ajiye masa ruwa da lemo mai sanyi dama ya tarar da kwanukan abinci amma ba ta su yake ba sai da nutsuwar sa ta dawo kafin ma ya tuna da yana jin yunwa.
Washe gari kuwa kamar yanda ya ce da safe ya ce ta shirya suje Asibiti dan daren jiya duk yanda ta so ta kama kanta yanda Suby ta ce kasawa tayi amma da yake batayi amfani da turaren kan tace ba shiyasa har ya samu damar tureta wai ya gaji bacci yake so yayi. Abun ya mata ciwo ƙwarai amma ta danne tara shi zatayi zata rama komai sala sala da zarar komai ya sake hawar mata saiti. Tayi dana sanin ƙin jin ta Suby da tun farko tace tayi ɗinkin ciki da wajen a ganinta iya gyara da kayan matsin da tayi amfani dasu sun isa amma gashi an samu akasi.
Marairaicewa tayi ta tsarashi akan idan sukaje Asibiti ai tonon silili zai yi mata. Ta ce zata kira Binta wacce ta ce masa Yayar Suby ce tazo gida kawai ta mata amma ya ce Aa, daga ƙarshe dai sukaje Asibitin da Bintan take aiki dama kuma tun jiya sun sanar mata dan haka dama a shirye take ko ta kirata taje gidan ku suje Asibitin su sameta tayi mata ɗinkin tace mata
"Wannan uban buɗewa ke kuwa Zully kamar wacce ta haifi yaya goma? Gaskiya kinyi ganganci ki kuma godewa Allah dan mutumin nan yana sonki in da wani tun jiyan sai dai ki ƙarasa daren a gidanku wlh".
Manage this please bana jin daɗi wallahi 😭😭
*KURA A RUMBU*
*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*
*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya naira 800, biya a asusun*
*7061838488*
*Opay*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*
*PAGE 54*
Jinyar stitches ɗin Zulaiha ta saka Bilal baya fita ko ina idan ba masallaci ba, duk ayyukan gidan shi yakeyi, sannan ya kula da ita a ɗan taƙin lokacin kuma ya ɗan fara samun nutsuwa daga tsoron sababbin halayen da ya ringa gani a gurinta tun bayan da aka ɗaura musu aure. Ranar data kwana uku ƙanwar Ummansu Anty Habi taje gidan ta kai mata gamje gamjen magunguna da ta ce na Aljanun da suke shafarta ne. Shi ya ringa jigilar dafa mata na wanka safe yamma kuma ya hura mata coal tayi turare, maganin na sati ɗaya ne ranar data cika satin tana yi kuwa Aljanun suka tashi.
Lokacin ya fita siyo kayan miya ya dawo ya tarar da ita su Suby sun daddanneta tana wasu abubuwa suka ce masa wai a haka suka tarar da ita suma. Dukda dai yayi mamakin ta inda suka shiga gidan tunda ya rufe daya fita ita kuma sun ce sun sameta ta hau iskoki to waya buɗe musu ƙofar?
Haka ya fita can masallaci ya samo wanda zaiyi mata ruƙiyya, suka ringa kafa masa Sharuɗan kar a ringa ɓata mata rai, kar ayi mata faɗa da sauransu in ba haka ba zasu dawo daga haka dai suka fice sai kuma suka riƙe mata ƙafa, sati biyu taci tana jinya kafin ta ware gaba ɗaya suka durfafi sabuwar rayuwar amarci tunda ɗinki ma ya warke, duk yanda take ƙoƙarin dannewa kar tayi abinda zai sake jefa zargin wani abu a zuciyar Bilal ɗin ta kasa.
Ranar da suka sake gamuwa dukda shi ya fara nuna buƙatar abun amma tun kafin ayi nisa taga ya canza, karsashin daya fara