Showing 48001 words to 51000 words out of 257873 words

Chapter 17 - KURA A RUMBU HAUSA NOVEL

23 Oct 2025

490

kwanta. Hakan da yayi ya nuna mun ya huce daga fushin jiyan, amma ni kuma cin mutunchin da ya mun fa? Shikenan a ganin sa komai ya wuce?

"Amma Bilal abinda ka mun jiya kana ganin ka kyauta?" Na faɗa murya ta na karyewa. Se ya tashi zaune yana kallo na yace
"Kin sani bana son dawo da abinda ya wuce karki ɓata mun rai Halima" daga haka ya miƙe ya shige ɗaki ya barni a zaune na rakashi da ido. Duk yanda naso na ƙarfafi kaina na nunawa Bilal jin zafin abin da ya mun na kasa, ganin ya sakko kawai se na lallashi zuciyata nima na haƙura. A haka azumi ya fara ja har an kai na goma. Daƙyar nayi guda huɗu saboda yanda lafiya tayi mun ƙaranci. Ciwon mara da ciwon kai suke damuna ga amai ba dama na shaƙi ƙamshin abinci ko banyi aman ba nayi ta kakari kenan. Munje chemist da Bilal suka rubutamun magungunan malaria harda allura ta kwana uku an mun amma banji sauƙi ba. Ganin lokacin al'ada ta ya wuce yasa na fara zargin ko ciki ne dani.

Ranar da aka kai azumi na goma tun yamma dama yace mun idan an sha ruwa zamu je gidan su mu gaishe su haka yasa dana tashi yin abin shan ruwa nayi da ɗan yawa zan ɗibar wa Hajjansu. A raina na raya se yayi magana dan kullum ne se yayi mitar ina dafa abinci yana yin yawa da zarar yaga kwanuka ze fara buɗe buɗe yana mitar duk cikin mu zamu cinye wannan a hakan ma ba wani abin kirki nakeyi ba saboda bana jin daɗi baya wuce abu biyu me dan sauƙin saraffawa na buɗa baki se kuma abinci da za'a sake ci da kuma lokacin sahur amma haka ze yi ta surutun nayi da yawa kuma a hakan ze cinye tas har ya ringa cewa beyi sahur me kyau ba. Dama ƙiri ƙiri ya hanani yin kunu da ƙosai na sadakar da nayi niyya wai da me zanji?

A kwando na jera kwanukan abincin dana zuba, ina jin kamar zazzaɓi ze rufe ni amma na daure, a sabon mashin ɗin daya buɗe shekaran jiya muka fita. Tun lokacin biki yace mun ya siyar da mashin ɗin sa se yanzu ya sake siyan wani. Muna tafe muna hira gwanin sha'awa har muka isa gidan a raina nayi gulmar yanda bece komai ba daya ga basket ɗin abincin,
kamar Hajiyar su zata goya ni haka ta ringa nan nan da ni. Taji daɗin abincin dana kai mata, ina zaune ta soya mun ƙosai tace tasan da yawan mutane sun fi son ƙosai da an sauke daga mai shiyasa da yace zamu zo ta ajiye ƙullin. Sosai kuwa naci ƙosan da kunun tsakiya a nan take gaya mun ai geron da waken ma daga gidan mu aka kawo musu harda buhun shinkafa dana sugar da pastar mangyaɗa. Se gurin goma saura muka bar gidan, a hanya naga gurin gasa tsire tun daga nesa naji raina ya biya dan haka nace masa dan Allah ya tsaya ya mu siya ba musu kuwa ya tsaya ya siya muka wuce gida.

A haka aka ƙara azumi biyar, tun washe garin da muka je gidan su nake jira naji yace na shirya muje gaida nawa iyayen amma shiru. Har Mama se da ta gaji ta mun magana akan yaushe zamu zo? Na ce mata bani da lafiya ne amma zamu zo, Allah sarki uwa washe garin da mukayi maganar kuwa se ga Imam da Amira da Nabila yar ƙanwar Abbanmu Anty Surayya da tazo hutu gidan Mama tace su zo su dubani. Ran da aka kai azumi na sha biyar ɗin tun asuba na masa zancen se yaushe zamu je gidan mu ne?

"Akwai abin da nake jira ne kin ga ai ba daɗi muje musu hannu haka babu wata tsaraba" amsar daya bani kenan. Se nace masa
"Yanzu ita Hajja ba haka muka je muka gaishe ta ba bamu kai mata komai ba suma gaisuwa ce ai ba wani abu aka ce dole se an kawo ba". Kamar baze yarda ba har na fitar da rai kuma bayan la'asar ina ƙoƙarin ɗora abin shan ruwa yace na shirya kawai ya kaini gidan. Sosai naji daɗi, da muka je be shiga ba ya ce mun se ya dawo ɗauka ta tukunna yanzu sauri yake ana jiran sa a wani guri. Mama na kitchen da Nabila suna aiki ta ringa kallo na da mamaki na rungumeta cikin jin daɗin ganin ta dan rabo na da gidan tun zuwan da nayi akan registration ɗin NYSC. Abba kansa se da ya tsokane ni yace dama gobe suke shirin zuwa ban haƙuri ace azumi har ya raba basu ga ido na ba gara suzo suji wane laifi sukayi haka.

Ina rufe fuska nace
"Ai kullum ina kiran ku a waya Abba"
"Haka ne, amma muga juna ɗin ma ai da daɗi ko Halimatu? Ko da yake ke fa tunda kika samu Bilal shikenan kika manta da kowa" Abban ya sake tsokanota se kawai na tashi na koma ɗaki dan duk se naji ban kyauta ba na kuma ƙudire a raina zan gyara hakan ba zata sake faruwa ba. Cikin farin ciki nasha ruwa da yan uwana, can ƙasan raina ina tunanin ko Bilal ya ci abinci? Ko dame ya karya azumin sa oho? Ana idar da sallar asham Mu'azzam yace mun
"Ga matsolon mijinki can a waje". Na galla masa harara kawai ba tare da nace komai ba. Tare suka shigo da Abba, a can falon ya zauna bayan sun gaisa da Mama na shiga kitchen na haɗa masa abinci na bawa Amirah ta kai masa, se da ya gama kafin mukayi sallama muka tafi kunya duk ta dabaibayeni jin Mama ta fahimci ina da ciki har tana tambayata wata nawa ne nace mata ban sani ba tun da bamu je asibiti ba pt test kawai nayi naga positive dan ko Bilal ma ban gayawa ba.

"Ya dai kamata kije gidan Labiba tunda kalar naki hankalin be nuna miki ba har yanzu" Mama ta faɗa sanda ta rako ni bakin ƙofa. Tunda nayi aure ko sau ɗaya banje gidan Anty Labiba ba ita ma kuma tun washe garin da aka kaini bata sake komawa ba wata tara kenan muna waya muna chat. Har ga Allah kawai ina jin kunyar abin da na mata akan zancen aure na da Bilal ne, duk da ko a fuska bata nuna mun komai ba amma nasan Anty Labibar da na sani babu yanda za'a yi nayi aure ta ɗauki wata tara bata tako gida na ba har idan ba da wani abu data riƙe a ranta ba ni kuma bana son naje ta tayar da maganar shiyasa kawai nake gudun zuwa gidan nata. Kuma muna haɗuwa a gida yaranta ma kusan duk sanda su Amira zasuje mun tare su ke zuwa dasu.

Amsawa Mama nayi da zanje in sha Allah na wuce tana sake jaddada mun na tabbata naje asibiti bata son sakarci. Washe gari nayiwa Bilal zancen zanje gidan Anty Labiba, be musa yanda ya saba ba yace duk sanda na shirya na je, take na kirata wayarta a kashe ina hawa whatsapp na ganta online dan haka na ce mata gobe zanzo in Allah ya kaimu. Amsar data bani
"Bana nan" na ringa juya maganar, bata ma tambayi ƙarfe nawa zanzo ba ko wani abu kawai tace bata nan. Da take cewa in har na auri Bilal zata yanke zumunta dani ashe dagaske take kenan? Take shaiɗan ya shiga mun famfo, na watsa hannye a fili nace
"Kin huta ai. Bilal dai da bakya ƙaunar gani na dashi shi ɗin Allah ya zaɓa mun muyi rayuwa tare se haƙuri". Shikenan naci gaba da sabgogina. Ganin har an kai azumi na ashirin da uku Bilal be bani ko ƙyalle da sunan na siyi kayan sallah ba na cire rai da zeyi mun ban kuma tambaye shi ba saboda hidimar daya zo masa katsahan ƙanwar sa da akayi bikin mu tare ta haihu haihuwar kuma tazo mata da matsala ƙarshe se CS aka mata mijin dake bashi da mutunchi tunda ta kwana ta wuni tana labor washe garin ya tattaro ta ya kawo ta gida su suka yi duk wata ɗawainiyar asibiti har aka ciro mata babyn kwana uku kenan ko zuwa ganin su beyi ba. Bilal ne ya biya kuɗin aikin yayyen sa mata kuma suka haɗa mata kayan barka da sauran abubuwan buƙata da suka tashi suka yiwa yaron huɗu ba da sunan Babban Yayansu da suke uba ɗaya shine ya bada ragon da aka yanka masa.

Cikin kuɗin da Abba ya tura mun tun washe garin da naje gida na siyi lace guda biyu na haɗa da atamfofi biyu cikin na lefe da ban taɓa komai a ciki ba na bada ɗinki. Na san Mama bata san ya bani kuɗin ba dan haka ni ma ban mata zancen ba, da sauran kuɗin nayi sauran buƙatun da nake dasu ciki harda zuwa asibiti na buɗe file na anti natal dan da na yiwa Bilal magana ina so naje asibiti cewa yayi me zanje yi bayan ga magunguna nan an bani kuma na samu sauƙi tun da a zahiri babu abinda yake damu na banda amai se zazzaɓin dare gari na waye wa kuma zan shiga sabgogi na idan naji garau nayi azumi idan naji bazan iya ba na sauke. Saboda ina so nayi masa ba zata akan cikin se kawai nace masa ulcer se ta tasar mun ya siyo mun Omeprazole da gestid a chemist yace na ringa sha.

Cikin ikon Allah azumi ya ƙare anyi sanarwar ganin watan sallah ya tsaya, kasancewar sallah ta ta farko a gidan aure yasa naji ina sha'awar nayi abincin sallah nima yanda naga anayi. Dake tunda Fadila ta haihu Bilal suke ta zirga zirga tsakanin gida da asibiti wata ran se tara yake dawowa yau ɗin ma yana gida aka kira shi jikin yaron ya rikice dake da jundice aka haife shi shine ya fita suka mayar dashi asibiti. Har mamaki nakeyi yanda ya damu sosai da lafiyar ƙanwar tasa ba kuma ya ƙyashin kashe kuɗi, da na tambaye shi ina mijin ta da suke ta ɗawainiya da ita haka ma cewa yayi shi ba ta mijinta su keyi yanzu ba dan idan ta mutu su suke da asara ba mijin ba jira sukeyi ma a ƙare azumi suyi ƙarar sa ya saketa ba zata koma ba. Ban tsawwala da jin dalili ba nace Allah ya rufa asiri kawai muka bar zancen.

Dake muna da kaji da jan nama ba'a fi kwana uku daya siyo su ba kajin guda huɗu ne manya manya se naman shima da ɗan auki se na ɗibi kaji uku na samu yaro ya yiwo mun cefanen miyar taushe na jiƙa farar shinkafa akan zanyi waina da sinasir. Tun daren na haɗa miyar ya rage ganye kawai zan zuba na saka ta a freezer na kwaɓa meat pie shima na haɗa na deɓi kaɗan na soyawa Bilal na saka sauran a fridge. Ina da samosa da spring rolls dama nace se na haɗa da safen na soya su tare. Na gaji lilis se goma saura na gama gyaran gida da wanke wanken abubuwan dana ɓata dan har zoɓo na haɗa, ina wanka Bilal ya dawo daga ganin fuskar sa na san babu lafiya nan yake sanar mun ɗan Fadila ne ya rasu. Na taya su jimami har nace zan kira ta lokacin yace na bari se da safe, haka nan muka kwana yanda Bilal ya damu kamar ɗan cikin sa ya rasa. Na ringa ayyana yanda zeyi farin ciki idan ya san ya kusa samun nasa ɗan shima.

Washe garin da wuri ya shirya dan zasuyi jana'izar yaron kafin lokacin sallar idi. Nima kafin ƙarfe tara na gama abincin sallah na, na zuba na gidanmu harda na Anty Labiba na ware na gidan su Bilal sannan na fitar da na maƙwafta. Sayyadi almajirin Maman Yusuf na bawa kuɗin Adaidaita ya kai na gidan mu dan ya san gidan ina aiken sa, se gurin sha ɗaya Bilal ya dawo tare da abokanan sa su uku. A falon sa na aje musu abinci suka ci se da akayi azahar suka tafi yace mun na shrya daya dawo daga sallah zamu tafi can gidan. Tsaf naci kwalliya da ɗaya daga cikin laces ɗin dana ɗinka. Yaron cikin jikina yasa fatata ta goge nayi shar dani ga yar kiɓar dana ƙara ta sake fito da albarkatun jikina. Hijab daya dace da kayan na saka dan kar suce suna zaman makoki ni kuma nayo kwalliya. Yana shigowa ya ɗaga ni ya rungumeni, se da yayi kissing goshi na ya haɗe hanci na da nasa yana kallon cikin ido na yace

"Kin san me yasa name ƙara sonki kullum?" Na girgiza masa kai alamar aa, se ya maida kaina ƙirjin sa yace
"Baki taɓa bani kunya ba. Duk sanda zan cika baki akanki se kin aikata fiye da yanda na kwarzantaki. Kasada kawai nayi da su Mansur suka ce zasu biyo ni suci girkin amarya. Nasan ba muyi zancen za kiyi abincin sallah ba amma sanin da nayi tunani na dana Halims a tare suke tafiya banyi shakku akan zaki fitar dani kunya ba se gashi harda snacks. Ke dai Allah yayi miki albarka ya barmu tare kinji my Halims" ya ƙarasa yana brushing lips ɗin sa akan nawa. Na ringa murmushi kamar wawuya jin ya yaba abinda nayi. Se da muka ɓata lokaci a nahiyar soyayya dan se da ta kaimu da canza wanka kafin mukayi sallar la'asar mukayi sabon shirin fita. Cewa yayi cikin sa ya zazzage wai dama ba wani abin kirki yaci ba duk su suka cinye. Na sako masa sinasir guda ɗaya yana ci yace

"Wato yarinyar nan kuɗi ne dake, kikayi ɗinki sallah Allah sarki ni da tsohon kaya naje idi ga kuma daƙwalen kaji kin zuba mana a miya ai se ki bani barka da sallah kuma na samu na zuba mai a mashin". Se da nayi far da ido kafin nace

"Ka so tsokana dai kawai da kayan da kajin naga duk kai ka siya, ni sarrafa su kawai nayi". Be sake magana ba daga yanda naga fuskar sa ta canza lokaci ɗaya kuma nasha jinin jiki na se dai duk son na hakaito me ze kawo ɓacin ran sa lokaci ɗaya haka na rasa se kawai na kama kaina nayi shiru nima. Sanda muka isa gidan su lokacin Abubakar ya dawo shima ya sauke kwanukan abincin da na bashi ya yiwo musu gaba dashi,
"Duka kajin kika dafa kenan?" Ya faɗa a saitin kunne na daidai sanda Hajja ta buɗe flask ɗin miya.
[5/18, 14:41] Buhainat: *KURA A RUMBU*
*(Based on true life event, some parts are fictional to spice up the story)*

*LABARI/RUBUTAWA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WOMEN OF WORDS WRITERS ASSOCIATION (WOW)*
*Whatsapp 07061838488* *Arewabooks @Maryamfarouk01*
*Wattpad @MaryamahMrsAm*
*TikTok @Maryamfarouk_Ummu-mahir Novels*

*Ban yarda wani ko wata ya juya mun labari ta kowacce siga ba tare da izini na ba*
*Kuɗin karatu yana wakiltar mutum ɗaya ne, kiji tsoron Allah karki ɗauki hakkina ta hanyar fitar mun da littafi*
*KURA A RUMBU littafin kuɗi ne, a biya naira 800, biya a asusun*
*1840175439*
*Access bank*
*Maryam Farouk, se a tura shaidar biya a lambar Whatsapp ta sama*

*PAGE 14*

Afuwan kun jini shiru. Wadanda suke cikin comment section group na bayar da uzuri.

A ɗarare na ƙarasa yinin cike da taraddadin yanda zamu kwashe da Bilal idan mun koma gida. Se da akayi magriba ya turo mun text a waya in fito mu tafi. Jikina ya sake yin sanyi, haka nayi sallama da Hajja da sauran yan gidan su tana ta mun godiyar abin arziƙi da tace an kawo musu daga gidan mu cikin azumi ga kuma turmin atamfa dana kai mata dama yanzu kuma na kaiwa mejegon itama Atamfa da wani lace cikin ɗinkunan biki da aka mun sakawata ɗaya ranar naje gidan dashi tace ya mata kyau ni na manta ma da munyi maganar se bayan data haihun ta roƙe ni in bata tayi fitar suna dashi.

Tare da Nasir na same su tsaye jikin motar Nasir ɗin, muka gaisa a mutunche Bilal ya shiga mzaunin gaba hakan yasa na fahimci Nasir ɗin ne ze sauke mu gida. A hanya suna ta hira da zarar Nasir ya sako ni se naji Bilal ya ɗauke wuta gane hakan yasa ko da Nasir ɗin ya sake tsomani cikin maganar nayi kamar ban ji shi ba. Ni kaɗai na sauka ya miƙa mun muƙulli ba tare da ya kalle ni ba na wuce ciki ina tunanin ina kuma zasu je kuma har se yaushe ze dawo amma babu fuskar da zan iya tambayar sa. Be shigo gidan ba se goma da kwata, ina zaune a falo naji tsayuwar mashin ɗin sa, ban motsa ba nasan cikin biyu ko dai ya buga ko ya kirani a waya tun da be fita da key ba ilai ko se ga kiran sa a maimakon yanda na saba daya kira in tashi naje na buɗe Get ɗin tunda nasan kiran na menene se kawai na amsa wayar.

Da murya kamar me bacci nayi sallama, ina jin sa yaja tsaki kafin yace
"Zo ki buɗe" daga nan ya katse wayar. Se da na koma ɗaki na ƙara turare kamar me fita zance sannan na saka hijab na fita. Ban san na ƙarawa kaina laifi ba, ina buɗe ƙofar ƙiris ya rage ya ture ni da tayar mashin ɗin ya shigo ciki, se da na kulle ƙofar na bi bayansa yana kafe mashin ɗin ya juyo kamar ze rufe ni da duka yana cewa
"Tsabar kin mayar dani ɗan iska na kiraki amma kiyi zamanki se yanzu kika ga damar zuwa ki buɗe kofar ko?"

Kallon sa kawai nayi takamaimai ni ban fahimci dalilin wannan hasalar tasa ba. Fuuu ya wuce ɗakin sa, har na bi shi se kuma na juya na shige falo ina ƙarfafa kaina akan bazan bi ta kansa ba tun da dai ba wani abu na masa ba. Sinasir ɗin dana ɗumama na saka masa guda ɗaya da yar miya a bowl na haɗa da tea dana rigada na dafa masa na ɗora komai a

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login