Showing 213001 words to 216000 words out of 257873 words

Chapter 72 - KURA A RUMBU HAUSA NOVEL

23 Oct 2025

496

da shi ya sakeshi sai ƙananan tsaki da ya ringa saki, bata damu ba ta cigaba da shafashi a ƙoƙarin mayar dashi kan network amma sai kawai ya tureta lokacin da wayar sa tayi ƙara. Abun ya mata ciwo matuƙa, tana sauraron wayar da yakeyi data gane da Hajja ne kuma masifa take masa dan sai bata haƙuri yakeyi kafin ya kashe bayan ya ce mata gashi nan zai zo gidan yanzu da yake da yamma ne.

Tayi ƙwafa ta bishi da harara sanda ya shiga banɗaki, sai kuma ta tashi da sauri ta ɗakko Humrar kiranyenta ta shafa sannan ta ɗebi maƙale mata a hannunta ta koma ta zauna tana murmushin mugunta, Tunda ba zaiyi dan Allah ba toh kuwa zai yi dan dole.

Bilal kuwa daya shiga banɗakin sakin ruwa yayi akansa dukda garin da sanyi sanyi amma bai damu ba, duk da ya san gaskiyar abinda ya sameta amma kuma zuciyarsa ta kasa karɓar abun har yanzu. Yana son Zulaiha tamkar rai, amma da zarar ya tuna cewar bai sameta a Mace ba sai yaji duniya ta masa zafi, duk sanda buƙatuwar ta ta motsa masa kuma da zarar ya tuna abun sai ya ji komai ya mutu kamar dai yanzun a matse yake ya kuma yi ƙoƙari ya kawar da tunanin amma suna farawa abun ya zo masa take yaji komai ya mutu duk yanda ya so daya daure ko dan ganin kamar itama tana so ɗin amma ya kasa.

Wani tunanin ne ya sake gifta masa wai me yasa ita bata tsoronsa?
Kashe shower yayi ya zauna akan toilet yayi shiru kamar mai jira wani ya bashi amsar. Ya tafi tunanin farkon aurensu da Halima daƙyar sai ya matsa take iya kallonsa babu riga amma ita wannan haka take ƙure shi da ido kamar mayya har lashe baki takeyi idan da ya biye mata ma da tuni tun kafin ɗinkin nata ya warke ma zata bashi kanta kwata kwata babu kunya ko jin nauyinsa a tareda ita ko da kuwa tayi ƙoƙarin nuna hakan bai san mai yasa yake ganin kamar na ƙarya ne ba.

Ji yayi kansa na nema ya fara ciwo dole ya kore tunanin ya miƙe ya shiga wanka, sanda ya fito tana kwance akan Gadon amma ya san ba bacci takeyi ba tunda bai ji munshari ba, ya wuce gaban mirror zai ɗauki wayarsa ya bar mata ɗakin hancinsa ya fara shaƙo masa wani ƙamshi, kansa ya sara, kamar wanda aka ja da igiya haka ya tafi kamar kuma waccen ranar yau ɗin ma haka ya ringa aiki tun yana na jin daɗi har ya koma na wahala sai gashi yana kuka wiwi duk kuma yanda ya so ya bari abu ya gagara sai da ita da kanta ta gaji kafin ta yakiceshi daƙyar ta gudu banɗaki ta kulle ƙofa.

Bilal kuwa kwanciya yayi riƙe da ciki yana juyi cikin azaba, ya gaji amma kuma so yake yayi abun, daƙyar ya lallaɓa ya fice daga ɗakin ya koma nasa ya shiga wanka, sai da yayi kusan saɓi uku har cikin hancinsa ya wanke kafin ya daina jin ƙamshin turaren a hankali kuma nutsuwa ta fara saukar masa ya fita ya kwanta akan gado yana sauke ajiyar zuciya a jere. Gaskiya ba haka kawai ba akwai wani abu dan shi dai a rayuwarsa bai taɓa gamuwa da irin wannan bala'in ba. Sai gurin ƙarfe tara ya iya tashi yayi sallar magriba da Isha'i, yana zaune ya jiyo tana ƙwanƙwasa masa ƙofa haɗi da kiran sunansa kamar na zai tashi ba sai kuma ya miƙe yana rangaji yaje ya buɗe mata.

Sum sum ta wuce ta ajiye try ɗin data shiryo masa kayan abinci akai, ba tareda ta kalle shi ba ta miƙa masa wayarsa tana cewa

"Tun ɗazu ake kira" ya karɓa yana kallonta sai kuma ya ji tausayinta yana ratsashi babu dalili. Abincin data zuba masa ya jata jikinsa suka shiga ci, jollop ɗin shinkafa taji nama ga kuma peppered chicken daban a gefe da salad sai lemon exotic babban kwali mai sanyi sosai. Sai da ya kai geji kafin ya shiga tantance abincin. Ɗanɗanon da ƙamshi harda yanda aka shirya abincin ma bai yi kama da girkinta ba.

Zulaiha bata iya girki ba bai kuma yi mamakin hakan ba domin ya fi kowa sanin daga gidan daya ɗakkota, yayi gyaran murya ya ce

"Daga ina aka kawo abinci?" Ta kalle shi a shagwaɓe ta ce
"Ni na girka mana" ɗan murmushi yayi ya ce
"Ai nasan bamu da ingredients ɗin da zakiyi irin wannan girkin, ya kamata ma a samo fridge gaskiya saboda ajiyar nama da kayan miya na gaji da siyan guntu guntun nan" daga haka ya ɗauki wayarsa ya shiga duba missed calls ita kuma ta kwashe kwanuka ta fita da su ranta ƙal.

Kiran Kamalu ya fara bi dukda yaga missed calls ɗin Hajja kusan guda goma, basu wani ja gaisuwa mai tsayi ba Kamalu ya ce masa

"An ce kayi ta zuwa nemana Allah ya sa lafiya dai"
"Eh wlh kuma nayi ta kiran layinka kullum a kashe, dama maganar shagunan nan ce na bawa lawyer na takardun ya duba amma ya ce fake ne" Bilal ya bashi amsa.

"Fake kuma?" Kamalu ya tambaya cikin mamaki Bilal ya amsa masa da
"Haka ya ce, nima nayi mamaki amma kuma dana haɗa su da wasu takardu na ga banbancin da ya ce akwai tsakaninsu da original ɗin".

"Gaskiya toh bansan a inda aka samu matsala ba dan kai shaida ne takardun nan hannu da hannu yanda aka bani su take na miƙa maka ban ko tafi dasu wani guri ba balle ace ni na canza su" Kamalu ya faɗa.

"Ai ba ina zarginka bane Alhaji Kamalu nima abun ya bani mamaki ne kaga kenan daga can gurinsu da suka siyar mana sune macutan, sun karɓi kuɗin mu ƙila zasu sake siyarwa da wasu kuma"

"Gaskiya a sanin da nayiwa Alhaji Balarabe ba zai taɓa yin haka ba, na fi shekara goma sha biyar muna harkar ƙasa da shi ba'a taɓa samun saɓani ba, amma abinda zai faru gobe idan Allah ya kaimu kazo office ka sameni sai muje gurinsa duk ma abinda ya faru sai a warware" Kamalu ya sake faɗa daga haka sukayi sallama.

Dukd dare ya farayi haka ya tafi gidan Hajja tareda Zulaiha, sai da ya tsaya a hanya yayi mata siyayyar toshiyar baki kafin suka isa gidan. Fadila na falo tana kallo ita da Abubakar shi kuma yana cin abinci suka shiga, ta gaishe shi ba tareda ta ko kalli Zulaihan ba Abubakar dai tamkar bai ji shigarsu ba sai da Bilal ɗin yayi masa magana kafin ya ɗaga kai tareda yi masa sannu a taƙaice ya cigaba da cin abincin sa.

Ɗaki ya wuce da Fadila ta ce masa Hajjan ta kwanta, ya zauna daga gefen ƙafarta yana gaisheta dan ba bacci takeyi ba kafin ta miƙe zaune fuska ba yabo ba fallasa ta ce

"Ashe kuma ka saki Halima"
Kai a ƙasa yana shafa ƙeya ya ce
"Kotu suka ce zasu kai ni Hajja ni kuma naji tsoro kar su fitar da waccen maganar shiyasa kawai na saketa".

"Ai shikenan, yanzu yaushe zaka karɓo yaran toh?" Hajja ta sake faɗa. Da sauri ya kalleta ya ce

"A karɓo yara kuma Hajja?"
"Da bar mata su zakayi shikenan an rabu kake nufi ko me?"

"Aa ba haka nake nufi ba, da niyyata dai a barsu su ƙara tasawa tunda yanzu idan an ɗakko su nan idan aka kawosu wahala zasu zamar miki" ya sake faɗa kai a ƙasa. Hajja dake kallonsa ta ce

"Au, ni kake zaton zan riƙe maka yaran ma kenan? Ita waccen ɗin daka auro menene amfanin ta? Da zuwa kawai tayi ta samu guri taci arziƙi kenan ko me?"

"Ba haka nake nufi ba Hajja" ya faɗa a hankali ta katseshi da cewa

"Ka saurareni da kyau dole ka karɓo yaran nan saboda ta hakane zaka ƙuntata mata da ita da iyayen nata kuma zamu samu damar jansu a ƙasa yanda muke so a dalilin yaran sannan itama wannan yar matsiyatan daka ɗakko ba zaman banza zatayi ba dole tayi maka wahalar yaya".

Shiru yayi ya kasa ce mata komai, Hajjan ce ta sake cewa
"Wai ina Hafizu ne kwana biyu?"

"Yayi tafiya ne kusan wata uku baya ƙasar" ya shata mata ƙarya, ta taɓe baki ta ce

"Yanzu saboda mugunta da hassada ƙiri ƙiri kaƙi kayi masa maganar Fadila ko? Tunda kai kayi mana baƙin ciki Allah ya kawo mana mai taimakonmu har gida amma ka kwaɓar da damar shine itama kake mata baƙin ciki karta samu in da zata huta har muma mu mora"

"Amma Hajja na gaya miki maganar nan ba mai yuwuwa ba ce ba, mutumin nan da matarsa yana sonta bai taɓa kallon Fadila a matsayin wacce zai iya so ba kina gani saboda rashin hankalinta ta ringa shige masa har sai da ya fahimci abinda take nufi in da yana ra'ayi ai da zai amsa amma daga haka mai ta janyo? Janye jikinsa yayi ya daina zuwa gidan nan kuma shine kike so ni na tallata masa ita gaskiya ba zan iya ba" ya bata amsa ba tareda ya kalleta ba.

Tayi ƙwafa ta ce
"Ai shikenan nan"
"Kiyi haƙuri idan na ɓata miki rai Hajja" ya sake faɗa cikin sigar rarrashi,
"Yanzu ita yaushe zata dawo ayi maganar auren?" Ta sake soko masa wata maganar, ya fahimci wa take nufi amma ya waske da tambayar wacece

"Ita shaiɗaniyar yarinyar nan mana" ta bashi amsa a fusace. Ya marairaice fuska ya ce

"Yanzu Hajja ko ni na dage zan aureta dan Allah sai ki barni nayi?"

"Akan mai zan hanaka? Dama ai abinda ya kamata kenan ko kuwa kana nufin taci banza ta lalataka sannan taƙi aurenka? Toh wlh ba zai yuwu ba" ta bashi amsa. Ya buɗe baki zai sake magana wayarsa ta shiga ƙara dan haka ya dakata ya zarota gabansa ya yanke ya faɗi ganin international number ko ba'a faɗa ba kuma ya san Jalilah ce.

Ji yayi zufa ta fara keto masa ya danna wayar a silent ya mayar da ita Aljihu ya miƙe yana kallon Hajja ya ce
"Bari naje Hajja sai gobe" ta amsa masa da
"Allah ya tashe mu lafiya" tana karantar sauyin da yayi lokaci ɗaya.

A falo Zulaiha kaɗai ya tarar tana ganinsa kuwa ta miƙe yayi gaba ta bi bayansa. Sai da suka zauna a mota kafin ta ce masa tana so taci Shawarma ta faɗa masa kuma ta inda take so. Ya kalleta da mamaki jin inda ta faɗo ɗin, kallon daya mata ya saka ta gane ta kwafsa dan haka tayi saurin cewa

"Saurayin Zahra ne yake siyo mata ya kai mata School, na taɓa ci sau biyu tayi mun daɗi sosai shiyasa na riƙe sunan gurin". Bai amsa mata ba suka tafi, tana ta sako masa hira dan ta kawar masa da tunani amma da Eh ko Uhm yake amsa mata kawai. ATM ɗin sa ya bata ya ce taje tayi order dukda yanda gurin yake cike da Maza amma yana buƙatar space ɗin ne saboda number ɗazu da ake ta sake kiransa da ita. Tana fita kuwa kiran ya sake shigowa, saida ya kashe motar kafin ya ɗaga murya can ƙasa kamar mai bacci yayi sallama.

Muryar Jalilah ta sauka raɗau a kunnensa
"Yau dai Allah yayi na sameka a waya" ta faɗa, ya sake narke murya ya ce
"Nayi kewarki Babe, mai nayi miki? Kin toshe duk wata hanya da zan iya samunki phone call, Whatsapp, IG duk kinyi blocking ɗina what have i done to deserve such punishment Jalilah?"

"Nayi blocking ɗin ka ko kayi blocking ɗina?" Ta bashi amsa da sauri ya ce
"Saɓo kikeyi kema kin san hakan ba zai taɓa zama gaskiya ba ya za'ayi nayi blocking ɗin ki?"

"Ai shikenan dai, kwana biyu? Nayi missing ɗin ka sosai" ta rage murya ta faɗa. Ya gyara zama yana cewa

"I missed you more Lily, yaushe zaki dawo?"

"Ya kamata ace jiya zan dawo sai kuma na wuce gurin Mom bata jin daɗi" ta bashi amsa

"Subhanallah, mai ya sameta? Amma da sauƙi ko?" Ya faɗa a cikin rikicewar ƙarya ta amsa masa
"Da sauƙi, kaya fa har sun kamo hanya kuma ba zasu daɗe ba dan ƙila ma su rigani isowa dan haka ka saka a gyara gurin da kace zamu mayar dashi store kafin na dawo a fara loading kamfani, sai kaga kayayyakin da muka samu abubuwa da yawa ma basu tura mana ba sai da nazo na gansu na so tare muka zo kaima na san da ka sake ganin wasu abubuwan da zamu iya ƙarawa da su".

Window aka buga ya sauke Zulaiha ta ziro kai tana cewa
"Menene pin ɗin?" Ya danne speaker wayar kafin ya gaya mata ta koma Jalilah ta ce
"Baka gida kenan?"

"Aa, eh mai kika ji?" Ya faɗa a duburce. Ta ce
"Naji muryar Mace"

"Halima ce Shawarma zata siya" yayi saurin bata amsa sai ta ce

"Allah sarki ta dawo kenan?"
"Eh ta dawo" ya sake bata amsa. Zancen kaya ta cigaba dayi masa yana sauraronta yana kuma kallon hanya dan kar Zulaiha ta taho bai lura ba kusan minti goma kafin ya cewa Jalilan zai kirata idan sun isa gida ya ajiye wayar ganin Zulaihan tareda wani ya ruƙo mata ledar abinda ta siya. Kallonsu ya ringayi, da farko ɗauka yayi ko yaron shagon ne sai da suka matso yaga Normal kaya ne a jikinsa ba rigar ma'aikata ba kuma magana yakeyi mata dukda fuskarta bata nuna sauraronsa takeyi ba amma yanda suka jero kamar ma jikinsa na gugar nata ya harzuƙa shi bai san sanda ya buɗe motar ya fita ba dai dai lokacin da suka ƙarasa ta nuna Bilal ɗin tana cewa

"Ga Mijina nan tunda na faɗa maka baka yarda ba shi sai yayi maka bayani" ta fizge ledar ta shige mota ta barsu a tsaye. Haƙuri mutumin ya shiga bashi kafin ya juya da sauri ya bar gurin shi kuma ya koma motar cikin fushi ya ce mata

"Akan me kika tsaya kika kula shi?"

"Ni a yaushe na kula shi? Kuma idan da mun fita tare da kai ai babu wanda ya isa yayi mun magana amma kayi zamanka a mota ka turani tsakiyar maza saboda baka kishina" ta ƙarasa idonta na kawo hawaye. Tsaki yayi ya tayar da motar har suka isa gida bai ce mata komai ba.

Part ɗin sa ya wuce yana fita itama ta sakawa falon muƙulli ta fitar da Shawarmarta da Smoothie ta shiga ci bayan ta kunna kallo, wayarta tayi kara, tayi murmushi ganin mai kiran ta ɗaga. Mutumin da suka haɗu ɗazu ne, ba tayi niyyar kulashi ba dan daya mata magana kai tsaye tace masa ita matar aure ce amma bai yarda ba da zata biya kuɗin siyayyar da tayi ya ce ta barshi taƙi shine ya zuba mata cash ɗin da sai da tazo gida yanzu taga dubu ɗari biyu ce a ledar. Ta san ba zai wuce a gurin Teejay ɗaya daga cikin yaran gurin ya samu number, Ahlan da ta gani a true caller kuma ya saka ta gane shi ne dan sunan da yake kan complement card ɗin daya haɗa mata da shi kenan.

Ba tsoro ko fargabar komai ta shiga yin wayarta kamar yanda ya ce aurenta ba matsalar sa bace in dai ta yarda su ƙulla alaƙa. Har sha biyu da wani abu kafin sukayi sallama ta wuce ta kwanta ba tareda ta bi ta kan Bilal ba wanda yake can shima yana sheƙe ayarsa da Jalilah dan daga waya ta fara hillatarsa da abinda yayi rantsuwar ba zai sake ba ya tuba sai gashi bai san sanda yayi unblocking nata a Whatsapp ba da kansa kuma ya kirata Video call sukayi abinda bayan sun gama kuma yayi bacci dan sai lokacin yaji ya samu nutsuwa. Duk daɗewar da yayi da Zulaiha wuya kawai ya ci amma yanzu a ɗan lokaci ya samu nutsuwar da ya daɗe bai sameta ba.

Tunani ya ringayi ko dai ta Hajjan ya yarda ya auri Jalilah ne? Aurensa da ita riba biyu ne, ga kuɗi ga kuma jin daɗi domin ita ɗin ta san ta kan duniya amma kuma kishi ba zai taɓa bari ya zauna lafiya da ita ba dan zuciyarsa ba zata samu nutsuwa ba zai yi ta zargi da hasashen tana kula wasu a bayan idonsa wannan ya saka ko yaji zuciyarsa na son kwaɗaita masa auren Jalilah da abinda zai samu a silar hakan zai kore tunanin domin dai bariki ta haɗa su a nan kuma zasu rabu.

Washe gari kamar yanda sukayi da Kamalu yaje ya same shi sun tafi gurin Alhaji Balarabe mamallakin plazar da Jalilah ta siyi shagunan. Alhajin ya karɓi takaddun take kuma ya kira Lawyer da wanda aka ci sa'a yana ta gurin dan haka ba'a wani ɗauki lokaci ba ya je ya same su.
"Gaskiya waɗannan takardun ba namu bane" Lawyer ya faɗa bayan daya gama dubasu. Alhaji ya tashi ya ɗakko wata folder ya ringa fitar da original takardu na sauran shagunan da ba'a siyar ba yana miƙewa Bilal da Kamalu suna dubawa, ya kwashe su ya mayar sannan ya ɗakko photocopy ya ware su ya cire masa na ainihin shagonsu ya bashi yana cewa

"Kaga photocopy ɗin original ɗin da muka baka nan" ba wani dogon bincike Bilal da kansa ya gane banbanci ƙarara na takardun hannunsa da photocopy waɗanda akace sune wanda aka bashi. Duk kansa sai ya ƙulle, ya kuma tuna tabbas irin waɗancan aka bashi domin bai manta stamp ɗin su da yake a kai ba wanda sai yanzu ya lura babu shi a na hannun nasa.

Alhaji Balarabe ya ce ya tafi da photocopy ɗin sannan a shirye suke domin su taimaka masa t duk inda zasu iya idan buƙatar hakan ta taso.
"Kayi tunani ko takardun sun shiga hannun wani bayan kai kar ka ce cire kowa walau ya uwa ko Amini muddin sun je hannunsa toh abin zargi ne domin babu yanda za'ayi a tashi rana ɗaya ace takaddu sun canza daga yanda suke zuwa wani abu na daban dole wani ne ya canza su" cewar Lawyer Alhaji Balarabe.

Haka ya bar gurin cikin damuwa duk kuma yanda zaiyi ya gano abinda ya faru ya kasa, to wa ma zai zarga bayan daga

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login