Showing 222001 words to 225000 words out of 257873 words

Chapter 75 - KURA A RUMBU HAUSA NOVEL

23 Oct 2025

463

da take shafarta kuma ba iya ita ba.

Ya gyaɗa kai tareda raɓeta ya wuce yana jin ta saki tsaki haɗi da cewa
"Ƙaryar banza" kafin ta bi bayansa, kafin ma fita da mota ya kulle gidan ita har ta kusa titi, ya na ƙoƙarin tsayawa ya ɗauke ta tare Napep ta shige abinta tamkar ma bata ganshi ba. Ya sauke numfashi mai nauyi yana shafa kansa. Yayi zaton samuwar Zulaihan zai zame masa cikar burika da kuma samun nutsuwa sai dai daga ranar data fara amsa sunan matarsa shi dai kullum komai ƙara lalace masa yakeyi.

Zulaiha ta raina shi, raini irin wanda bai taɓa zaton wani mahaluki zai yi masa a duniya ba. Da fari zama ya fara yin daɗi a tsakaninsu, yana ƙoƙari gurin ture abinda yake hanashi sukuni akanta ya tarairayeta irin yanda ya daɗe yana mata tanadi itama kuma tana ƙoƙari matuƙa gurin kyautata masa sai dai abinda ya fara haɗasu kwashe-kwashen ƙawayenta.

Ya mata magana ya fi sau shurin masaki akan mutanen da take tarawa suyi masa kaca kaca da gida kuma su tsallake su tafi su barshi a haka itama da take zaune a gidan ba zata gyara ba haka zata zauna cikin ƙazantarta tayi ta danna waya ko tayi kallo idan yayi magana ta ce dare yayi an hanata shara da daddare tunda shi kuma ba zai iya bacci da datti a in da yake ba dole komai dare haka zai gyara gidan hakan kuma ba zai hana washe gari su sake dawowa su maimaita abinda sukayi jiyan ba.

Ga Almubazzaranci, buhun shinkafa daya ajiye bai ko rufa musu wata biyu ba tace ya ƙare duk kuwa da ba wai shi kaɗai bane akwai su taliya, macaroni harda couscous, kada kayan shayi suji labari dama, idan ya siyo madara ta leda ko gwangwani yau in sha Allahu kwana uku yayi yawa sai dai ya tarar da burbuɗi a ciki balle ƙwai da idan ta tashi shida take soyawa idan bai tashi ba haka zata cinye ita kaɗai su Nama, kaza kuwa tunda ya siyo na farko bayan an kawo mata Freezer da ta ce Mijin wata Antyn ta ne ya siya musu ita da Nuratu ya yiwo cefane da yawa aka zuba, shi dai bai irga sau nawa ma ya ci abincin nata ba balle ya ci Naman ba'a rufa sati biyu ba zai fita ta ce masa ya aiko da naman da za'ayi girki, ya rufeta da faɗa bata saurara ba itama ta haye masa tana cewa

"Karka kuskura ka zageni akan nama wlh, banda tsiya da ƙaranta mai akayi akai nama da har zaka ringa tada jijiyoyin wuya akansa? Dama ba saboda na ci ka siyo ba ko kuwa ado zanyi dashi a Freezer? Toh wlh karka sake, ba kuma ka isa ka mun shamaki da wani abu a gidan mijina ba zan ci abinda nake so kuma dole ka kawo dan haƙƙina ne dole ka bani abina" ta faɗa tana wani zare masa ido kamar uwarsa.

Ya ringa kallonta cike da al'ajabi ba tareda ya shirya ba kuma ƙwaƙwalwarsa ta tafi masa tariyar lokutan baya zamanin Halima. Ya tuna lokacin da yake mata tijara akan abinda ya siya da kuɗinsa ko wanda aka kawo mata daga gidansu, dai-dai da rana ɗaya bata taɓa ɗaga kai ta kalle shi ba balle ta mayar masa da raddi idan ya gama kuma ta bashi haƙuri.

Kawar da tunanin yayi ya kalleta ya ce
"Kin fi kowa sanin ba'a bishiya nake tsinko kuɗi ba dan haka tun wuri ki shiga hankalinki ki kuma koyi tattali" daga haka ya wuce shi da kansa mamakin kansa ya kamashi. A wata biyun ta masa abubuwan daya kamata ace ya rufeta a ɗaki ya mata dukan tashi kisha gishiri amma ko magana mai zafi zuciyarsa bata taɓa yarda ya furta mata ba ko yayi niyya kawai sai yaji ba zai iya ɓata mata rai ba sai dai ya shanye komai a cikinsa shi kaɗai.

Gajiya yayi da tafiya ya samu gefen titi yayi parking, sai da ya matsar da kujera baya ya kwanta haɗi da tallafe kansa ya lula tunani. A lissafe yake komai ya rasa kuma ta inda ya kuskure abubuwa suke neman su lalace masa haka.

Wayarsa ya ciro daga Aljihu yaga sake ganin Missed call ɗin Alhaji Lawan, ya ja tsaki a fili to wai mai yake so yayi masa ne?
Yana ƙoƙarin sake kiran Jalilah kiran Alhaji Lawan ɗin ya sakw shigowa, ya kuma zabga tsaki kafin ya tashi zaune dakyau ya ɗaga wayar. A gajarce suka gaisa Alhajin ya ce

"Da sassafe mutane suka buga mun gida, na fita na same su suke sanar mun da sun siyi gidan ne kuma su ba'a faɗa musu ma da akwai yan haya a ciki ba dan mutumin tafe yake da yara da zasuyi masa shara su wanke gidan wai amarya za'a saka nan da sati ɗaya dan ya ce zuwan da yayi na ƙarshe lokacin ana aikin gyaran gidan kuɗi ne bai cika ba sai yanzu aka bashi muƙullin gidan".

Bilal ji yayi kamar ba hausa mutumin yakeyi masa ba, lokaci ɗaya kuma tunaninsa ya tafi akan tabbas sai dai idan asalin wanda aka siyi gidan a gurinsu ne suka sake siyarwa da wani kuma Jalilah ce zata warware wannan matsalar tunda ita ya san waɗanda ta siyi gida a hannunsu shi takardu da muƙulli kawai ta bashi idan bai manta ba tace gidan na saurayin wata ƙawarta ne.

"Ka kwantar da hankalinka Alhaji in sha Allahu yanzu zan kira asalin wanda na siyi gurin a hannunsa duk yanda ake ciki zaka ji ni" ya bashi amsa cikin kwantar da murya. Alhaji Lawan ya ce

"Gara dai, dukda ni kam na haƙura dan idan baka manta ba sai da nayita nanata maka bana son rigima, idan ka san gurinka akwai rigimar gado ko ta gwamnati akansa ka faɗa mun dan na shiga irin haka banji daɗi ba ƙarshe sai asara na ɗauka dan filin gomnati ne mutumin yayi ginina ciki na siya amma kace babu komai, to ni dai na haƙura ka dawo mun da kuɗi na kawai ka riƙe gidanka, dama tun safe na kira lawyer na na shaida masa komai zaizo ya sameka yanzu haka ka gammu har munci ƙarfin kwashe kaya daga gidan dan haka ina sauraron kuɗi na" daga haka ya katse wayar ba tareda ya bari Bilal ɗin ya sake cewa komai ba.

Tsaki Bilal yayi bayan daya sauke wayar daga kunnensa yana cewa
"Ai da sauƙi ka tunda ka saba ɗaukar asara wannan karon ma haka zakayi haƙuri wlh".

Jalilah ya sake kira, wayar na dab da katsewa aka ɗaga ya sauke ajiyar zuciya sai dai kafin yayi magana muryar Namiji daya ji ta saka murnarsa ta koma ciki

"Tana cikin uzuri, idan saƙo mai muhimmanci ne ka faɗa sai a sanar mata" mutumin da muryarsa ta nuna ba asalin bahaushe bane ya faɗa. Tunani ya tafi akan wane uzuri takeyi? Ba zai wuce tana tareda wani namijin suna lalata ba dai ya san, yayi tsaki wani abu mai kama da kishi ya taso masa murya a cuskule ya ce

"Ka ce mata Bilal ya kira kuma uzurin gaggawa ne".

Gidan Hajja ya wuce, ya tarar da ita da Fadila da tulin kaya dangin atamfa, leshi da materials suna ta dubawa bakin nan kamar zai tsage saboda murna ko sallamarsa duk su biyun ba su ji ba saida ya shiga cikin falon kafin suka lura da shi.

"Yawwa kamar kasan dama yanzu nake so na kiraka ka zo" Hajjan ta faɗa bayan data amsa sallamarsa. Yana kallon kayan ya ce

"Waɗannan fa?"
"Lefen ƙanwarka ne" ta bashi amsa tana tura masa wani ɗaurin kuɗi da a ƙalla zasu iyayin miliyan ɗaya ko sama da haka. Cikin muryar data bayyanar da farincikin da take ciki tace

"Miliyan biyar ya bata kuɗin lefe da sadaki, kaga siyayyar da tayi akwai wasu a ɗaki da kuma sauran da ba'a kawo ba ga dai abinda yayi saura nan sai ka haɗa ka siya mata kayan ɗaki irin na Halima da aka fitar dan ka san ba ƙaramin gida zata shiga ba. Hassadar da kayi mata ka ƙi ka mata hanyar abokinka gashi ta zame mata taki Allah ya kawo mata wanda ya dokeshi a arziƙi".

Shi dai kallon Hajjan kawai yakeyi harta kai aya kafin ya ce
"Yaushe Fadila ta samu miji har aka karɓi sadaki bamu sani ba? Kuma su Baba Sani ne suka karɓa ko su Yaya Aminu?"

"Uwar su Baba Sani da Aminu ce ta karɓa, ni ce zan zake soko Sani a cikin sabgata? Ai har abada wlh. Kuma Fadilar budurwa ce da sai wani ya karɓar mata sadaki ko me? Kai ma ɗin abinda ya sa na faɗa maka yanzu saboda kai zakayi kayan ɗaki ne idan ba haka ba cikin yan gayya zaka fito sai ya rage kwana biyu ɗaurin aure kafin a sanar muku" Hajja ta bashi amsa. Ya sauke ajiyar zuciya ya ce

"Allah ya sanya alkhairi, zan kuma bayar da gudummawa abinda ya samu amma batun nayi mata kayan ɗaki bai taso ba tunda dai ba'a faɗa mun da wuri ba balle nayi tanadi dan bani da wasu kuɗi a halin yanzu".

Hannu Hajja ta shiga tafawa tana salallami yanda kasan wacce taga bala'i tsirara kafin ta lailayo ashar ta watsa masa tana cewa

"Lallai Bilal, ni zaka kalli tsabar ido na kace mun baka da kuɗin da zaka yiwa yar uwarka kayan ɗaki amma ai kana da kuɗin yiwa yar iskar fitsararriyar matsiyaciyar matarka ko?"

Runtse idonsa yayi dan sosai yaji zafin kalaman data jefi Zulaiha da su, yana ji ta ringa sababi tamkar zata aro baki tana zagin Zulaiha da iyayenta dashi kansa.

"Karka ɗauka shirun da nayi maka kafi ƙarfi na ne ko kuma bani da yanda zanyi da kai, wlh Bilal; kaƙi yin abinda nace a lokacin zan nuna maka asalin kalata daka manta. Tunda ka auro yar iskar yarinyar nan ka ɗaga waya ka kirani ma ya zama sai sa'a balle ka tako ƙafarka ka zo cikin gidan nan sai dai idan taka ce ta kawoka, to ba duniya na haifawa kai ba, babu kuma wasu yan iska da basu tayani shan wahala da rainonka ba da zasu fini jin daɗinka a yanzu dan haka kayi duk yanda ka so nima ba zan fasa yin abinda na so ba" tana gama faɗar haka ta shige ɗaki ta barsu.

Yana tafe yana lissafa sabon jidalin daya same shi, yanzu tsakani da Allah a ina Hajja take so ya nemo kuɗin da zai yiwa Fadila kayan ɗaki a sati uku kuma ma wai irin na Halima ita ya san nawa ake siyar da irin kayan ne?

Gurin Nasir ya wuce suka sake tattauna batun gidan yana sake nanata masa
"Wlh Alhaji Lawan bashida daɗi, rufin asirinka ɗaya kuɗin sa ya fito tunda ya ce ya haƙura da gidan idan ba haka ba ina jiye maka tijarar mutumin nan wlh"

"Ai sai dai yayi koma menene ciniki ne kuma ya biya an bashi gida da takardu ya rage tsakaninsa da su can suje wanda yafi ƙarfi ya mallaki guri" Bilal ya faɗa, Nasir dai bai sake ce masa komai ba ya kamo wata hirar wacce batayi tsayi ba Bilal ɗin ya masa sallama ya wuce dan gaba ɗaya babu abinda yake jin daɗi yanzu komai ya masa zafi mafita kawai yake nema.

Yawo ya ringayi a gari har yamma kafin ya koma gida har sannan kuma Zulaiha bata dawo ba dukda ba sabon abu bane dama idan ta fita kawai sai an ganta. Kitchen ya shiga ya duba ko zai samu abinda zai ci dukda ya san da wahala, ya gama buɗe-buɗen kwanukan daya gani amma babu komai a ciki ya wuce ya buɗe freezer yana tsaki, bai taɓa shiga kitchen ɗin bai samu abinda zai ci ba a sanda Halima tana nan. Bayan leftovers da take ajiyewa ga kayan ƙwalama kala-kala har sanda aka janye mata tallafi daga gida in dai ta samu kuɗi ko yaya ne sai tayi wani abun na taɓawa ta ajiye kuma duk shi yake cinyewa har idan ta rigashi ta cinye abinda yayi saura ma ya samu bakin yin masifa.

Da mamaki ya kalli cikin freezer dake danƙare da kayayyaki, kaji, jan nama, kifi kala-kala gasu nan. Ya rufe yaja baya ya tsaya yana tunanin daga ina aka samo su? Domin dai tun cefanen farko daya mata irin haka ta cinye bai sake siyowa da yawa irin haka ba, da Halima ce sai ya ce daga gidansu aka kawo mata amma Zulaiha fa, ya sani kaf danginta na uwa da uba babu mai iya yi mata haka.

Fita yayi daga kitchen ɗin har zai fice daga falon gaba ɗaya kuma ya fasa ya wuce ɗakinta. Yanda kasan ɗakin Namiji ko ina an zubar da kaya wankakku da masu datti, ya ringa yamutsa hanci yana tattare mata kayan sai yaji ɗakin ma har wani tashi yakeyi. Tsaf ya gyara kayan daya kwashe ya ɗaure mata su a zani dan ko laundry basket bata da shi, ya cire bedsheet ɗin da ya fi wata ɗaya akan gadon sai da ya sha lalube kafin ya samo wani ya shimfiɗa.

Wardrobe ɗin tata kanta kamar ta yara komai da mazauninsa daban, ya ringa hasaso wardrobe ɗin da take a gurin da ƙatuwar gaske data sha ado da mudubi kowanne compartment da abinda take sakawa a ciki, ɓangarorin atamfa daban hala lace da sauran kayanta ga ƙamshi Halima ko bata fesa turare ba a hakanta ma ƙamshi takeyi.

Gefen gadon ya samu ya zauna yana shafa goshinsa da hannu ɗaya, sanda suke tare ya raina tsaftarta, a hakan gani yakeyi bata iya ba ko shara tayi in dai yana nan sai ya sake maimaitawa ko idan tanayi ya ringa kushewa kenan ya ce nan bai sharu ba bata goge can ba can batayi kaza ba sai kace ba mace ba aikin gida ma ace shi Namiji ya fita iyawa duk idan yayi mata hakan sai dai tayi murmushi kawai bata taɓa nuna ɓacin rai ko tayi fushi ba sai dai ma ta nuna jin daɗi dan tana yawan faɗa tsaftarsa tana cikin abubuwan da take so a tattare dashi.

Tashi yayi idonsa ya sauka kan drawer dake saman mudubi wacce sai an lura da kyau sannan za'a gane ana iya buɗeta, ya buɗe ido cike da mamaki yana kallon abubuwan da suke ciki, rafar yan dubu-dubu daya gani ya ɗauka guda ɗaya ya shiga juyawa a hannunsa kafin ya mayar ya ajiye ya ɗauki wata yar kwalba data ja hankalinsa.

Instruction ɗin jiki ya karanta take kuma ya samu amsar abinda ya daɗe yana ci masa tuwo a ƙwarya cikin tarayyarsu da Zulaihan. A aljihu ya jefa kwalaben guda biyu ya rufe mata drawer ya koma kitchen ya dafa indomie sannan ya koma ɗakinsa.

Wai duk a yaushe Zulaiha ta samu irin wayewar nan bai sani ba? Shi dai a shekarun da suka shafe ko da wasa bai taɓa ganin wata alama da zata ɗarsa zargi ko wani abu zuciyarsa ba. Yana cin abincin maganganun Kawunsu suka shiga dawo masa. Toh ko dama abinda yake magana akai kenan? Ko kuwa akwai wani abun bayan wannan ma?"

Ƙarar wayarsa ta katse masa tunani da sauri ya aje cokalin ya ɗauki ruwa ya sha ganin mai kiran, Jalilah ce ya ɗaga.

Daga can ɓangaren murya washe Jalilar ta ce
"Sweet baka gida ne?"
"Ina gida mana mai ya faru?" Ya bata amsa, ji yayi kamar an ƙwanƙwasa Get kafin a shagwaɓe yaji ta ce

"Amma shine nake ta buga ƙofa kana ji na ba zaka zo ka buɗe ba?"

Ai sai yaji kamar an tsinka masa mari a bazata, yayi firgigit ya miƙe tsaye kamar wanda ya farka daga suma ya ce
"Na'am, me kika ce?"

"Nace ina ƙofar gida kazo ka buɗe, dan Allah I'm stressed enough for today Bilal daga Airport kai tsaye na wuto na gaji kazo ka buɗe mun tun ban faɗi a inda nake ba" Jalilar ta bashi amsa cikin muryar dake nuna gajiyar tata dagaske. Laluben key ɗin motarsa ya shigayi bai ko tsaya saka riga ba dan single ce da three quarter wando a jikinsa ya zura takalmi ya fita bayan ya jefa wayar aljihu ba tareda ya ko katse kiran ba.

Buɗe ƙofar yayi ya leƙa sukayi ido huɗu da Jalilah dake tsaye da ƙaramar akwati a gabanta tana danna waya fuska a haɗe, da sauri ya mayar da ƙofar zuciyarsa ta shiga luguden daka. Bai tsammaci dagaske take ba ya ɗauka dai ta shigo Kanon shiyasa zai tafi ya tarota a inda take ya nemi in da zaiyi mata masauki ashe ita harta ƙaraso ma.

Cikin ɗaga murya Jalilah tace
"Menene haka Bilal? Wane irin wulaƙanci ne wannan?"

Bai amsa mata ba ya wuce ya kunna mota, sai kuma ya fito daya tuna dole dai sai ya buɗe Get ɗin tunda dai motar ba zata fita ta saman katanga ba. Yanda ka san maraya haka ya narke fuska ya nufeta yana cewa

"Bari na ɗakko mota sai muje na kaiki masauki dan Allah". Akwatinta taja ta wuce shi ta shige gidan tana cewa

"A nan naga damar sauka" ya bita da sauri ya riƙe akwatin ta sakar masa ta shige ciki kamar gidanta tana kallon compound ɗin daya sha sabon fenti. Murmushin da Bilal bai san dalilinsa ba ta saki tana cewa

"Gyara aka yiwa gidan ashe? Gashi kuwa ya ƙara kyau" ta wuce falo shi dai kamar wanda aka dasa ya tsaya a guri ɗaya ya kasa bin bayanta.

Turus tayi tana kallon cikin falon kafin ta waiwaya ta kalli Bilal daya sauke kai ƙasa tamkar an ƙure munafuki, har ta buɗe baki zatayi magana sai kuma ta fasa ta ƙarasa shigewa tana kallon gurin. Kusan minti biyu kafin Bilal ya samu ƙarfin guiwar bin bayanta ya shiga falon ta kalleshi fuska babu yabo ba fallasa ta ce

"Ashe dai kayan gurin ne suka ƙara masa kwarjini yanzu kuwa ana shigowa an san gidan gwauro ne" ta ƙarasa da wani murmushi kafin ta miƙe ta nufi ɗaki tana cewa

"Allah sarki Halima sai kuma na ɗan ji tausayinta kaɗan yar yarinya ka mayar da ita bazawara".
Shan gabanta yayi tana

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login