Showing 213001 words to 216000 words out of 235422 words

Chapter 72 - GIDAN SARAUTA COMPLETE

Zeeneert   

06 Sep 2025

3513

breathing",yayima Dad tambayar ah rude. Kan kacemai maaikatan masarautar dake harabar gurin duk sunyo kansu suna mamakin abunda yafaru din ba ajimaba kuma sega karar ambulance da alama tanayowa gurin da suke ne,haka aka daukeshi akasaka shi cikin motar kafin suka karasa sashin shi adakin shi suka kwantar dashi yayinda likita yashiga duba shi cikin gaggawa wanda already yazo da kayan aikinshi ma,allura yayi mai tareda sakamai drip wanda ah tunaninshi shine zai taimaka mai ya farfado zuwa anjima tunda makasudun ciwon bewuce ulcer dakuma Bp bane ke damunshi dukdama Bp din he's not sure seya farfado kafin aduba. Duban Dad yayi kafin yace insha Allah zuwa anjima ze tashi,daya farka just let me know Dad dake ta zufa cikeda damuwa yace
"toshikenan Doctor,thank you very much"......

Murmushi likitan yayi yana "don't worry, it's my job",kafin yajuya yafita Sulaiman ne yace ko inkirasu Abba ne Dad?........

Cikin sauri Dad yace"no you don't have to call them,kana iya tada musu hankali by calling them insha Allah zaisamu sauki soon".....
To Allah yasa cewar Sulaiman din,atake kuma wayar Sulaiman din tashiga ruri dubawa yayi inda yaga Dr Na'im ne,babu bata lokaci yayi recieving call din bayan sun gaisa yake fada masa rashin lafiyar Almustapha din cikeda damuwa Na'im din yace...
"I knew it,indai yayi wasa saka damuwa da rashin cin abincin nan na'iya kwantar dashi"......
"Anyways I'll be on my way,kuna gida Ina?"....
"Eh muna gida", Sulaiman yabashi amsa kafin sukayi sallama......

Bangaren su Mai Martaba kuwa tunda suka fita sukabar masarautar straight gidansu Asma'u sukabi suka dauketa don dama already tashirya tun safe harma Daddy yace ko akaita can masarautar se su wuce amma Mai Martaba cewa yayi abarta insunfito zasubi sudauketa. tunda tafito take ta rarraba idanu kozata ganshi amma babu halamunshi haka tawuce motar dasu Hamida ke ciki ta bude tashige wani irin ihun murna suka saki tareda rungume ta cikin jikinsu daman tunda aka doso gidansu Asma'un suketa mamakin meza ajeyi Afiya ne tace"Daman kina gida all this while?"........

Gyadamata Kai tayi ahankali, Hamida sake rungumeta tayi tana "we missed you so very much",yayinda Amira ta turo baki tana"itada ta ruguza mana all our wedding plans,nidai banyi kewarkiba",dariya Asma'u tayi tareda jan karan hancin Amiran tana"kedai fadi gaskiyar Amira".....

"To wai miyasa ma kika dawo gida Sis,su Ummi basu fada miki laifin wancan jakar zalihar bane ba?",wannan karan Afiya ne tayi magana,tsaki Amira tayi tana"ae ba munta fada mataba anma seta dinga ganin kaman muna taya Sumayya kishine bayan ninasan duk wanda yahada harka da Magajiya karshenta he'll turn out to be like her"........
Murmushi Asma'u takumayi tanajin yanda Amira da Afiya keta masifa kan abunda yafaru kafin tace"yanzukam baya wuceba, she's now exposed and everyone knows the truth daman duk wani munafiki karshen shi bazaiyi kyau ba kuma duk abubuwan datayi kanta tayimawa bamuba"........
Gyadakai Hamida tayi tareda cewa hakane Asma'u, Allah yashiryemu bakidaya yasa mufi karfin zukatan mu se lokacin Afiya tayi realising baran baramar datayi na maganar Magajiya because ita kwata kwata ma mantawa takeyi Hamida Yar Magajiya ce,jiki ah sanyaye tace Aunty Hamida I'm very sorry......
Dariyan yake Hamida tayi kafin tace"for what Kuma?".......

"Nidai I'm sorry please",Afiyan tasake emphasising,gyada matakai Hamidan tayi tareda cewa....

"you did nothing so,there is nothing to be sorry for". Haka suka cigaba da hirarrakinsu wanda duk yawancin labarin akan Zaliha ne su Amiran kebama Asma'u harsuka iso kaduna straight aiport suka wuce inda already plane dinsu is ready jiransu kawai akeyi su iso kafin yatashi. Around 1:00pm jirginsu yayi landing ah aiport na Maiduguri and already har motocin dazata daukesu tazo daga hotel din da yakama musu don acewarshi bazaiso yasauka gidan sarkin Bornon ba bayan abubuwan dasuka faru din haka suka wuce hotel din wanda already ankebe musu floor daya daga shi har mutanen shi,sunyi wanka sunci abinci kafin suka huta baki dayansu inda Mai Martaban yayi niyar zuwa gidansu Zalihan washegari daganan kuma sesuyi tunanin wucewa Chad kuma. Acan Zaria kuwa wuraren azahar Almustapha yafarka ganin su Na'im yayi azaune suna dan hirarrakinsu da alama ma basusan yafarka ba dan motsin dayayi da hannunshi ne yajanyo attention din Sulaiman cikin sauri yakaraso inda yake cikeda tausayinshi yace...
"Yaya Almustapha how are you feeling now?".....

Bece mishi komaiba sema maida dubanshi kan drip din dake hannunshi dayayi,ahankali Na'im yataso yakarasa gefen gadon inda aka ajiye abincin Almustaphan kafin yadauki mug yashiga hadamai tea,seda yagama hadawa sannan yaxo yazauna yana taba temperature din jikin shi tareda cewa"katashi kasha tea kafin kaci abinci".......
"Am not hungry",shine abunda Almustapha din yafurta Hajiya Muniba dayanzu shigowanta dakin kuma sarai taji meyace yasa cikin sauri ta tari bakinshi tahanyar cewa"mekaci tunsafe dazakace you're not hungry Yarima?".........

Lumshe idanunshi yayi ahankali donshi maganganunsu ma ciwon Kai yakesaka mishi wallahi,daukan mug din tea din tayi wanda Na'im ne ya ajiyeshi agurin kafin tace katashi kaci ko inyi maka dure wallahi,why will you be stabbing yourself atunaninka akoina Asma'un take zataji dadin ganinka haka kokuma hakan shizai sa tadawo, we're all worried about her dakake ganin mun na amma bamu tada hankalinmu ba inbanda addu'a da mukeyimata na Allah ya bayyana ta sabida munsan wannan ne kadai soyayyar dazamu iya nuna mata".....
"So,maza tashi kaci abinci inkuma duren kakeso inyi maka to abume sauki ne agurina tunda ganida garada ah kusa rikemin kai bazai bani wahalaba",dukyanda Sulaiman yaso rike dariyarsa kasawa yayi seda yadan dara Imam kuwa babu yanda ya'iya dole yatashi yasha tea din seda yashanye tas sannan Hajiya Muniba tazuba mai abinci ah plate nanma ta tasashi gaba seyaci, jijjiga matakai yayi alamar bazai iya ci ba......
"Oh duren zamuyi kenan komi?".......
Lumshe idanunshi yayi kafin yabude bakin tasakai abincin jiyayi kaman tasamai flagen ah baki kwata kwata babu taste haka yakejin abincin abakinshi amma sabida bayason jayayya yasa yadinga karba,ah loma na biyar dinne yashiga kwarara amai, seda ya amayar harda tea din dayasha duka. Subhanallah shine abunda Hajiya Muniban tace kafin tashiga yimashi sannu,haka akasamo towel Sulaiman yagogemai jikinshi daya baci da aman suna cikin haka Dad yashigo da likitan sannu sukayi mashi kafin Hajiya Muniba tayi bayanin abunda yafaru recently,gyadakai likitan yayi kafin yace ulcer ce tayi mugun kamashi ga kuma damuwa dayasama ransa dole seyataimaka yanabin dokokinmu kafin yasamu lafiya dukdama lafiya na Allah ne......

Gyada Kai dukansu sukayi,yayinda likitan yazauna gefen Almustapha din yana masa Questions gameda yanda yake ji shikuma yana ansa masa daga karshedai likitan yayi dan gwaje gwajenshi sannan yace my suspicion was right,Bp dinshi yahau gakuma ulcer dake damunshi. Ajiyar zuciya Dad yayi sannan yace daman yanada BP ne?........

"Yanadashi din tunda gashi yatashi yanzu",cewar likitan kafin yamaida dubanshi kan Almustaphan yace tunda inkaci abinci amayar wa kakeyi bari insake samaka wani drip din it might help and that does not mean kadaina cin abinci ko kana amayar wan ka dinga ci koda kadanne please and batun damuwa please karage saka makanka damuwa if you've any problem tell them they might help you out, you're a Doctor so,I expect you to know all the consequences". Gyada masa kai Almustapha yayi inda likitan yasake saka mishi drip din sannan yayi masa prescribing drugs, Na'im ne yakarba tareda cewa bari yaje yasiyo, he's a Doctor yasan damuwar Almustapha din amna bayason yayi musu katsalanda besides doctor dasukedashi dinma is doing his job perfectly but abudayane yasani zaitaimaka ma Almustapha wurin samun lafiya that's yasamu "peace of mind" and that will only happen in akasamo Asma'u inbahaka ba kwana nawa ana rokonshi yakwantar da hankalinshi yaki and he doesn't blame him ita zuciya haka take indai batasamu abunda takesoba bazata taba zama stable ba...

&&&
Da dare tanajinsu Afiya daga me hello sweetheart se me I missed you love, Hamida me tayata hirarma tafice gurin Ummi wannan dalilin yasa all her loneliness yadawo sabo,toma miyasa bataga Almustapha ba bayan ance dashi za azo,juyi tayi kan gadon tareda daukar pillow tarungume ah kirji gashi wayarta ma tabarshi acan gida bare tarage kewarshi koda ta hanyar kallon hotunanshi ne,wayarma tunranar data jefa ta ah drawer batasake waiwayonta ba,hango babban wayar Amira tayi kan bedside drawer ashema da karamar take waya cikin sauri tadauka tareda unlocking dinta direct pictures tashiga inda tayi arba da hotunanshi bila adadin,kallo tadingayi tanajin hankalinta nakara kwanciya wani tayi murmushi wani kuma tayi dariyan yanda yabata rai akayi hoton,jitayi anwabce wayar daga hannunta tabaya cikin sauri tatashi tana"waye wannan?"....

Dariya Amira tayi tana"inmutum yana kewan mijinshi yakirashi mana bawai yatsaya yana kallon hotunan shiba,you can see him for real by making video call" ......

Turo baki Asma'u tayi tana"cemiki nayi kewarshi nikeyi".....
Nifa shawara nabaki Sister in-law, Amiran tabata ansa playfully kafin kuma kamar wanda aka tuna matada abu tace"tukunnan ma wait!"......
Tsayawa Asma'u tayi tana kallonta kafin Amiran tace....

"if I could remember Yaya was sick and worried about your disappearance to ya akayi ba afadamishi kindawo ba?"........
"Banganeba,besan inanan ba kikeson kice?", Asma'u tayima Amira tambayar cikeda curiousity,yes besaniba don dayasani he'll be the first to come and see you bakisan halin dayashiga bane da bakyanan, cikeda zumudi Asma'u tace"Are you serious?"....
"How did he react?"
Gwaliyo Amira tamata sannan tace"naqi wayon bazan fadaba,kikirashi kitambayeshi"........

Hararanta Asma'u tayi kaman zatayi kuka tace...
"banzo da wayataba Allah".......
Dariya Amira tayi tareda kwaikwayon muryar Asma'un tana"sekince you missed my brother and you love him kafin inkira mikishi".......
Batarai Asma'u tayi sannan tace"kada kikiran mana shima daya damu dani zainemeni ae",daganan takoma tayi kwanciyarta alaman tayi fushi dariya Amira tayi tana I'm sorry and Yaya Imam is also sorry for not calling but I assure you bemasan ansamekiba dayasani wallahi dashizaifara zuwa gareki let me even call Yaya Sulaiman zansa ah handsfree zakiji duk conversation dinmu", takarashe maganar tareda fara dialing number Sulaiman din. Ummi dake bakin kofa tanajinsu tace seki kirashin ae mugani uwar iyayi,cikin sauri Asma'u da Amiran suka dubi inda Ummin take yayinda takaraso tsakiyar dakin tana disconnect the call joor.......
Cikin sauri Amiran tayi disconnecting call din daman ko ringing baifara bama kafin tace"Ummi amma Yaya Almustapha besan ansamu Asma'u bako,tell her nasan ke kilan tayarda da maganarki" ......

Asma'u batasan sanda taja bargo ta lullube kanta ba tsabar kunya haka tanaji kaman ta rufe Amira da duka,wannan kayan kunyar data jamata har ina fisabillahi,dariya Ummi tayi ganin abunda Asma'un tayi kafin tace"kyale sokon mijinkin nan waishi yadauka yamana wayaune dayaki biyomu bayan besan kina tareda muba,seyayita neman naki mugani inzai sameki ah Zarian kafin Sulaiman yadawo daga Indonesia din"......
Itadai Asma'u batace komaiba dukda maganar Ummin tadaure matakai, Amiran ne tace banganeba Ummi.....

Zama Ummi tayi tareda cewa"we wanted to surprise him seya watsa mana kasa ah ido kan bazai biyomu ba se Sulaiman yadawo daga Indonesia,Kuma it was just an excuse fa bayason biyomune kawae batareda Asma'un ba ah tunanina zecigaba da nemanta ne inyasameta sesu taho tare"......
Dariya Amira tayi sannan tace"Kuna jama Yaya raidayawa fa Ummi don Allah kubarshi hakanan"........

Dariya Ummin ma tayi kafin tace"let him be I want him to value my Daughter much more than yanda ya wahala,next week zaisamo mu ah chad insha Allah don nasan dolenshi yataho indai Sulaiman din yakoma tunda yariga yama Babanku alkawari so karkowa yafada mishi please, it's going to be a surprise for him"........

Gyadakai Amira tayi kafin tace"to Ummi",sannan tadubi inda Asma'un take tareda cewa kinji mijinki bemanta dake ba he's there busy looking for you harma haka yasashi kin zuwa kallon long lost maternal family dinshi, you're indeed very lucky sis Asma'u don wallahi ko ah mafarki bantaba tunanin Yaya Almustapha zai iya yima wani wannan abunba"......


Murmus uhi Asma'u tasaki acikin bargonta,it feels so great to be loved by the person you love,jitakeyi kamar kada Amiran tadaina magana yayinda wata zuciyar kuma tashiga tunanin ko awani hali yake yanzun,koma miyene she hope he's doing alright. Dahaka har bacci yayi awun gaba da'ita batareda tasani ba.......

Washegari karfe goma su Mai Martaba sukayi gidan su Zaliha balaifi sunsamu tarba mekyau wanda Mai Martaba yaji wani iri sabida yasan xuwan dayayi bawai good news yakawo ma mahaifin nataba,mutum me kirki dakuma nagarta irin haka does not deserve the news he brought to amma yazaiyi?.....

Kuskure ne Zaliha tariga da ta tafkashi
seda suka nutsu dukansu kafin Mai Martaba yasaka akashigo da Zaliha din tunda tashigo mahaifinta kebinta da kallon mamaki kafin dakyar yamaida hankalinshi kan Mai Martaba yayinda Mai Martaba yafara magana ahankali"I'm sorry da maganar danazo maka dukdama da nayi niyan turo mutanena suzo sumaka bayani sedekuma nagartarka dakuma zumuncin dake tsakanin mu yasa nayi tunanin zuwa dakaina,maganar Zaliha ce takawoni yarka damuka hada zumunci na aure,nan Mai Martaba yashiga yimasa bayanin duk abubuwan dasuka faru harkawowan yau kafin yakarada, I'm really sorry naso ace zan iya yanke wani decision dabaikai wannan ba amma banida yanda zanyi,she hurt us way too much.........

Tunda Mai Martaba yake magana sarkin Borno ke sauraronshi seda yagama tas sannan yayi ajiyar zuciya tareda cewa"naji duk bayananka and banyi blaming dinka ba in anyway or the other infact if I was in your place zanyi abunda yafi hakama sannan bazan manta gode makaba dakayi tattaki kazo hargida kakawomin 'yata,this really shows how kind-hearted and generous you're, I'm very ashame of myself as her Father dabazan ma iya duban idanunka ba donnidai nasan I tried my best wurin tarbiyantar da ita bansan ya akayi tayi wadannan abubuwan ba so,i'm very sorry",sarkin Borno yakarashe maganar murya ah raunane haka sukayi sallama da sarki Abdulrahmanu kafin suka tafi,duban Zaliha da take zaune ah inda take tundazu yayi sannan yace,"you choose to be like your Mother right ku dai abun duniya yarufe muku idanu baku ji baku gani,tokizo kiyita zama anan din muga inzaki samu kwanciyar hankalin daya dacedin kinji,kicigaba dazama muga kozaki samu sarkin dazaki auradin don ko kin samu nidai bazan sake saka hannuna acikin maganar auren ki ba bare har kisake jamin kayan kunyan dakikajamin yau ah idon mutanen dasuke kallon darajata",yanakai aya yatashi yatafi yabarta agurin,wani irin kuka mai sauti tafasheda don bata tabajin tayi nadamar abunda tayiba seyau,itakam tasan nata yakare and she's now back to square one tukunnanma dawani idanu zata dubi mahaifiyar ta bayan tacemata dukyanda zatayi tasan yanda zatayi tayi achieving goals dinta na zama Queen kada tayarda tadawo mata gida as a divorcee............
Kasama tashi tayi ah wurin se sautin kukanta da ke tashi,candai dataga abun bana karebane seta tashi tafice zuwa bangaren ta donbatamayi tunanin dosan sashin mahaifiyar tataba,she's not ready to face her now. Bangaren su Mai Martaba kuwa tunda sukabar masarautar Borno suka raba hanya dasauran don kuwa su Mallam Hudu dawanda zasu juya Zaria airport akawuce dasu sabida karfe daya jirginsu zai tashi zuwa Kaduna inda su Mai Martaba kuwa tafiyarsu Chad se gobe dasafe in Allah ya yarda. yanma lilis su Mallam Hudu suka Isa masarautar Zaria anan ne yatararda labarin rashin lafiyar Almustapha wanda jikin gaba yakeyi ba bayaba shiyasama ko gida baiwuce ba yawuce sashin nashi hankali tashe,wannan karan su Sumayya,Mom da Hajiya Muniba yasamu ah dakin don su Sulaiman tunda suka fita sallar la'asar basu dawoba. Tambayarsu yashigayi yamai jiki inda suka amsa da dasauki,Hajiya Muniba nacewa dasauki kam as compared to dazu dayake ta suma yana farfadowa. "Subhanallah abun haryakai haka?",Cewar Mallam Hudu din kafin yakarada Allah yakara Lafiya inadai likita yazo yaduba shi?,wannan karan Mom ne ta ansa da eh karasawa yayi jikin gadon tareda dan taba temperature din jikin Almustapha din jikinshi zafi rau kaman garwashi cikeda tausayinshi yace"inasu Sulaiman din?"......

Sunje masallaci basu dawoba tukunnan,gyada kai yayi still baidaga hannunshi daga jikin Almustapha dinba,sunjima ahaka kafin daga karshe yayi musu sallama yafita,to what could be the cause of his ilness newai tunda jiyannan sunbarshi Lafiya lau if he could remember and moreover yana ganinshi ah Fada all the time. Yanacikin tunanin nan shikadai ayayinda yake tafiya a cikin harabar masarautar jiyayi ankira sunanshi wannan dalilin yasa yadago cikin sauri Dad da Sulaiman ne ke yowa inda yake seda suka karaso kafin suka gaisa Dad din natambayarshi yasuka baro mutanen Maiduguri...
"nifa I thought se gobema zaku dawo nandin".......
Cikeda girmamawa Mallam Hudu yace...
"aa daman yaune zamu dawo sukuma zasu wuce Chad gobe insha Allahu se gashi daga isowan mu kuma natarar da labarin rashin lafiyar Yarima shiyasa ma banwuce gida ba nazo inga yajikin nashi and it seems like it's something serious".eh wallahi Mallam Hudu I don't even know yazanyi insamo Asma'u because from all indications rashinta ne yajanyo duk wannan abubuwan and likita yace dole yakwantar da hankalinshi inbahaka ba abun gaba zenayi ba baya ba gashi banason su Abdulrahman suji because hankalinsu gabadaya zaidawo gida and I don't want them to forget about the trip dasuka jima suna tsarashi,fatnmudai Allah yabashi lafiya cikin gaggawa maganar Asma'u kuma nasaka asake cikiyarta ah radio stations da gidan Tv sannan munsaka duk wanda yasameta yakawo mana information din inshallahu zamu bashi kyautar milliyan daya",cewar Dad din kafin ya numfasa yakarada cewa"I hope this will help wurin samota",tunda yafara maganar Mallam Hudu yasaki baki yana kallonshi da mamaki donshidai kanshi ya daure sannan yarasa wace Asma'u ce ake magana akai tunda shidai Asma'un dayasani din tuni tana taredasu tunda har borno sun tafi tare,cikeda curiosity Mallam Hudu yace"wace Asma'u kuma ranka yadade?".......
Cikeda rashin damuwa da tambayar Dad yace"matar Almustapha din mana bata bataba tun anagobe biki sarauta"......

Sakan baki Mallam Hudu yayi sannan yace"Asma'u ai tuntuni tana tareda mu infact kusan satin ta daya ah gida kafin jiya mukaje muka dauketa mukayi Maiduguri da'ita",cikin sauri Dad yace"haba dan Allah,wai dagaske kakeyi ko wasa Hudu?"........
"Wallahi tana Maiduguri tareda su Madam da Mai Martaba,shimai Martaban baifada maka baneba?"......

"Bai fadamin ba wallahi,I know nothing about it, infact I was very upset daya tsallake zaiyi tafiya batareda annemi Yar mutane ba kawai Allah bai motsi bakina da inyi masa maganar baneba sannan nasake yi mashi uzuri da zancen zeje ganin mahaifin wancan yarinyar ne shiyasa,yanzu dai you mean Asma'u is in Maiduguri?"....
"How did all this things happen Hudu?",dan numfasawa Mallam Hudu yayi kafin yashiga bama Dad labarin tunsanda Ummi tanemi taimako gurinshi harzuwa yau cikeda mamaki Dad yace ikon Allah,so much yafaru amma bansani ba to why on Earth zasu tafi da'ita without her husband's knowledge fisabilillahi. Haka Dad yadinga mita ta inda yashiga batanan yake fitaba kafin yaciro wayarshi yashiga kiran layin Mai Martaba baijima yana ringing ba yadauka ko amsa gaisuwar da Mai Martaban kema Dad din Dad baiyiba sema balbaleshi

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login