Showing 291001 words to 294000 words out of 364327 words
zauna kayi typing mai tsaho,kayi editing,ka tura cikin duka groups din da kake ciki,akwai masu comment ka zauna ka amsa musu,kunga baki daya wannan lamarin bazai yiwu ka iya aiwatar sa shi lokaci daya ba,sau tari wasu basa fahintar haka har wani ma kan gaya maka baqar magana saidai kawai ka shanye kayi masa kawaici*
*masu numberta kuma ta kira da sukemin plashing don son annabi su daina min plashing,wlh bana qaunarsa,sannan kiran dare,'yan uwa dare fa mahutar bawa,wasu kuma kira da asuba,su fadar maka da gaba ka dauka wani mummunan abu ne ya faru,wanda yake kira kuma bana dagawa shima yayi uziri,wayata a silent take ban fiya barinta a ringing ba,wasu lokuta kuma ina rejecting to sometimes ina typing ne idan layin yana cikin wayar da nake typing da ita.*
*ina fata fans kun fahimceni,duk wanda yaga yayi min magana baiga reply ba yayi haquri,wani saqon na danne wani idan sukayi yawa,sau tari ma idan ina online ka turo shi yana sama sama ina qoqarim amsawa,mu dinga yiwa juna uzuri,nasan duka qauna ce kuma na gode,Allah yasa mu dace ya bamu ikon ci gaba da haquri da juna*
______________________________________
Kusan a makare ta tashi,idanunta cike taf da bacci tayi sallah,saman abun sallar ta sake bingirewa bacci na fusgarta,sama sama ta jiyo muryanshi,tsaye yake a kanta cikin farar jallabiya yana kallonta,bata tantance shi sosai ba ta gaidashi tana daga kwancen idanunta na lumshewa,cikin mamaki ya amsa yana kallonta,sai yaga ta juya taci gaba da barcinta,ya jima tsaye yana kallonta qudundune cikin hijabi,yana mamamin wanne irin bacci take haka?,tsawon wasu daqiqu yana tsaye kafin ya juya ya fice.
Qarfe tara na safiya ta sake farkawa,barcin tamkar bai isheta ba,ga mutuwar gabbai,sai ta shige bandaki tayi wanka saboda taji qwarin jikinta,duka dai sammakal,amma dai kasalar ta ragu,gaban madubi ta shirya cikin gown mai A shape ta wani material mai kyau,ta yane kanta da qaramin mayafi wanda ya dace da material din ta wuce kitchen,falon fes yake da alama masu aiki sunzo sun gyara duk da dama ba datti yake yi ba,rasa abinda zata dafa tayi,ta jima tsaye tana tunani,sai kawai ta dauko dankalin turawa ta fere,ta dora a wuta ta dafashi,ta sauke ta murmusheshi,kifin gwangwani ta bude ta murmusheshi saman dankalin,ta zuba mai a kasko tu juye dankalin da kufin,a hankali take juyawa tsawin mintuna sannan ta kada qwai ta yanka albasa a kai da maggi ta juye kan dankalin da qwan taci gaba da juyawa har sai da qwan shima ya soyu sannan ta juye a plate,ta tsiyayi ruwan shayin da yaji kayan qamshi ta fito falo.
Kacibus sukayi da anty ni'ima matar yaya adam,cikin fara'a ta sauya akalar tafiyar tata
"A'ah,anty ni'ima,shigo mana" itama fuskarta dauke da fara'ar ta qaraso,duka sukayi masauki saman kujerun falon,sumayyan ta janyo center table ta dora plate da cup dim hannunta suka soma gaisawa da ni'iman sannan tayi mata tayi,abun ya burgeta duk da bata san meye ba ko ya akeyi,ba musu ta sanya hannu suka soma ci,sumayyan ta tambayeta ko a zuba mata ruwan zafin tace alhamdulillah,wannan ma ya isa,suna ci suna hira tamkar sun shekara tare.
Tas suka tashi da shi,ni'ima ta kalli sumayya
"Kai amiran umman khalipha,wannan abun yayi dadi,amma fa akwaisa kwadayi,ya ake yinshi?" Dariya ta saki
"Kai anty ni'imah,simple abu ne fa" a tsanake ta kwatanta mata yadda tayi din sannan ta dauke farantan tayi kitchen da su ta dawo suka ci gaba da hirarsu.
Tare suka sauko tana biye da shi a baya,ji take tamkar ta dawo da kwanakin baya,bata so ta tuna cewa yau zata sallamawa waccar 'yar qauyen mijinta da tafi so fiye da komai a duniya,sam fuskarta babu walwala haka suka ci gaba da takowa,muryar ni'ima ya jiyo,ya waiwayo ya dubesu,cikin girmama juna suka gaisa,sannan sumayya ta gaidashi tana dan dauke kai,kishinsa itama take ji har cikin zuciyarta,saidai bata son ta nuna,dining din da masu aiki suka shirya da kayan kari suka nufa,yayin da ni'imah ta miqe
"Bari na wuce,ko wajensu ummee ban shiga ba" sam bata son ni'iman ta tafi,taji dadin zuwanta,sai ta miqe tana fadin
"Bari na dauko mayafi mu shiga tare,nima ban je ba" tana nan tsaye sumayyan ta shiga daki ta dauko mayafinta,hankalinshi na kansu duk da yadda su'ad ta tare gaba da baya,da biyu take yin komai,a nutse ta qaraso bakin dining din a ladabce tace
"Zanje mu gaisa da su umme ni da anty ni'imah" ba tare da ya dago ba yace
"Ni din ma banje ba,ta wuce ma taho" sam bataji dadi ba,sai ta dawo a sanyaye
"Anty ni'imah tare zamu fito" murmushi ta sakar mata
"ba damuwa sai kun fito"daya daga cikin kujerun dake falon ta samu ta zauna tana jiranshi ya kammala,tana iya jiyo duka abinda su'ad ke fadi,hirar darensu na jiya take ta sako mishi yana basarwa,jin bacin rai na neman mamayarta ya sanyata miqewa tsam tayi shigewarta dakinta.
Tana gaban mudubi tana gyara zaman kayan makeup dinta ya shigo cikin nutsuwa,har yanzu ranta a bace yake,sai taqi dagowa ta dubeshi duk da yadda take jin tsaretan da yayi da idanunshi
"muje na kammala"ya fada a a taqaice
"Kuje na taho" itana ta maida masa da yanayin da yayi mata maganar,sarai ya fuskanci ranta a bace yake
"Muje nace"
"Nace na taho" shiru ya ratsa na wasu muntuna
"Ummu abdallah" da hanzari ta daga kai ta dubeshi,ita yake kalla da shanyayyun idanunshi masu dauke da wani irin magadisu mai qarfi da tasiri,yana kallon yadda cikin kwana biyu fatarta ta skma sauyawa tana wani qyalli,ko idanunshi ke mashi gizo?,ya tambayi kansa,shidai yaga sauyi qwarai tattare da ita,kawar da kanta tayi,saidai sunan yayi mata dadi har cikin ranta,cikin qaramin lokaci ya soma saukar da sanyi a ranta,shima sai ya dauke nashi kan,ya taka zuwa inda mayafinta yake ya dauko,ya iso gabanta,sai ji tayi ya soma yafa mata yana fadin
"Idan baki shirya takawa da qafafunki ba,am ready to carry you,komai ta fanjama fanjam" dan qanqani daga cikin aikinsa kenan,hakan ya sanya yana gamawa ta motsa tayi gaba yabi bayanta.
Kamar jiya haka suka rankaya su ukun baki daga,saidai ita bata dawo bangaren nata ba sai wajen qarfe biyu,bayan ta bada saqon abubuwa da take ganin tana da buqatar amfani da su,bayan ta kammala sallar azahar din dakinshi ta haura,dai dai sanda su'ad ta fito cikin heavy makeup,idanunta manne da sun glasses da cogen takalminta tana karkada muqullin mota tare da taunar chewing gum ta fice bayan ta watsawa sumayyan wani banzan kallo,kau da kanta tayi itama tana jan tsaki,ya ilahi batasan ma me yasa take kishin almustapha haka ba.
A yamutse ta tadda dakin,ita ta gyara kowacce kusurwa ta dakin,ta dauko sabon zanin gado ta sauya,ta gyara toilet,ta hada dukkan under wears dinshi ta tsaftace da hannunta ba tare da taimakon washing machine ba ta shanya cikin toilet din,tana saukowa aka kawo mata saqon,ta amsa ta nufi kitchen kai tsaye.
Lafiyayyar sakwara ta shirya tare da water leaf soup,wadda taji ganyen water leap,ogun,ganda,tsokar na da stock fish,blander ta jawo ta niqa aya da kwakwa da dabino ta hada lemo ta sanya a fridge,nono mai kyau da aka siyo mata ta hada da fura ta dama bayan ta wats kwakwa a ciki ta saka shima cikin fridge,sai data tabbatar da kammaluwar komai sannan ta rufe kitchen dinta da key,don bata mance rayuwar da sukayi da fa'iza ba,wuyat data sha kasancewar kitchen dinsj daya,kalanzir gishiri,suger duka a girkinta,murmushi ta saki tana rayawa a ranta,duniya labari,ko ina fa'iza ta shiga yanzu ohi,Allahu A'alamu.
Lokaci ta bata sosai a toilet tana murje jikinta,ita kanta mamakin yadda fatarta ke sheqi da laushi tayi,saidai tana ganin kayan gyaran jikin data yi amfani da su ne suka amsheta,kwalliya tayi maras yawa saidai ta dace da kyakkyawar madaidaiciyar fuskarta,ta sake kuma fito da armashin kyanta,ta jima tana saqe saqen wanne kaya zata saka,wando ta ciro belted high top wide leg trouser ash colour ta hadashi da long sleeve t.shirt fara qal wadda aka yiwa adon ash daga wuyan rigan zuwa qasanta,kisonta ta raba jelar gida biyu ta kama kowanne da qaramin ribbom ash,ba qaramin kyau tayi ba,duk wani tudu da kwari na jikinta ya fito turarukanta na musamman tayi amfani da shu,wadanda qamshinsu ke tashi a hankali har su gama cika hancin mutum,kwalabar turarenta babba ta dauka bayan ta kammala komai,ta zira wani irin plate din farin takalmi mai taushi ta soma bin duk inda burner take a gidan tana zuba turaren,a haka har ta qaraso falon.
Tana durqushe kusa da burner din dake bakin matattakala tana zuba turare a ciki taji an bude qofar sashen,batayi tsammanin ganin kowa ba hakan ya sanya ta fito haka,a nutse ta juya,almustapha ne a gaba su'ad na biye da shi
"Hasbunallahu wa ni'imal wakil" ya ambata yana lunahe idain nasa sanda idanunshi sukayi tozali da nata,karon farko da ya soma ganinta cikin suturar da ta bayyana duk wani structure ta jikinta,su'ad dinma idanuwanta na kanta,mamaki da kishi suka cikata,take wani bacin rai ya lullubeta,dama yarinyar tasan sanya ire iren kayansu?,ba sai an gaya mata tahowarta din nan taga shigen kayan a shagon da take siyayya acan,taso siyosu saboda tasan zasu burge almustapha kuma sun burheta itama,bugu da qari kayan sabbin design ne da suka fito sati sati uku kacal da suka wuce,amma saboda kudin hannunta yayi qasa ta haqura,kishin yanayin halittar da Allah yayi mata ya cika mata zuciya,ba zata manta ba har mai ta saya na qara mazaunai da qirji amma almustapha ya hanata shafawa,ya zaunar da ita yana gaya mata irin illolin dake tattare da irin wadan nan mayukan da kuma na bleeching,duk da bata taba bleeching ba ita,natural farinta ne,to amma ko banza yau gashi ya dauko mai abun,ita tana zaune,kewayeshi tayi ta wuce corridor dinta da zaya kaita ga dakinta kai tsaye,zuciyarta na tafasa,kamar ta shaqe kanta,ta wurga jakarta saman gado tare da tuje mayafin kanta ta wurgar shima tana yamutsa gashin kanta
"No....no,it can't" ta dinga maimaitawa tana girgiza kai,sai ta sake takowa a hankali ta dawo corridor din nata,ta tsaya tsakanin labulayen da suka rabata da hango falon kai tsaye,ta sanya hannu ta yaye labulen ta yadda zata iya hangosu.
Tattausan murmushi ya soma sakin mata idanunshi cike taf da mayen qaunarta,ita dinma duban shi take fuskarta dauke da murmushi,duban cikin idanunshi kadai sun gamsaf da ita,wani irin qauna take ji na daban na ratsata,qwafin gwiwa game da shi take ji,ya bude dukka hannayenshi yana mata alama ta taho,sai ta noqe kai kamar qaramin yaro yaso quya cikin wani salo na daban,ya motsa bakinsa cikin muryarsa da har gobe take sake daukaka darajarshi cikin idanunta
"Don't kill me babe,taho please" a yangance ta soma takowa,sai ya kasa jiranta har ta qaraso inda yake,ya soma shima takawa a hankali suka hade tsakiyan falon,kyakkyawan masauki yayi mata a qirjinsa yana sakin wawuyar ajiyar zuciya,baisan ta taka wannan matsayin cikin zuciyarsa ba karo na biyu sai a yau ya sake tabbatarwa,qamshin dake tashi kawai jikinta ya isar masa samun nutsuwa da kwanciyar hankali,sumbarta ya soma yi a ajejjere tako ina cikin nuna zallar soyayya da shauqi.
Cikin matsanancin tashin hankali ta saki labulen ta shiga dakinta a sukwane ta soma ball da jakarta data yar a bakin qofa
"No almustapha,no,why u r doing this" ta ambata tana dukan bango da hannunta,kana ta tafi saman madubinta ta soma watsar da dukkan abinda ta gani samanshi suna sauka qasa gami da tarwatsewa saman tiles,wannan bai isheta ba sai data dauki kwalbar turarenta ta doka jikin madubi,tunu ya tarwatse dai dai ya kuma yi silar yankarta.
Qarar wannan fashewar kayayyaki ita ta dawo da almustapha hayyacinsa,idan dai dai kunnuwansa ke jiye masa daga dakin su'ad ne,cikin hanzari ya raba sumayya daga jikinsa ya juya zuwa dakin,hawaye shabe shabe ya sameta tanayi bayan tarwatsa gashin ta dake daure da tayi,bata damu ba tana ci gaba da jifa da dauk abinda hannunta ya kai kai ciki har da t.v plasma dake manne a bangon dakin ta kwada mata make up kit din data wawuro,riqota yayi yana ambatar
"Meye haka su'ad,hankalinki daya kuwa" yunqurin qwacewa take
"Leave me almustapha,leave me" ganin haukar tata da gasje take ya sanyashi daka mata tsawa wadda ta sanya sumayya dake tsaye falo hankalinta yayi matuqar tashi
"U r mad?!,baki ganin wai me kike yi ne?"
"I know almustapha,am going to kill my self ma gaba daya" tsatstsauran riqo yayi mata sanda yaga tana laluben kwalabar dake farfashe a wajen,ya damqeta baki daya ya hankadata saman yamutsatstsen gadonta,ranshi ya kai qololuwar baci,sai kace tabin jinnu?,yanzun nan fa suka shiga gidan tare lafiya lau,binta gadon yayi ya mata riqon tsauri tana gunjin kuka tare da yunqurin qwacewa.
A qalla sun tasamma kashe mintuna goma a haka kafin ta soma sassauta haukan da take yi,sai kuma kuka da taci gaba da yi,cikin fargaba da nutsuwa sumayya tayi sallama bakin qofar dakin,a karon farko kenan,sanye da dogon hijabinta har qasa,waiwayowa yayi da jajayen idanunshi ya zubeta kanta,wadda ita kuma idanunta ke qarewa yadda dakin ya hargitse kallo,ko bai bata amsa ba ta soma hasashen abinda ke faruwa,ba zata manta ba,ba zata manya daren data yankeshi a hannu ba sanadin kishi
"Jeki am comming,everything will be okey" kai ta jinjina ta juya ta fice,idan da tasan ma abinda ke faruwa kenan ba zata bata lokaci ta shigo duba abinda ke faruwa ba,ranta ya dinga baci,me mata suka mayarda kishi ne?,tabbas babu halittar da bata da kishi,kishi halitta ce,kuma dole kayi kishin abinda kake so,hatta dabba tana da kishi,to amma meye amfanin hankali kenan?,meye amfanin ilimi?,meye amfanin girma da shekaru?,sai ta tsinci kanta ta mai jan tsaki data tuna zainab fa'iza karima ga kuma su'ad.
Miqewa yayi cikin takatsantsan don ma qafanshi da sau ciki ya laluba inda suka ajiyan kayan akwatin taimakon gaggawa,ya qaraso inda take,har yau qwalla na bin idanunta,tsugunnawa yayi ya soma mata dressing inda ta yanke ba tare da yace komai ba,idonta na kanshi ta soma maganganu cikin dashewar murya,tsaf ya fahimci abinda ya jawo mata aikata hakan,baya ga kishi har labe kenan ta soma?,abinda ya tunzura shi kenan,yana jin kamar ya dauketa da mari zuciyarsa na tausarshi,har ya kammala wanke mata tsaf,yayi kama hannunta ba tare da ya dubeta ba yayi mata allurar rage radadin ciwo ya maida akwatin muhallinsa ya juya da niyyar ficewa,qam ta riqe hannunshi ciki marairaicewa
"Kada ka tafi ka barni na roqeka almustapha,kada kaje wajen yarinyar nan,duk abinda kake so zan maka" idanunsa da suka sauyi launi kadai da ya watsa mata ya sata laushi kaso hamsin cikin dari
"Sake ni!" Ya fada a tsawace,sakin nasa tayi yaja baya baki bude tana kallonshi har ya fice a dakin,a falo ya tsaya ya fiddo wayarsa ya kira ummee yace ta turo ma'aikatan nan dakin su'ad zasuyi dan wani aiki,ya gama ya maida wayar aljihunsa ya wuce bedroom dinshi.
Har suka zauna cin abinci alamun bacin ran basu sakeshi ba,hakan ya matuqar taba ranra itama,yana zaune saman dining ya hade hannayenshi waje guda yana dubanta,qoqari yake ya saita kanshi don kada ya shiga haqqinta ko ya sanyata damuwa kamar yadda yaga kuzarinta ya soma raguwa,baki daya warmers din ta bude wanda take qamshi ya cika wajen,sai ta koma kujerar dake daura da shi ta zauna,idonta cikin nashi tana sakar masa murmushi,a hankali ta sanya hannunta saman hancinsa ta ja madaidaicin hancinsa da ya zauna das bisa fuskarshi ya qawata kyawunsa
"Me zaka iya ci ciki mu gani?,kai din cikakken bahaushe ne?ni duka ma fa nakeso ka cinye" ta qarashe maganar taba dage masa girarta,murmushi ya subuce masa lokaci guda,ya raba hannyenshi yana rarraba ido tsakanin kwanukan,abincin da ya jima baici ba kenan,kusan ya manta ma da ita a jerin abinciccika,ya maida kallonshi kanta
"Kina son miji lukuti me qiba kenan" qayataccen murmushi ta saki masa
"Idan na cinye wannan abincin duka yau anan gun zan kwana,bazan iya kai kaina daki ba" dariyar data riqe ce ta subuce mata,ganin yadda ya soma kwatanta yana shafa sumar kanshi
"Dariya kike?,ke zakiji a jikinki,don ba lallai ki iya daukan lukuti ba idan na qara qiba" kunyar maganar ta bata,sai ta soma gunqurin zuba masa abincin yana binta da kallo,komai nata burgeshi yake sake yi duk kwanan duniya,dabi'u da al'adun masu burgewa da kuma mabanbanta kullum yake sake gani wajenta,wasu ya manta da su tana tuna masa su daya bayan daya,wasu yana sane da su saidai baisan inda zaya gansu ba yau gasu cikin gidanshi a gabanshi,spoon ya amsa da niyyar fara ci,sau ta langabe kai tana dubanshu,yau wani irin abu take ji yana fusgarta zuwa gareshi
"I promise to feed you when we r together"
"Thanks" ya fada murmushin na fita a fuskarshi
"No" ta fada tana girgiza kai,ya gane mai take nufi,zuwa yanzu ya fara fahimtarta,tafi qaunar ya sanya mata albarka fiye da godiya,hakan baya rasa nasaba da muhimmancin albarkar wajenta fiye da godiyar,shima hancinta ya ja
"U r smart,barakallu fiki"
"Wa laka" itama ta maida masa,ta debi abinci ta kai bakinshi da cokali,sai yasa hannunshi ya amshe cokalin ya ajjiye
"Da hannunki nakeso ki bani" ba musu ta sanya hannun,ta miqa bakinsa yayi bismillah sannan ya soma amsa,kasa cewa komai yayi sai jinjina kai da yake a fakaice,wasa wasa sai gashi yaci leda hudu,ya dubeta suka hada idanu sai suka qyalqyale da dariya baki dayansu
"U r the best cooker apart from my mom da na sani" yabon yayi mata dadi qwarai,sai ta jangi jug na tana tsiyaya masa lemon da tunda ta fara zubashi ya zuba masa idanu,ta cika glasa cup ta kai bakinsa,ya kurba,sai ya cire yana duban cup din tare da hadiya na bkinshi
"Kunun aya?" Kai ta gyada masa,dariya ta subuce masa,yayi qas da murya
"Kinsan barnar da yake min ko?,halan kin shirya gyarota" ido ta zaro don har ga Allah batasan komai a kai ba,matsowa ya sake yi dab da ita,cikin kunnuwanta ya gaya mata komai,kunya ta sanyata sunne kai,sai yayi relax jikin kujera yana dubanta murmushi na fita a fuskarshi
"Can you remember our first night?,the day i start......." Sai ya kasa qarasawa yana dariya
"Hamza......shi ya hadani da shi,ashe gata yayimin,ya zama silar shigata wata sabuwar duniya mai qunshe da ababan mamaki da jin dadi masu tarin yawa,sai ta dire cup din tana dariya idanunta a qasa,riqe