Showing 342001 words to 345000 words out of 364327 words

Chapter 115 - KUNDIN KADDARATA COMPLETE HAUSA NOVEL

HUGUMA   

20 Aug 2024

40118

tana kiranta suna gaisawa lokaci zuwa lokaci.

         Yana nade saman gado yana duba saqonnin hotuna da lamin ke turo masa na gonakin da suke nema yadda noman yayi kyau,lokaci lokaci yakan daga kai ya kalleta sanda take shirin bacci gaban madubi,ya lura tunda suka dawo jikinta a sanyaye yake,haka yake,tana tuna wato rayuwa garanbawul ce,haka sharri tamkar jifa ne,duk sanda ka yishi komai daren dadewa sai ya dawo ya sauka tsakar kanka,a hankali ta hauro gadon,sai ya bar abinda yake ya zuba mata idanu kafin daga bisani ya bude mata hannayensa,dama abinda take jira kenan,ba bata lokaci ta isa jikinsa ta lafe tana shaqar tattausan qamshin da yake fitarwa,bugu da qari tafin hannunta na kan singalalin hannunsa dake cike da gargasa tana shafawa,hakan ya sakashi lumshe ido saboda yadda tsigar jikinsa ke zubawa
"Babe....mai ya sakaki mutuwar jiki haka?,ko baby ne?" Kai ta girgiza sannan ta soma kwatanta masa fa'izan da ya gansu tare,yace ya ganeta,nan ta bashi labarin yanayin da take ciki,shiru yayi yana jinjina mata,ba shakka ba kowacce mace bace haka,ya tabbata da wata ce dariya zatayi tayi shewa kafin ta shelantawa duniya,zata ce Allah ne yasaka mata abinda fa'izan tayi mata,sau gashi ita neman hanyar da zata fiddata daga cikin qunci take
"Kin taimaka mata ai ko?,ba sai an sake wani abun ba"shiru tayi kaman ba zata yi magana ba sannan tace
"A'ah....ranka ya dade da zaiyiwu a qara mata jari,a baiwa mai gidan wani qwaqwqwaran sana'a da zau kula da iyalinshi baki daya"
"Babe.....ta cutar min da rayuwarki fa?" Kai ta kada
"Na sani...amma na yafe mata,tunda gasji daga qarshe ni naci riba,Allah ya yimin kyakkyawan sakamako da gwarzon miji kuma masoyi irinka,daya tamkar da million" ta qarashe maganar cikin wani salo mai kwantar da rai,dariya ya dinga saki sannan ya ruqunqumeta cikin jikinsa yana jinta har cikin bargonshi
"Duk abinda kika ce shi za'a yi" ya rada mata akunne cikin salo na rada kaman wanda zai shide.

  ********   *****   ********

       Washegari shi da su'ad suka wuce jigawa,yayin da ita kuma ta tattara ya nata ta nata sai gida.

       A falo ta tadda mama ita da anty meena suna hiransu tamkar uwa da da,cikin farinciki suka tarbeta,mama kam kallon sumayyan take taba sambarka tare da godiya wa Allah,yaran meena biyu suna makaranta sai qaramin yasir sulaiman mai sunan malam ne,wanda baifi wata uku ba,gida kam yayi kyau masha Allah ya burge sumayya qwarai,ta dinga shiga tana fita tana godewa Allah,har da tsokanar mama cewa bata ga dakinsu ba,dariya anty meena tayi
"Kukam ai an gama yayinku tunda an yaye ku" suka sa dariya baki daya,a nan ta yiwa mama barka,da anty meenan ma baki daya.

      Kusan itama anty meena nan ta zauna da su,ranan bata je gidansu masu jego ba duk da kusan kullum sai taje,sai da zata dora abinci ta fita ta barsu,kafin sannan yaran sun dawo daga makaranta,abin mamaki duka sun santa,don yaya abbakar na nuna musu ita akai akai yana gaya musu sunanta,abinka da yaro da riqe abu,saidai basu sake da ita sosai ba kaman yadda suke sakewa da su halima.

       Tare malam suka shigo da yaya abubakar,kowannensu murna fal cikinsa da ganin sumayyan,sun sha hira sosai har ya abbakar ya gaji ya wuce bagarensa ya bar sumayyan da malam,labari yake ta bata kan irin ci gaban da rayuwa ta samu,yana sake jaddada mata irin soyayyar dake tsakanin baba prof da shi,da kuma yadda ko da yaushe zumuncinsu ke sake gaba yaba habaka,sosai take sake ganin qimar baban cikin ranta,ba shakka shi aboki ne kuma masoyi ne daya tamkar da dubu.

       Washegari suka dunguma gidan halima,baki daya harda yaran yaya abbakar nabila da yusuf da anty meena mamansu,almustapha ya bar mata mota da driver,wanda zai dinga kaita duk inda taje da buqatar zuwa,sanda suka je gidan 'yan barka nata shiga da fita,'yan uwan abdur rahamn,wasu ta sansu musamman na bangaren babanshi tunda sun hadu da mukhtar ta nan wajen,wasu kuma bata sansu ba,duk wanda ya santa a sanda take gidan mukhtar a yanzu da ya ganta sai ya kalleta ya sake juyawa ya dubeta,munagukan da a da suka cusguna mata baki daya jikinsu a sanyaye yake,baki daya sun kasa zama kusa da ita,kunya da kuma ganin yadda sumayyan ta sauya ta zama wata babbar mace duk ta cikasu,itakam bata dauki komai ba,tamkar basuyi mata komai ba haka ta sake musu fuska,abu daya ta sani shine an rige an wuce wajen,yanzu kam rayuwa ta baiwa kowanne certificate din abinda ya aikata,a gidan ta tadda zainab wadda shigowarta kenan,itama tana ta fama cikinta ya shiga wata na tara,sumayya ce nata keda wata bakwai da satittika,dukkansu suna zagaye da 'yar uwarsu,fuskarsu qunshe da farinciki,yaron yana saman cinyar sumayyan tana kallon tsantsar kama tsakanin yaron da babanshi abdurrahman,wato duk bawan da bai yarda da QADDARAR ubangiji ba lallai zai ci wuya cikin lamuranshi,matar mutun kabarinsa,yau ga yaron abdur rahman da halima saman cinyarta,sannan gata dauke da cikin almustapha,mutumin da ko a mafarki bata taba saninsa ba,sanda qaddara ta gindaya kuma ta sanshi din bata taba koda hasashen zama irin na auratayya zai hadasu ba,hira suke sosai gwanin sha'awa,wadda ke nuna zallar hadin kai da fahintar juna dake tsakaninsu,abdallah baya nan yana tahfiz sai azahar zai dawo.

        Sanda taga abdallah masha Allah,wani baragen girma gareshi,ya fara zama wani babba,ga wani hankali da nutsuwa tattare da shi,kana gani kasan ya samu isashshiyar tarbiyya,girma yake abdallan sosai,sanda ya ganta fuskarshi washe da fara'a ya iso gefan cinyarta bayan ya gaida duk wanda ya taras cikin falon yana fadin
"Ammi....ashe kinzo baki gaya min ba?"murmushu ta saki ranta fes,tana sake ganin girma da qimar abdur rahman har da ma haliman
"to ai gashi yanzu ka ganni ko?"
"Ammi kinga munyi sabon baby ko?,wai abba yace da ni yake kama?" Ya fada yana wasa da 'yan hannun jaririn dake cikin safar hannu,murmushi sumayya ta saki
"Sosai ma,kama kai" murmushi ya saki cikin jin dadi,nan ya soma bata labarin makaranta,kai kawai take kadawa tana murmushi,ganin abun take kaman mafarki,kaman ba ita ta haifi abdallah,qaunar yaron nata da tausayinshi suka dinga ratsata,ta kasa daurewa har sai data dora hannunta saman kanshi sanda ya kawo mata ruwa mai sanyi ya ajjiye mata yace tasha ta shafa a hankali ta furta
"Allah ya yi maka albarka kai da sabon qaninka mai kama da kai"
"Amin ammi na", basu suka bar gidan ba sai dare,don sai data jiraci dawowar abdur rahman tayi masa barka,yaji dadin zuwan nata sosai,yayi zaune abinsa a cikisu,sun dan taba hira,wanda yawanci kam abdallah ne,yanayin baiwar da Allah yayi masq,akwai basira da hazaqar karatu qwarai da gaske,wanda hakan ya sanya ake masa tsallaken aji,a hasashensu bazai wuce shekara goma ba zai shiga j.s,kayan barka ta yiwa babyn masu yawa kyau da tsada,akwati guda,sannan ta yiwa halima atamfofi biyu lave biyu,mayafi takalmi da jaka,ta mata godiya itama,saidai bataso godiyan ba,don bata ga abinda zata samu nak duniya 'yan uwanta basu mora ba,sai wajen takwas suka koma gida bayan sun sauke zainab har qofar gidanta suka taho da abdallah,tace bata yafe zuwan ha itama sai anzo mata har gida,tayi murmushi ta amsa mata,ranta fes ta koma gida,baki daya 'yan uwan nata suna cikin rayuwarsu cikin wadata da walwala,ba wata maiatsala a cikinsu,ci sha sutura da muhalli mai kyau kowacce bakin gwargwado ta mallaka.

       Washegari ya abbakar ya sake tareta suka sake lissafi kan dukiyar abdallah,abin ba'a cewa komai sai albarka Allah ke sawa dukiyar,ta nunku fiye da zatonsu,bayan sun gama ta fidda tsaraba cikin kwalaye wanda batasan da ita ba,almustapha ya tanada kawai taga ana sauke mata su,haka yake,mutum ne da idan zaiyi alkhairi bai fiya son a sani ba,zaiyi abunsa ne a boye,shi yasa ko zaman tsarabar bata san da shi ba,na mama daban na malam daban,har da yaya abbakar,saura yace ta baiwa wanda taga ya dace cikin 'yan uwa,sai yammaci ta sake shiryawa suka fice ita,abdallah,yusuf da nabila sai gidan anty yahanasu,ba qaramin murna tayi da ganinsu ba,duk da abdallah dama bai sati biyu abdur rahman bai kai mata shi ba,sun zauna hira nan taji duk abinda ke gudana,auren jamila da fatima Allah yayi za'a yi din,saidai kayan gado nason kawo tsaiko,don ma abdur rahman ya dauke nauyi duk abinda za'a ci ko a sha a bikin har a gama,kowa cikin dangi ya nade hannu,dama can danginsu ba masu riqe zumunci bane,hakan ya sanya ko sanda iyayensu suka mutu ita taci gaba da riqon mukhtar,sosai taji ba dadi,ta dauki nauyin kayan gadonsu jamilan da fatima,kunya da nauyinta suka ishesu,godiya suka dinga mata,itakam bata kula ba,iyalan mukhtar sunfi qarfin komai a wajenta,ko banza abdallah ya hada haduwar da babu rabuwa cikinta,data koma gida sukayi shawara da ya abbakar da malam,ta barwa yaya yahansu gidansu wanda suka zauna a qarshe ita da mukhtar kyauta,tunda yanzu dukiyar abdallah ba komai bane don su barwa yayan gidan,kuka kam haka ta dinga yinshi,har sai data saka sumayya qwalla,tace mata babu komai haka rayuwa dama take,nan yayan ta fara shiryen shiryen komawa,tunda fes yake akan shiha lokaci lokaci ayi gyara yaya abbakar bai barshi haka ha don kafa ya lalace,gidan da suke ciki kuma zasu saka 'yan haya,sumayya tace ta dinga amsar kudin tana buqatunta na yau da kullum da su.

      Suna suka sha hankali kwance,tayi kyau sumayyan sosai,duk wanda ya santa idan ya kalleta sai ya sake dubanta,kana kallon nata zaka san cewa nutsuwa da kwanciyar hankali sun samu muhalli cikin rayuwarta,a nan ta barsu drivanta ya dauketa ya maidata gida wajen mama,tafison ta ganta kusa da ita.

********    ******   ********

      Da safe suna zaune falon mama ita da abdallah,yusra da yusufa da maman suna karyawa,yaran na gabanta baki daya kowa na karyawa tana fama da su,gyarawa wancan kofi gyarawa wancan zama,kayan bacci je jikinta ko wanka bata yi ba,yunwar data ke ji ta sanyata zama karyawa,ya abbakar dake shirin fita shi ya shigo yana fadin
"Mama...ga surukinki zai shigo ki gaisa...da alama sauri yake halan ka wucewa zasuyi" sam bata gane wa ya abbakar din yake nufi ba,kafin ta farga har mama ta masa izini,sai muryarshi taji a bakin falon yana niyyar shigowa.

       Almustapha ne sanye cikin shadda dinkin tazarce,riga da wando,kanshi babu hula sai sumarshi dake kwance tana zuba qyalli,yayi kyau maqura har taji gabanta na faduwa sanda suka hada ido,ko yaya suka danyi kesa da juna na kwanaki sai taji ya sake zame mata sabo,ta soma tattare kofunan yayin da ya shigo ya tsugunna gaban maman yana gaidata,cikin jin kunya irin na surukuta suka gaisa,yana yi yana satar kallonta,ta kasa daga kai ta dubeshi kaman ta nutse,su yusra suka gaidashi yayin da abdallah ya isa gabanshi ya durqusa yana murmushi ya gaidashi,hannu ya miqa masa sukayi musabaha shina fuskanshi dauke da murmushi,yana son yaron sosai cikin zuciyarshi,saidai tarihin sumayyan da yaji yasan bazasu bashi shi ba,saidai yana kan bakanshi ko nan gaba sai ya dauke yaron,yadda yaron ua sake nutsuwa da girma sai yaji dama danshi ne,dama jininshi ne,saidai ko a yanzun yana jinsa cikin jikinsa tunda akwai jinin sumayya tattare da shi
"Tashi kije mana sumayya" mama ta bata umarni sanda almustaphan ya gama gaisheta ua fita zuwa dakin saukar baqi,a kunyace ta amsa,ta koma daki ta zura hijabi ya sake feffesa turare,dui da cewa qamshi ya kama jikinta,ko daga bacci ta tashi baka rasa jin qamshi a jikinta,don sai ta shafe loko da saqo na jikinta da turare ko ba kwananta bane kuwa,ko da basu tare.

       Yana tare da abdallah hannunshi cikin nashi,da alama tambayoyi yake masa kan karatunshi,yana bashi amsa,kuma yana bashi amsa yadda ya kamata don akwai alamun gamsuwa tattare da shi,shigowarta ya sanya abdallan zame hannunshi ya fita ya basu waje,tsaye tayi suna duban juna,ya miqe ya isa gareta ya hadata da jikinsa
"Meye haka?,salon horo ne ko kuwa?,ni zakiyiwa qwalele?,kinsam bazan juri kallonki haka ba ko?" Murmushi ta saka tana ajiye boyayyar ajiyar zuciya,dududud satinsu guda basu ha juna ba amma tana jin kaman sun yi wasu watanni masu dama
"Tsoro nake ji ne?" Ta furta a hankali
"Tsoron me?"
"Ina tsoron ko kazo tafiya da nine ba tare da na shirya ba,in sake tafiya in bar mama" murmushi mai sauti ya subuce masa,sannan ya soma rada mata
"Hakan naso matata,saboda mi kadai nasan yadda nayi kewarki,saidai idan hakan bai miki ba...zan iya zama na jiraki har tsahon sanda zaki gama abinda kike yi,ba abinda bazan miki ba,kinsan saboda me?" Kai ta girgiza alamar a'ah,sai ya juyo da ita suna fuskantar juna idanunshi cikin nata
"Ke din macace ta musamman,mai fifita farincikin mijinta akan nata,mai fifita buqatarta akan tasa,ina sane da cewa,sau tari kikan dauki zabina ki bar naki,kikan gabatar da komai nawa gaban naki,kin maida kanki tamkar baiwa a gareni" sai ya saketa ya durqusa gabanta kan gwiwarsa
"Don me nima bazan zama bawa a wajenki ba?,wannan shine qarshen adalcin da zan miki,Allah ya halicci zuciya da son mai kyautata mata da qi da kuma gudun duk abinda zai munana mata" bata ankara ba qwallar zallar farinciki ta subuce mata cakude da murmushi,jin kanta take tana shawagi a sama,cikin wata duniya wadda take mata kwatankwanci da duniyar SARAUTAR MATA,sai ya miqe da hanzari ya rungumeta ta baya saboda cikinta ya masa shamaki ta gaba,sun jima a haka sannan ya janye yana dauke mata hawayen da yatsansa
"Ko a yanzun ma ka buqaci mu tafi ni mai biyayya ce a gareka" kai yake girgizawa cikin farinciki
"A'ah....kije ki gama shirinki a nutse" kai itama ta girgiza
"Um...um,bazan barka kana jira ba haka noor,kaje ka dawo"
"Na yadda,amma zaki rakani asibiti?,zanje na duba bayin Allah"
"Sam'an wa d'a atan noor" murmushi ya saki kalman ta masa dadi,kissing dinta yayi sosai,sannan yace mata zaya dawo da yammar su je.

        A nutse ta fara shirinta,tana yi lokaci lokaci murmushi na qwace mata,lallai kam gaskiyar masu magana da suke cewa namiji tamkar yaro yake,sannan idan kika maida kanki baiwa shima zai zamto bawa a wajenki musamman idan yasan suka haqqoqinki da Allah ya dora masa.

       Da la'asar sakaliya ya iso kuwa,ya dauketa suka tafi,a nan yake tambayarta abdallah,tace babanshi yazo ua dauke abinsa,tana dariya tace shikam ko yauahe gani yake kaman zan daukeshi ne
"Akwai kam lokaci,lokacin da zamu daukeshin kuma babu yadda zaiyi" murmushi tayi don bata data cewa,kaman kowanne lokaci sunji dadin zuwanshi,suka dinga gaidasu cikin girmamawa,kan ya wuce office sai da ya bincika,komai yana tafiya kan tsari da kulawa tamkar yana nan,daga bisani suka wuce office din yana maqale da ita.

      Murmushi yaga taba saki sanda suka shiga office din,ya tambayeta mai ya fari?,sai ta kada kai tace mishi ba komai,kamota yayi ya matseta,ta saki qara a shagwabe,ya sake tambayarta,cikin muryarta mai sanyi tace
"Kawai ina tuna last zuwanmu office din nan,abinda ya faru" shima ya tuna sai ya saki murmushi ya lumshe idanunsa ya bude sannan ya kashe mata ido
"Na tuna babe....amma kada ki soma cewa zaki tsokaneni....kinsan me?,wani kwarjini kikamin wanda ban taba jin wata diya mace duk fadin duniya tun tasowata tamin ba a sannan na kasa miki scan,sannan ga wani shock da naji sanda naga skin dinki....kai babe,you are unique wlh" dariya ta saki ta dora kanta kan qirjinsa,daga gefe idanunta suka sauka kan hotunan mukhtar dake saman table dinsa,ta qurawa hotunan idanu,a hankali ya maida kansa inda yaga ta maida hankalinta,sai ya jata zuwa wajen,ya sanya hannu ya daga hoton yana kalla kafin ya dubeta
"Mukhtar?" Ya fada cikin sigar tambaya,idanu kawai ta zubawa almustaphan
"Am sorry" ya fada sannan ya hadesu waje guda ya yagasu qananu ya ajjiye saman teburin sannan ya waiwayo ya dubeta
"Ina da kishi a kanki babe.....am sorry if i hurt you" ya fadi yana duban idanunta da son karantar yanayinta,saidai taqi bashi dama,hannunta ya kama yana ci gaba da kallonta bayan ya matso da ita dab da shi har suna musayar numfashi
"Na yarje miki ki masa addu'a,ki sashi a addu'o'inki,amma banda nan" ya dora hannunshi saitin zuciyarta
"Nan din mallakata ce ni daya har ABADAN"knocking din da aka yi shi ya qwaceta,don ya soma dora mata wani nauyi,tamkar yana jiran amsar da zata bashi,daya daga cikin nurses din ne ta shigo dauke da file na mutanen da zai gani,cikin harshen turanci ya tambayeta na mutum nawa ne?,tace masa talatin,yace mata ta rage guda goman qarshe ta maida musu ashirin zai iya gani
"Sir....suna son ganinka da gaske ne goman da kace a cire din...."da hannu ya dakatar da ita kana ya mata nuni da idanu kan ta rage kaman yadda yace mata,qarasawa tayi ta irga ta debe din,sumayya ta matso kusa da shi murya can qasa
"sorry sir,ayi haquri a gansu" hararar wasa ya jefa mata
"Ke zaki tayani?,da wuya fa?"
"Na maka alqawarin ba zaka gaji ba,ina gefanka fa?"
"Really?" Ya fada yana dage mata girarsa guda daya,idanunta ta juya kafin tace
"Yes sir" tana sakin murmushi,kiranta yayi ta dawo da su din sannan ya sa mata kujera daura da shi ta zauna,da dai dai da dai dai patient ke shigowa yana dubasu,wani abun wanda yasan zata iya ya sanyata ta tayashi,wanda ba zata iya ba kuma yayi abinshi tana kallo,suna tsaka da haka wata budurwa ta shigo,kana kallonta kasan tana ji da kanta,cikin yauqi ta zauna kan kujerar da marasa lafiyan ke zama suyi bayani,sai fama take tana wani basarwa,sam bai daga kai ba bare yasan wanda ya shigo,hankalinshi na kan sumayya dake cike takardar wadda ta fita take shigar da wasu abubuwa da yace ta shigar,akwai fikira tattare da ita da basira mai dimbin yawa,komai tayi sai kaga hikima a ciki,tamkar likita haka ta tsara komai yana kallonta murmushi irin na gefen baki na fita kadan kadan,hakan ya sake sanyawa ya tafi da patient din data shigo
"Me kika karanta ne?" Ya tambayi sumayya fa kanta ke duqe tana rubuta kwanan wata,dubanshi tazo yi sai suka hada idanu da ita tana dubansu,hakan ya sanya maimakon ta bashi amsa sai ta masa alama da idanu na ana jiranshi,sai a sannan ya dauke kai ya dubi patient din,murmushi ta sakar masa,ya dauke kai yana bude file din nata
"Me sunanki?" Ya tambaya saboda yaga kaman ba suna kan file din da alama sabo ne
"Meela" ta bashi amsa tana yauqi
"Meye ne meela?" Ya tambaya a akausashe don ya soma jin haushin yadda take wani gwalangwaso
"Eh da shi ake kira ne amma real name din ja...."
"go straight


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login