Showing 78001 words to 81000 words out of 364327 words

Chapter 27 - KUNDIN KADDARATA COMPLETE HAUSA NOVEL

HUGUMA   

20 Aug 2024

40065

shi"malam ya fada cikin tausasawa. Haka malam din ya dinga lallashinta yana bata kalamai har ta samu ta danji sauqin zugin zuciyarta,saidai abinda take ji na game da kewar yaron har yau bai sauya ba.

       Data koma daki taga sauran kayayyakinsa kasa ci gaba da daurewar tayi,ba shakka raba da da uwa ba qaramin abu bane,shi yasa aka ce ko mutuwa tana shakkar idon uwa,yaya wadanda suka rabu da 'ya'yayensu suke ji rabuwa ta har abada?,ashe da sauqi ita tunda yana nan cikin duniyarta kusa da ita amma duk da haka ta gaza daurewa,kuka tayi mai yawan gaske wanda shi ya haifar mata da zazzabin da ciwon kai mai tsanani har ranar da aka daura auren,haka nan aka tattarata aka kaita dakinta tana mai ci gaba da kuka mai qunshe da abubuwa iri daban daban

     **** *9:30 pm*  *****

      Lukman Bashir shine asalin sunansa,haifaffen garin kano cikin qaramar hukumar kano municipal,yayi karatunsa iya N.C.E sai ya fada kasuwanci gadan gadan,mahaifiyarsa hajiya kubra shi kadai tallin tal ta haifa,hakan ya sanya ta dauki so da qauna da kulawa ta dora masa,wannan shine dalilin da ya sanya duk lokacin da yayi aure ta fuskanci yana mutuwar son matar take rabasu don wai ba zata bari a mallake mata yaro ba tana kallo,kasancewar gidansu daya part guda yayi mata da ya tashi ginin gidansa,a haka a haka ta sanya lukman ya rabu da mata kusan hudu kenan duk da cewa yana dacen matan aure masu matuqar haquri da biyayya saidai ita sam bata gani,haquri da biyayyar da sukewa lukman din ita ke jawo musu qauna gunsa,amma ita gani taje tsabar asiri ne matan suke yi,sam matan basu da sukuni,hatta zanin daurawa idan zai musu ita ke karbar kudin ta siyo ta bada adinka musu ita kuwa sai wanda ta zaba zata sanya,hakanan duk cikin matan da yake aurowa mutum daya ce ta haihu da shi don na wani dadewa take bari suyi ba,ita din ma a gidansu ta haife sai da ta yaye hajiyan tasa aka karbota,'ya mace ta haifa wadda ake kira da nuwaira.

       Hausawa suka ce alhaki kwikuyo ne,a irin haka ne Allah ya hada lukman da KARIMA gogaggiya mai idanu a tsakiyar kaa wadda ita ta haifa masa yara uku dukka mata zaitun marwa da radiya,da fari kariman lumbu lumbu ta yiwa hajiyan har ta saki jiki da ita,sannan daga bisani ta sanya gaba daya daga lukman din har hajiyan aka sanya su qarqashin ikonta,daga lukman din har hajiyan umarni suke karba daga wajenta,babu wanda ya isa ya tsallake abinda ta shimfida masa,sai a bayan idonta su yita takaici da jimami amma a gaban idonta ko tari ba wanda ya isa yayi,mutane da yawa sunyi murna sunyi shewa da wannan sauyi domin ya zamewa hajiya kubra izina.

       Tun bayan da ya auri karima bai kuma gigin qara wani auren ba sai a yanzu da yake KUNDIN QADDARArsa na rubuce da auren sumayya,sanda yake gaya mata zai qara aure a tsorace yake,ita kanta tayi matuqar mamaki,a fusace ta shiga dakinta ta kira wayar malaminta ta sanar masa,wayar tace ya kashe zaiyi bincike nan da awa guda zai nemeta,ya kuwa nemetan ya sanar mata wannan aure ba makawa sai an yishi saboda yarinyar nada addu'a hakazalika 'yar gidan malamai ce,wannan kalma ta sake tunzura karima ta sanya aka sake sabunta aiki mai kyau akan hajiya da lukman don kada sumayyan ta samu kafar rusa mata shirinta wanda ta riga ta qudurceshi cikin ranta,haqura tayi saidai duk wani harkar biki kama daga lefe da sauransu ita tayi su,komai sai data ninka kudinsa sannan kuma ta zuba abinda ranta yaga dama,sauqin daya gidansu sumayyan gida ne na dattako babu wanda ya damu dabtsada ko yawan abinda aka zuba cikin lefen.


         Qarfe tara da rabi na daren bayan an kaita gun hajiya an gabatar da ita yayin da ita kuwa hajiyan ke fadin tabi karima wanda ya baiwa kowa mamaki sannan aka dawo da ita dakinta wanda falo ne guda daya makeke sai dakunan bacci na kowacce mace da bandaki a cikinsa,sai dakin yara da mai gida kitchen da bandaki duk cikin babban falon,cikin falon dai ya kira sumayya don dama ita karima na zaune a falon tun kan a kawo sumayyan har kowa ya watse
"To sumayya wannan itace uwar gida na uwar 'ya'ya na,idan kika bita kamar kin bini ne,na auroki ne ba don bana sonta ba,bana so kuma ki raina min ita,hatta hajiya farincikinta shine farincikin karima da fatan kin gane" kanta ta cira a hankali tana dubansu baki daya,cikin zuciyarta ta furta
"Ikon Allah,yau kuma da wacce kalar Allah ya hadani?".
Miqewa kariman tayi cikin izza tana yatsina
" idan ka gama ka sameni a daki,kada ka wuce minti biyar"
"To....to to" ya amsa cikin inda inda tare da binta da kallo har ta wuce dakinta,da sauri ya dubi sumayya
"Amarya ta muje na rakaki daki kinji" ya fada cikin kwantar da murya,ba musu ta miqe tayi gaba mamaki na kasheta,wai dama haka lukman din yake?me yake shirin faruwa ne?.

      Bakin gado ya zaunar da ita yana duba agogo don kada yayi laifi
"Zauna bari naje,in Allah ya yarda zanyi qoqarin dawowa,ga kaxarki nan idan kina jin yunwa kici kafin na dawo" ya fada yana juyawa ya fice da sauri,binsa tayi dakallo baki daya qimarsa da mutuncinsa da take dan gani a da suna ficewa fit daga ranta,hawaye suka soma fita daga kuncinta data tuna rayuwar gidan mukhtar makamanciyar wannan,saidai sam da alamu bata kai qazancewar wannan ba,ita kuma nata salon QADDARAR kenan?. Juyawa tayi ta kwanta tana faman zubar da hawaye.

       Har bacci ya soma fusgarta taji yana ambaton sunanta sama sama,ta bude idanunta tana dubansa,murmushi yake yana kallonta shima tare da duba bakin qofar dakin kamar wani ya biyoshi,ganin ta tashi ta zauna ya sanyashi maida qofar dakin ya murza key,kamar wanda ke sauri jirgi zai tashi ya barshi yake magana
"Tashi maza ki dauro alwala,ina fatan dai kinci abincin ko?.....kinyi sallar isha'i?.....dauro alwala sumayya babu lokaci...."ya fadi yana satar kallon qofar dakin
Cikin mamaki take dubanshi duk ya wani firgice,lokaci kada ya qure kamar yaya take tambayar kanta
" don Allah tashi mana sumayya kada ta....."bai qarasa fada ba aka fara dukan qofar kamar za'a ballata
"Innalillahi wa inna aihi raji'un" ya fada yana dafe kansa.
"Zaka bude ko sai na sassaba maka,maci amana" inji mai buga qofar,jiki ba qwari ya nufi qofar ya bude mai bugun ta fado dakin tana raba idanuwa,kubra ce sai data qarewa dakin kallo ta fuskanci babu abinda ya faru sannan ta kalleshi
"Ni zaka ci amana ka karya alqawarin daka yimun?,to wallahi ko kwana a dakin baka yi butulu kawai,maye,tunda ni ban isar maka ba,wuce muje nace ka tsaya ka kafeni da idanuwa" sai ya waiwaya yana duban sumayyan har sai data ingiza qeyarsa sannan ya fice yana waiwaye.

     Kan sumayya ta dawo da kallonta"da sauran quruciyarki amma kin zabi nakasta rayuwarki,idan don kwanciyar aure kika zo gidan nan to kinyi babban kuskure don yadda kika zo haka zaki koma,don babu wasu 'ya'ya da za'a haifa a gidan nan sai nawa yaran,itama wadda aka haifa din don uwarta ta rigani zuwa ne,wlh da ni na rugata zuwa da bata isa ta haifeta ba,keda lukman kuwa saidai kallo"
"Ke lukman ya dama,kuma ta Allah ba taki ba,ni an bani ilimin yarda da QADDARA mai kyau ko akasinta,hikinar ubangiji kuma yawa gareta,hakanan sanin gaibu sai Allah,duk kuma nisan jifa wataran qasa zai fado,mai yiwuwa ma idan ya tashi fadowar ya dawo tsakiyar kan wanda yayi jifan"
"Ke ki iya bakinki wallahi idan baso kike kiyi kwanan gidanku ba"
"Idan kinso kina iya karbe aron numfashin ma da kika bani idan yaso nayi kwanan kabari baki daya" sumayya ta fada hankalinta kwance,don ya zuwa yanzu tana jin ta gama daukar haquri da rainin wayon kishiya,bata cuce su ba don me su zasu dinga cutar da ita,tabbaa dafi da gubar zainab har yau bata bar illata zuciya da gangar jikinta ba,don kusan ita ta zama silar data sake cillota wannan muhalli da take ganin wata rayuwa miji ke biyayya wa mata. Mamaki ya cika kariman don ta jima rabon da a mayar mata da magana haka,sai zuciyarta ta tuna mata daga inda sumayya ta fito,take gumi ya fara tsatstsafo mata,tabbas sai ta sake shiri a kanta,qwafa taja sannan ta juya tana fadin
"Da karimatu kike zancan lallai bakisan wace ni ba"bata yi nauyin bakin maida mata amsa ba don kada ma ta fita bata ji ba
"hakanan bakisan wace sumayya ba,ki zuba ido kisha kallo". Bayan fitarta muqulli sumayya ta sanyawa qofarta ta shiga toilet ta daura alwala,sam bata ji wata damuwa na barinta da angonta yayi ita daya a dakin ba,kaya ta fiddo ta sauya wadanda zata sake a cikinsu sannan ta sanya hijabi ta tada sallah,kyawawan nafiloli ta raya daren sosai da su kafin bacci ya rinjayi idanuwanta.

*asuba ta gari amaryar lukman*

*mrs muhammad ce*👑

📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖


*~NA~*

*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*

*WATTPAD:HUGUMA*

*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)

4⃣1⃣



*Bimillahir rahmanir rahim*

*wattaqu yauman turja'una fihi ilallah,summa tuwaffa kullu nafsin ma kasabat wa hum la yuzlamun*

*_KUJI TSORON WATA RANA DA AKE KOMAR DA KU IZUWA GA ALLAH A CIKINTA (RANAR LAHIRA),SANNAN A SAKAWA KOWACCE RAI ABINDA TA AIKATA (SHARRI KO ALHERI)ALHALIN SU BA'A ZALUNCESU BA(BA WANDA ZA'A ZALUNTA DUK ABINDA KA AIKATA SHI ZAKA GANI)_*

______________________________





Qarfe tara na safiya tayi wankanta,ta shirya cikin atamfa dinkin riga da zani,ba wani kwalliya tayi ba amma tayi kyau,dakin ta sake karkadewa ta goge sannan ta koma bakin gadonta ta sake kwanciya,idanunta ta lumshe tana saqa da warwara,kewar abdallah take ji sosai cikin zuciyarta har qwalla na shirin kawo mata,tunani ne fal zuciyarta tana wassafa yaya rayuwa zata kuma kaya mata cikin wannan gidan.


Hayaniya ta dinga jiyowa cikin falon da surutai,ta bude idanunta ta kalli agogon dakin,goma tayi har da mintina arba'in da biyu,saita bude sif dinta ta ciro hijabi ta zura kana ta sanya silifas dinta ta murda qofar dakin ta fito.


Duk uban hayaniyar da take ji yara hudu ne cikin falon,yarinyar farko wadda ita ta sake hautsina yanayin falon ma hakimce kan kujera kamar wata babbar mace duk da du du du ba zata wuce shakara sha uku ba,kallo take a tashar mbc three ta qure volume kamar ita da mutum dari suke kallon,sai yarinya ta biyu wadda batafi shekara uku ba dake zaune qasanta kan carfet taci uban indomie ta hadeta da ruwan shayi tana wasa da ita,daga can wajen step na dining kuwa wasu yaran ne su biyu,daya shekarunta goma daya takwas suna karyawa,su biyun kadai sun dame gurin kamar qanwar tasu dai,ta sake wurga idanunta,wata yarinya ce data tasamma zama matashiya wadda ta kusa shekara goma sha hudu takure a saqon kujeru,kallo daya zaka mata kasan daban take kamar yadda kamanninsu ya bambanta da sauran yaran dake falon,don dukkansu kamarsu daya ita kadaice kamarta daban kamar yadda ta fisu kyau baki dayansu.


Dukkansu sun ga fitowarta saidai babu wanda ya kulata,ta dubi qofar dakin karima wanda ke garqame ta sake dauke kai
"Ina kwana anty"
Taji an ambata daga bayanta,saita waiwaya,yarinyar dake zaune ce saqon kujera ta gaidata tana murmushi,maida mata murmushin itama tayi tana mamakin zarnin dake tasowa daga jikinta
"Lafiya qalau,an tashi lafiya?,me sunanki?"
"Nuwaira"
"Sunan mai dadi" sai tayi murmushi tana cewa
"Na gode anty".
"Ko zaki rakani wajen kakarku?"
"Wa?,hajiya"
"Eh"
"Muje in rakaki anty" ta fada tana wucewa gaba sumayya na rufa mata baya.


"Wallahi bari umma ta fito sai na gaya mata duk abinda kika yi,bata ja mana kunne ba?" Yarinyar daje saman kujera ita ta ambaci hakan tana jijjiga kai,cak yarinyar ta tsaya kamar an ambata mata mala'ikan mutuwa,idanunta na tara qwalla tace
"Kiyi haquri don Allah kada ki gaya mata"
"Wallahi sai na fada saidai ta kasheki" ta fada tana buga hannu alamun babu fashi,wani abu ya tsayawa sumayya a wuya,takaici da mamaki suka cikata,sai ta janye nuwaira tana fadin
"Muje babu abinda zai faru dake kinji kada ki damu" jikinta babu qwari ta bi sumayyan suka fice.


Kafin su qarasa gun hajiyan sumayya ta dubeta
"Me yasa kinsan kina fitsarin kwance da kika tashi baki sauya kayanki ba nuwaira?,kinsan fa ba'a son mace da qazanta" sai yarinyar ta fara qwalla ta soma sharewa tana cewa
"Wallahi anty tunda bana fitsarin kwance,saddiqa keyi sai a hadamu kwanciya gado daya,idan tayi duk sai ya jiqani,idan ta tashi ita sai nuratu ta sauya mata kaya,ni kuma ba zan canza ba har sai umma ta gama bacci tayi wanka ta fito sannan zata nunan wadanda zan sauya din,koda asuba bana samu nayi sallah sai rana ta fito" ta fada da alamu abun na ci mata tuwo a qwarya,shiru sumayya tayi tausayin yarinyar na kamata,wannan wanne irin zalunci ne,tun kallon farko da ta yiwa yarinyar ya nuna tana jin jiki a gidan,amma tana tunanin kamar ita ce yarinyar nan daya da karima jiya ta gaya mata uwarta daban,don ta tabbatar sai ta tambayeta
"Ina mamarki to?"
"Mama na tayi aure a wani gidan,tun kafin a yayeni aka karboni aka bawa hajiya ni,to da abbanmu ya sake aure ya auro umma sai umman ta karbeni nake gunta"take tsanar karima ta darsu a zuciyar sumayya,lallai ba shakka bayan shirkar tsafi ma harda azabtar da yarinyar da bata ji ba bata gani ba,wai me mutane suka dauki duniya ne?,kowacce mace son kanta ya mata yawa?,burinta ta mallaki miji ta rabashi da kowa nasa?,ta rabashi da 'yan uwansa da tazo ta samesu tare,'yan uwa da suka zamar masa bango marufar asiri tun yana zanin tsumma har kawo yau,ta rabashi da duk wani alkhairi uwa uba ta rabashi da mahaliccinsa,ta sakashi a musibar da ranar gobe qiyama bazai iya tsallaketa ba,ta rabashi da hankalinsa bare ya kula da addininsa,wanda ya cancanci a bashi haqqinsa ta hana ya basu yanzu duka wannan qauna ce?,sai tace sonshi take shi yasa ta aikata haka,wannan ko babban maqiyinka ba shakka iya cutarwar da zai maka kenan,da irin wannan tunani suka isa bangaren hajiyan.


A duqe suka sameta tana share falon nata dake malale da carfet,kallo daya sumayya tayi mata ta fuskanci shekarunta basukai ace tayi tsufar da tayi a yanzu ba,da sallama suka shiga ta dago tana amsa musu riqe da qugunta wanda bisa dukkan alamu ciwo yake mata,nuwaira ce ta gaisheta ta amsa babu yabo ba fallasa yayin da sumayya ta qarasa tana amsar tsintsiyar hannunta tana gaidata,amsawa tayi tana dubanta yayin da sumayya ke qarasa mata sharar har ta kammala sannanbta dawo inda hajiyar ke zaune tana yiwa nuwaira masifar sai zuba zarni take taje bandakinta ta wanke jikinta,mamaki ya cika sumayyar,to ko batasan meke wakana bane cikin gidan?,batasan ba laifin nuwairan bane karima ce ta cancanci fada idan da duka ma ayi mata?,tashi yarinyar tayi ya shige bandakin hajiyar sannan hajiyar ta maido kallonta ga sumayyan
"Ban gane fuskar ba wace ce ne?" Murmushi kawai tayi ta dan sad da kai
"Oho,ko amaryar lukman ce" kai sumayyan ta gyada.


Shiru ne ya biyo baya,hajiyan na dan satar kallon sumayyan,sai taji ta dan sake da yarinyar duk da ba hira suke ba zaman kurame ne,a haka har nuwaira ta fito daga bandakin sanye da jiqaqqun kayanta wadanda ta wanke bayan ta dauraye jikinta ta maida su a haka
"Wani nuwaira nikam bakuyu abin kari bane yau,gashi har sha daya na shirin gotawa yau ba'a kawo kin komai ba,ko luba mai aikin bata zo bane?"cike da madaukakin mamaki sumayya ke sauraron zancan
"Tazo hajiya,bansan ba'a kawo miki ba,don ko nima yau ban karya ba,naga dai su nuratu na karyawa ni ma ba'a bani nawa ba"ta fadi babu alamun damuwa tattare da ita bisa dukkan alamu ta riga da ta saba da hakan,yamutsa fuska hajiyan tayi
"gaskiya na fara jin yunwa wlh,wannan abu Allah kayi mana maganinsa"
"Amma hajiya ai naga kina da sauran kayan abincinki da kika ce bazaki iya ci gaba da girki ba ai abba bai debe su ba ko?"
"To idan banda abinki ina fama da lalura ina zan iya,sharar ma don bazan iya zama cikin qazanta bane nake daburtawa nake yinta" ta fada ta muskutawa da alamu yunwa na sakadarta,tausayinta duka sai ya kama sumayya ta dubeta
"To hajiya idan ba damuwa sai na shiga na girka miki ai ko?"haba ta riqe
" a'a,har kya fara shiga madafi ta sanadina?,ki barshi babu komai idan da sabo ai mun saba da irin wannan gashin,ke dai kawai Allah yayi mana magani"murmushi tayi kawai ta miqe tana tambayar nuwaira inda kitchen din yake.


Sallamar karima a gadarance ita ta maida hankalinsu bakin qofar,ita ke gaba gogan na binta a baya riqe da wani dan qaramin flask wanda bako shakka abun karin hajiyan ne a ciki,idanunsa na kan sumayya yana faman sakar mata murmushi ,wani takaici da haushinsa suka qumeta saita dauke kai tana jin kamar taje ta shaqeshi,haka nan kawai taji jarumin namiji yana burgeta,sai ta tuna sanda zainab ta fara murza kambunta lokacin tana gidan mukhtar,tabbas ko a lokacin mukhtar din kan tauna tsakuwa wani lokaci.


Hajiyan da za'a yiwa sannu a gaisheta ita ke faman yiwa kariman sannu tare da gaisheta,lukman ya koma gefan hajiyan yana gaidata cikin dari dari suke gaisawar kamar suruki da suruka duk don kada su batawa karima rai,baki sumayya ta saki tana kallon abun mamaki bayan hajiya ta bude flask din da aka kawo mata,wani gantalallen soyayyen dankali ne da rabin wainar qwai babu ko tea amma hajiyan sai godiya da sannu take mata
"Saidai yau kici haka hajiya don kafin na fito jikokin naki sun shanye shayin"
"Ai babu komai,idan baka yiwa jikanka ba wa zaka yiwa" ta fada fara'a kamar gonar auduga.


Kallon sumayya karima tayi bayan sumayyan ta gaida lukman wanda ke faman binta da kallo kamar tsohon


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login