Showing 177001 words to 180000 words out of 364327 words
ji,ta kasa zama waje daya sabida farinciki,ba shakka tana mai tabbatarwa kanta sumayyan tayi kyakkyawan gamo mai dauke da dumbin alkhairai
"Kiyi jaquri sumayya,na miki shishshigi,saidai ina mai baki haquri tare da neman alfarma kan ki yimin wannan alfarmar kada ki watsan qasa a ido" maganar malam din ta hadu ta sake yi mata nauyi a ka,duk da halin ha'ula'in da take ciki amma haka ta tattara kalaman
"Don annabi ka daina fadan haka malam,ka daina bani haquri,ni bani da wani da na cancanci a nemi alfarmata a kansa,kaine silata kai ka haifeni,duk yadda kayi da ni malam daidai ne,na tabbatar ba zaka taba cutar da ni ba,na amince na miqa wuya a gareka,roqon da nake maka kadai shine malam ka bini da addu'a,ka sakani cikin kowacce addu'a taka,Allah ya qarfafeni,ya hanani gazawa bare na watsa maka qasa a ido,na samu juriya mai yawa da zata kaini ga cika burinka" tana kaiwa nan ta gaza dairewa,sai ta fashe baki daya da kuka zucuyarta na tuna mata abubuwa masu yawa,wadanda suka faru da wadanda kan iya samunta a gaba,fata take Allah yasa SHAFUKAN KUNDIN QADDARARTA sun qare ashe akwai wasu sabbin shafukan kar a gaba,sai yaushe ne zata kammala bitar wannan kundi mai dan karen wuya da sanya zuciya da gangar jiki yin rauni,rauni kuwa bana wasa ba,ya barwa zuciya da rayuwa tabbai masu wuyar warkewa,masu wahalar sha'ani da sarrafawa tare da tanqwara zuciya a kansu,duk wanda ke dakin jikinsa yayi sanyi,sunsan mai take tunawa
"Insha Allahu sumayya daga wannan karon ba zaki sake kuka ba,da yardar ma duka lokacin dariyarki ne yayi,na tabb I understandatar da cewa ban kaiki imda zaki wulaqanta ba,na kaiki ne cikim ahalin da suka gaji karamci da mutunci tun daga tushe,ko bana raye ina da yaqinin muhtari ya isheki uwa da uba ma baki daya,addu'a kuwa kullum kina cikin addu'o'ina,zaki rabauta sumayya da yardar Allah,tashi kije,Allah ya albarkaceki da dukkan wani abu da ya shafeki"
"Amin" baki daya mazauna dakin suka amsa,sai ta kasa tashi saida anty dije ta kamata,kai tsaye dakinta ta kaita ya zaunar da ita sannan ta zauna gefanta tana kallon yadda take kuka kamar hawayenta zai qare,bata cemata ta tafas ba har sai data soma tsagaitawa don kanta,bawai don ta gaji bane ko ta samu sassaucin da take son samu,ta tsagaita ne saboda yadda idanunta suka soma radadi da kuma yadda ta fuskanci antyn nason tayi magana da ita
"Sumayya kuka kike saboda auren almustapha?" Ta jefa mata tambayar kamar wadda batasan batun ba
"Na tabbata bakisan waye almustapha ba,banda haka da sai nace kukan da kike kin yiwa Allah butulci" jajayen idanunta ta daga ta kalleta alamar tamabaya,ciki yaqini anty dijen ke kada kai
"Tabbas abinda na fada hakan yake,kinsan irinsu mustapha suke tsada a wannan lokaci?,kinsan yadda mustapha ya tara managartan halaye kuwa?,kin taba tambayar kanki me yasa su'ad ke tsananin kishinsa duk da kishin banza take tunda batasan yadda zata riqeshi ba?,kin manta waye baabaa da karamcinsu?,kina zaton idan kika qi aurensa zaki ci gaba da zama haka ba tare da kinyi aure ba?,kinwa kanki wadan nan tambayoyin?" Kai take girgizawa bayan ta gama sauraronta,cikin rawar murya ta soma furta
"Anty a fuskata almustapha bashi da kirki,bai taba kyautata min ba ko sau daya,anty...kin manta yadda auren soyayya ke kayawa a wannan zamanin ina ga irin wannan?,baki daya almustapha anty ba ajina bane kamar yadda nake nima ba ajinsa bace,babu dacewa tsakanina da shi anty,komai nawa da nashi ya sha banban,ra'ayi yanayi al'ada wayewa da dabi'u,ta yaya zamanmu zaiyi daidai,baya ga haka ma baki daya anty KISHIYA!,kishiyar ma irin su'adah,kin manta anty ina kika baro wannan?,kin manta kishiya duk inda na shiga itace babbar qalubalena,bayan bansan me na musu ba,ko don ni yarinyace?,ko din bani da qarfin qwatarwa kaina 'yanci,ko don ban iya mugunta da baqin hali ba,wadan nan sune dalilan?" Ta fada wasu hawayen masu dumi na bin kuncinta,hannunta anty dije ta riqe tsam cikin nata,madadin taga tashin hankali bisa fuskarta sai taga murmushi ne ma kwance kan fuskarta
"Almustapha?,ko ba haka bane sunanshi?,kin manta shi namiji ne?,namiji kuwa ko wayeshi ta bangaren zamantakewar auratayya dole ya sakarwa mata,ki manta da wannan ki cire rashin soyayya a tsakaninku a matsayin matsala,kishiya ita kike tsoro?,ina zaton zuwa wannan lokacin kin horu sumayya,meye yayi saura meye bakiji baki gani ba,sai d'ai d'ai,wannan karo ki sama ranki cewa kishiya ga gama yin nasara a kanki da yardar Allah,waccan karon ma dan dai kawai yana cikin KUNDIN QADDARARKI ne,ke mai bawa wata labari ne,dame kishiya zata tsorataki sumayya,bayan kina da Allah,kina da tsarkakakkiyar zuciya,ke matuqar su'ad ma ta baki tsoro sumayya ke kika so,ki kwantar da hankalinki damuwa ba taki bace,bakisan sirrin da Allah ya boye ba har ya turo baabaa dai dai wannan lokaci,bana son qara ganinki hawayenki daga yau" Kai kawai ta gyada mata ba don tana tsammanin samun salama cikin ruhinta ba,komawa tayi kawai ta lafe kan gado kanta na sarawa,ita kadai tasan me take ji,kai kawai take mirginawa tana jin nauyi da girmam zancan a qirjinta,su halima da zainab ne suka shigo a sanyaye saboda ganin yanayin sumayyan,antyn tace suje kawai ba zata samu zuwa ba ita da sumayyan,bata son ta tafi ta barta a yanayin da take ciki,wayarta dake gefanta tayi ruri,kiran abdur rahman ne,idanuwanta ta runtse tana kiran sunayen Allah,sai a sannan ya fado mata,me zata da shi?,me zata gaya masa ya yarda da ita,tabbas bata da abinda zata ce masa,hakanne ya sanya ta qyale wayar taci gaba da rurinta har ta katse don karan kanta,qarar wayar kawai qara mata ciwon kai yake,wanda zuwa lokaci wani zazzafan zazzabi ya rufeta ta kwanta sosai,saidai bata bari kowa ya gane ba.
****** ******* ********
Tunda ya isa gida kafatanin al'umar dake cikin gidan suka fuskanci akwai wani gagarumin al'amari na farinciki da ya faru da mai gidan,tun daga manyan ma'aikata na gidan har qananu,take ya yiwa kowa qarin albashi sabida tsananin farinciki da nuna tsantsar godiyarsa ga Allah.
Bai samu ganawa da matan gidan ba sai bayan sallar magariba,ya warware musu komai,babu abinda ummee tace,ita kanta tasan yaron nata yana da buqatar sauyin rayuwa,kawaici kawai irin nata yasa basa tsomala baki cikin lamuransa,saidai sauyi wanne iri?,sauyin zai yiwu kuwa ta wannan bangaren,bayan kowa yasan ra'ayim almustapha wajen zabar matar aure?,kai hasalima kaf tarihin rayuwarshi bashi da muradi ra'ayi ko sha'awar yin mata biyu sam sam,bata manta yadda ya dinga qananun maganganu sanda yayansu adam zai sake aure na biyu,saidai a tarbiyyarsu sam babu musu ko jayayya kan duk hukuncin da jagoran gidan ya yanke,saidai su tayashi bin dokarsa ko hukuncinsa,bangaren anty maamaa ma tayi farinciki,don a dan zamanta da sumayya ta karanci halayenta,ta kuma san ta sha banban da halayyar su'ad,saidai itama tata fargabar ta yaua almustaphan baqin bature dan ra'ayin riqau mai doka da qa'idoji zai amshi wannan lamarin,gashi uwa uba baban yaja kunnen kowa da kada wanda ya sanarma almustapha maganar shi da kansa zai sanar masa,kome meye tasan na dan lokaci ne zai wuce,to baki dayansun masu biyayya ne gareshi,sannan babu wanda baida burin ganin farinciki cikin rayuwar mustaphan.
Anty farida da huda kam da suka ji lamarin har wani ihun farinciki suka saki,kasa zama sukayi sai da suka dangana da baabaan suka yi masa godiya tamkar su ya yiwa,murmushi kawai yayi yasan lamarin na damun kowa,koma dai meye shi ya fisu farinciki da shigowar jinin sule cikin tashi zuriyar.
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
[23/02, 11:51] Beesama Zamani Wrt Grp: ✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
7⃣4⃣
*Bismillahir rahmanir rahim*
*Allah S W T yana cewa*
*KACE HAQIQA MUTUWAR DA KUKE GUJE MATA MAI RUSKARKU CE,SANNAN KUMA KU KOMA IZUWA GA MASANIN ABINDA KE FILI DA NA BOYE YA BAKU LABARIN ABINDA KUKE AIKATAWA*
Ya Allah kasa ta ruskemu kana masu farinciki da mu,muna masu farincikin haduwa da kai
______________________________________
Gaba daya ta koma ta zama wata irin cikin kwana biyu kacal,duk wani kuzari da buri data ci na bikim zainab yayi nashi wuri,tsantsar tashin hankali take shiga a duk sanda ta tuna lamarin dake tunkarota,ko ya zata qare?,ko meye zai faru da ita wannan karo?,shine tambayar da take yawaita yiwa kanga,uwa uba Abdallah da ya tsaye mata a rai,ana ya gobe kamu nafisa ta iso gidansu,wani kallo take binta da shi tana tabe baki
"Ke yanzu sai kace wadda zatayi auren fari kamar wadda yau zata fara zama da kishiya shine kika bi kika susuce haka?,a haka zaki qwaci kanki duk kin fafa zabgewa kina ramewa?,amma wallahi kin bani kunya" cewar nafisa,daga kai tayi tana kallonta tare da mamakin wanda ya gaya mata zancan
"Me kike kallo na,munyi waya da amira ta gayan komai,ta kuma ce tana kiran wayarki amma kullum switchoff,na gaya mata zan shigo kanon tace na duba mata ke don Allah" ta sake fadi tana duban sumayya,fada ta zarce da yi maga,kuka ya qwacewa sumayyam,wau su don Allah ita kadai take gano abinda take ganowa,su basu hangen komai,ta gama fadanta sannan ta koma lallashinta,inda daga qarashe ita ta tilastata ta miqe tayi wanka tace zata rakata siyayya,jiki babu qwari haka ta shirya,ga zazzabin dake sakadarta a hankali,bugu da qari ga wani ciwon mara da ya saukar mata,wanda bata sani ba ko tashin hankalin da take ciki ne ya jawo shi oho.
Wani katafaren shago wanda ke saida kayan jiki na zamani nafisa ta kaisu,da idanu sumayya ke kallonta sanda take loda kayan tana zaba,harda wanda sumayyan yanzu ke amfani da shi tun wanda ta taba siya mata a uk har yau da shibtake amfani da yake ya karbeta,suna cikin mota take shaida mata yadda zata yi amfani da sauran,haushi ya kama sumayyam,yamzun suna nufim wami namiji zata yiwa hidimawa jikinta saboda za'a daura mata aure da shi
"Wallahi da kin gayan ni kika siyawa bazan barki ba,sabida asarar kudinki kawai kika yi babu abinda zanyi amfani da shi cikinsu" a fusace nafisan tace
"Wallahi baki isa ba kinyi kadan,amfani da su wallahi ya wajabta a kanki" ganin yadda nafisan ta hasala ya sanyata yin shiru,saboda ko qwaqwaqwarar magana bata sonyi yanzu kanta zau fara sara mata.
A bangaren baabaa kuwa shirin daurin auren yake babu kama hannun yaro,kai kace wannan shine karon farko da za'a yi daurim aure cikin familyn baabaa prof din,ana ya gobe daurin aure suka baro abuja suka sauka gidanshi dake kano,saboda ya kasance kusa da abokinsa,duk wanda ya dace ya san da daurin auren babu wanda baabaa bai aikawa ba.
Duk abinda ake idanu ne nata sai ta koma 'yar kallo sabanin daa da itace amara,katunan daurin aure masu dan karen kyau tsari da tsada baabaa ya sanya aka buga ya baiwa malam wani shima ya raba wani,duk wanda yaji daurin auren ya zama na mutum biyu harda sumayya sai yayi mamaki,saboda kowa yasan babu ita a batun,da kansa baba ya sanya cikin kwanaki hudu aka yima sumayyan akwatu uku na suttura wadanda zata sanya kawai bawai lefe bane,lefanta yace sai almustaphan yayi kamar yadda ya yiwa su'ad,kaya ne masu kyau da tsada dinkakku,kama daga shadda laces atamfa material sa sauransu.
Da ido kawai take binsu lokacin da aka zo yima amarya zainab lalle,almara kawai take ganin komai,wai ita za'a daurawa aure nan da kwana uku?,abinda ko cikin mafarki bata taba hasashensa ba,qememe taqi bada hannunta ayi mata komai,anty dije tace a barta kada a matsa mata,tasan cewa akwai lokacin da ita anty dijen da kanta zata sanya ayi mata kuma dole ta bada hannunta.
Ana ya jibi daurin aure kwana tayi tana kuka saboda nasihar da mama tayi mata,ta gaya mata duk wanii motsi da zata yi wanda bai dace ba tamkar ta watsawa mahaifinta qasa a ido ne,ga gidan ya fara amsar baqi,haka ta tashi washegari da zazzabi da ciwon kai amma haka ta dinga cijewa tana shiga jama'a,wanda hakan bai amfana mata komai ba face sake qaruwar ciwon kanta.
Bayan sallar isha'i tana kwance cam uwar dakan maman kan abun sallah,hasbunallahu wa ni'imal wakil kawai take ambata babu qaqqautawa saboda yadda taji nugun zuciyarta na daduwa,sallama taji anayi tsakiyar gidansu wadda ta sanyata miqewa dungur gur ta zauna tanq raba idanu kamar wadda aka ritsa da wuqa a maqogaro,muryar abdur rahman ce,sai gabanta yaci gaba da faduwa ta fashe da kuka qasa qasa tana cusa kanta tsakanin cinyarta.
Daga airphort direct gidan ya zarto ko gida bai nufa ba sakamakon mummunan labarin da ya sameshi ta bakin bahijja,kai tsaye aka yi masa iso falon malam wanda shigowarsa gidan kenan,a mutunce suka gaisa saidai kallo daya malam yayi masa yaga sauyi tattare da yanayinsa
"Ina fata lafiya malam abdur rahman" cewar malam din,kai ya girgiza cikin sanyin murya
"Malam,na jima ina neman yarda da amincewar sumayya tun kafin rasuwar yaya mukhtar har kawo yau din nan,na fara samun hadin kanta a kwanakin nan,saidai ta nemi alfarmar na bar maganar har ka kammala aurar da zainab,kwatsam sai jiya na samu labarin wai za'a aurar da sumayya malam haka ne?" Kai ya jinjina kafin yace
"Wannan haka yake abdur rahman,zan aurarwa dan aminina sumayya,sam banyi tunanin kana ci gaba da neman sumayya ba abdur rahman,ban kawo haka a raina ba" sosai ya girgiza da jin amsar malam din,idanunsa suka kada ya dubi malam din
"Malam ni nafi cancanta da sumayya,ka yimin alfarma ka aurar min da ita" cikin tausayawa malam din ke dubanshi
"Kayi haquri abdur rahman,wannan wanda zan baiwa sumayya wa familynsu sunfi qarfin na musu haka,idan da wani ne can daban babu abinda zai hana na maida auren kanka,amma zan gaya maka kadan daga labarin muntari,zan gaya maka kadan daga cikin waye muhtari a gurina" warware masa yayi DANGANTAKAR dake tsakaninsa da baabaa prof,dangantakar kuma da suke fata da burin ba zata sake katsewa ba har ABADAN,wanda hakan suna burin ya zama hanyar ci gaba da yado da qarfafa zumunci da dangantakarsu.
Cikin gamsuwa abdur rahman yakw gyada kai,babu shakka irin wannan dangantaka dake tsakanin malam da muhtari ko shine idan yana da diya abinda zai iya faruwa kenan,ba zaiso ya zama silar datse wannan kakkaurar tsohuwar igiya ba da ka qullata tun duniya na kwance,tun basu gama sanin su waye su ba kawo yau,saidai rabuwa da sumayyan ba abu bane mai sauqi tattare da shi,wani mugun ciwo ne da zai ci gaba da illata shi
"Shikenan malam,ina muku fatan alheri,saidai mu a tayamu da addu'a,Allah ya bamu haqurin jurewa" ya fada cikin karyewar murya
"Allah ya yi maka albarka,ya sanya juriya a zuciyarka,ya musanya maka da wadda ga fita alkhairi a gareka"
"Amin malam,na barka lafiya" ya fada yana mai miqewa,cikin tausayawa malam din ya bishi da kallo,har ya kai qofa ya kirashi ya dawo ya tsugunna kansa a qasa
"Abdur rahman"
"Na'am malam"
"Idan har babu takura kuma ba zaka damu ba,mai zai hana ka nemi halimatu 'yar uwar sumayyan,a tunani kamar zata iya maye maka gurbinta"
"Indai malam kana ganin hakan yayi daidai bazqi haifar da wata matsala ba na karba,ina kwadayim zuriyarka ne malam,na tabbatar akwai alkhairi ga dukkan wani d'aa da ya fito daga gidan nan" murmushi malam din ya saki cikin jin dadi
"Kayi tunani a nutse,kada kayi abinda kasan zaka takura,idan halima tayi maka ka dawo zan baka ita,idan bata yi maka ba babu komai zan biku da kyakkyawar addu'a"
"Ta yaya malam zanqi jininka,halima jininka ce jinin sumayya,na karba malam,kuma in sha Allahu a gobe zan bada sadakina nima kada itama na rasata"murmushi ya subucewa malam,sosai ya sanya musu albarka tare da jan doguwar addu'a ta fatan alkhairi a garesu baki daya,yace yaje sitting room a bude yake zai turo masa haliman,miqewa yayi kansa a qasa yana yiwa malam din godiya,abun mamaki cikin qanqanin lokaci tashin hankalin daya tsinci kamsa kaso dari sai yaji babu hamsin ciki,ya taka ya fice sitting room din gidan yana jiranta.
Malam yana daga falon ya qwalawa haliman kira,gama cire lallenta kenan taji kiran malam din,ta goge hannum nata ta sanya hijabinta ta shiga dakin
"kije sittin ro abdur rahman na jiranki" jin maganar tayi banbarakwai sai ta daga kai ta dubi malam
"Ni ko yaya sumayya dai?" Daquwa ya mata
"Dan gidanku na kasa gane sumayyan sai ke zan kira?,ke nace ba sumayya ba" bata sake cewa komai ba ta miqe ta fito ta nufi sitting room din gabanta na faduwa.
Tsaye yake tsakiyar sitting room din hannayensa goye a bayansa ya zubawa qofar shigowar idanu,tana sallama suka hada ido,karom farko taji wata faduwar gaban da bata taba jin irinta ba don ta kalleshi,idanu ya zuba mata yana amsa sallamar,sai yake hango yanayinta da sumayya muraran,ya taba kula da hakan shekarun baya amma ba kamar yanzu ba,ga mamakinsa murmushi sai ya subucewa lebansa,ya zuba mata ido yana ci gana da kallonta har ta qaraso gabanshi,cikim diriricewa tace
"Ya abdur rahman gani.....malam yace wai.....kana jira na"
"Bismillah zauna" babu musu ta taka ta zauna kan daya daga cikin kujerun,gabanta ya iso a hankali ya zube a gabanta wanda hakan ya sake haddasa mata faduwar gaba da,sai ta jita ta takura sabida basu taba zama gab da gab irin haka na,duk a qasa yake zaune a gabanta amma yana kusa da ita
"Halimatus sa'adiya,malam baice miki komai ba?" Kai ta gyada da sauri sabida ta gaji da yadda gabanta ke faduwa,murmushi ya dan saki,wato shi zai yiwa kansa yaqi kenan ko?,daga idonsa yayi ya zubesu a kanga,sai ta janye nata idanuwan
"Halimah kina sona zaki iya aure na?" Taji tambayar babu zato na tsammani,ido ta zaro tana dubanshi,kasa cewa komai tayi har sai da ya maimaita,bakinta na rawa tace
"Yaya abdur rahman.....yaya sumayya.....ita yaya sumayya fa?" Murmushi ya saki
"Bakya gidan ne?,bakisan malam ya bata wani ba?,ni kuma a yanzu malam ya bani ke zaki iya aure na?" Shiru tayi gabanta na faduwa,yayin da kunya ta kamata ta sadda kai qasa qwalla na taruwa a idonta,hakan taji tsoro ya kamata,malam zai aurar da ita kenan itama,jin shiru ya sanyashi sanya yatsunsa ya daga fuskarta,kallo daya tak yayi mata ya fuskanci