Showing 147001 words to 150000 words out of 364327 words

Chapter 50 - KUNDIN KADDARATA COMPLETE HAUSA NOVEL

HUGUMA   

20 Aug 2024

40127

ba,mutumce mai son jama'a da faran faran,hakan ya sanya take da qawaye sosai,sai a lokacinne sumayyan tasan alfanun qawa da dadinta,musamman idan ka hadu da mai kyakkyawar halayya irin ta zulaiha mai sonka da zuciya diya,da fari sumayyan ta fara tababa kan yadda zatayi shiga ta fita ba irin wadda ta saba ba,zulaihan ita ta karbi kudi wajen anty dije ta rakata ta siyo irin sutturun qasar,wanda zaki sanya basu fidda tsiraicinki ba,wadanda zaka dace da zamani ba kuma tare da ka fidda tsiraicinka ka sabawa al'adarka ba da addininka baki daya,sau tari idan ta shirya zata makaranta laila kan tsokaneta
"Wallahi anty sumy kin canza cikin watanni kadan,bakiga yadda kayan nan ke miki kyau ba,kamar ba sumyn malam ba,maman abdallah" anty dije na tayata
"Kin rigani a fili na rigaki a zuciya,ta koma wata qaramar baturiya,haskenki ne kadai ba qarasa nasu ba,inaga ma kafin mu koma fa kim saje da su,kayan sun amsheki" ita kanta ta sani amma sai ta saki dariya
"Ina wani kyau a kayan banasaren mutum anty,dadinta daya kawai basa fidda tsiraicin mutum" duk da haka bata bar hijabinta ba,don babu sutura mafi daraja a gunta irin hijabin,saidai duk sanda ta sanya kafin ta kai makarantar suna shan kallo ita fa zulaiha,har zulaihan kan ce
"Ke kuwa sumayya ki haqura mana"
"Babu abinda zai rabani da hijabi sai mutuwa,sai randa likkafani ya zama sutura ta ta qarshe" dariya zulaihan keyi
"Nima wasa nake miki".

       Wata baiwar qwaqwalwa Allah ya baiwa sumayyan,cikin wata biyu kacal harshenta ya fara juyewa,su kansu uncle farouq da anty dije mamaki suke,ganin tana ganewan ne ya sanya ya yanke shawarar sanyata wata makarantar dake training wa mata zamantakewar rayuwa,ciki harda nau'in girke girke na kowacce qasa,duk randa zakuyi girkin wata qasa tofa malamar 'yar asalin qasar ce,makarantar akwai tsada don ko ita anty dije ta burgeta,ba don tayi tsada da yawa ba itama taso shiga,amma tunda 'yarta ta samu tace ba komai ta dinga koya mata.

        Watansu biyu da daddare uncle farouq ya kwashesu suka fice suga gari karon farko tun bayan zuwa,don sam bai da lokacin zama a gida,awa biyu kacal sukayi suka dawo saboda yana da aikin da zaiyi,suna gab da shiga gidan ya tuna dawowar qanin abokinsa wanda gidansa ke daura da nasu,sunje ganin gida ne shi da matarsa sai shekaran jiya suka dawo,baki dayansu suka nufi gidan don a gaisa,anty dije ta riga data sansu dama,mai gidan na girmama uncle farouq kasancewarsa abokin yayansa.

       Gidane qarami kamar nasu,ga mamakin sumayya matar gida matashiya ce wadda kusan zasuyi sa'anni da ita,yaronta daya itama wanda ya kusa shekara hudu,nafisa asalin shuwa ce,tana aure da mijinta Dr auwal wanda qarin karatu ya kawoshi qasar,shekararsu biyu kenan,shekara biyu ya rage musu su koma gida,shekararsu hudu da aure,yaransu daya khalid wanda shima shekararsa hudun dai dai da shekarar aurensu,saidai har yanzu bata qara wata haihuwar ba,ita din ma karatu take,yanzu haka ta kusa hada degree dinta a fannin kasuwanci,abinda tafi sha'awa kenan tun tana yarinya,kusan gado tayi,sabida kasuwanci shine sana'ar mahafinta .

        Ba qaramin dadi taji ba da ganin iyalan uncle farouq din,sai ta jita kamar a gida nijeria,nan kusa da su dama babu wani dan nijeria,duk a tsakiyar fararen fata 'yan asalin qasar take,tun kafin su tafi ganin sumayya sa'a take a gunta ta dinga fadin
"Na samu 'yar uwa"
"Lallai kam,wannan,ai sai kinyi da gaske nafisa,bata da son mutane,ga shegen qulafucin zaman gida,makaranta kadai ki fidda ta"
"Zamu saba ai ko sumayya,zaki zama qawata" ta fada tana kallonta,tashin farko taji sumayyan tayi mata,nutsuwarta ta burgeta,murmushi sumayyan tayi
"Insha Allah maman khalid"
"Kamar gaske" cewar anty dije
"Haba umman khalipha kada ki sage mana gwiwa mana" inji nafisan.

        Sumayya kam ta gwada mata halinta,mutum ce mai yawan janye jiki ga baqin mutane,musamman wanda ta fuskanci rayuwa bata ajesu bigire guda ba,bata son sanya kanta inda zai zame mata matsala ko dana sani a gaba,ko kuma inda ya fi qarfinta,qwarya tabi qwarya haka nata ra'ayin yake,wanda ta gada ne daga wajen mahaifanta,mutane masu sanin daraja da qimar kansu,masu wadatar zuci da yakana,bata manta nasihan mama da kullum take gaya musu,kaso duniya mutane su qika,ka qi duniya mutane sai su soka,ka guji kwadayi,don shi din mabudin wahala ne,matuqar ka hau motar kwadayi to la shakka babu inda za'a saukeka sai tashar wulaqanci,mutunci yafi kudi,mutunci abu ne da idan ya zube qasa bai yiwuwa ka kwasheshi,mutunci abu ne da kudi ko wata isa basu iya siyanshi,ire iren wadan nan maganganu ke mata tasiri,takan zama mai tsantseni duk inda ta samu kanta,takan koma dora mutuncinta gaban komai nata.

        Nafisa 'yar gata ce gaba da baya,itace auta a gidansu baya ga maza yayye da take da su guda hudu,ita daya ce diya mace qwal daya tilo da iyayenta suka haifa,hakan ya sanya take ganin gata,baya ga arziqi da Allah ya yiwa mahaifanta,nafisa irin mutanan nan ne masu son jama'a,sakin fuska da jan mutane a jiki,ko kadan ba zata taba yin wani aiki da zai nuna maka ga daga inda ta fito ba,saidai idan kai idanuwanka suka kai ka gani,tunda taga sumayya taji tayi mata,take jin ta samu 'yar uwar data rasa a baya,duk da cewa tana da tarin qawaye amma sai taji sumayyan ta zame mata daban.

        Tun sumayyan na janye jikinta har ta saki jiki,nafisan ita ta soma koya mata cumputer,ta naqalceta sosai,itama halayen nafisan sun burgeta,yadda ta tsammaci halin masu kudi duka guda ne ashe ba haka abun yake ba,taga misali daga kan nafisa da kuma amira,a yanzu haka amiran ko yaushe na kan kiran sumayyan,har tana mamakin bata ganin kudin da take qonewa wajen kiran nata?,kullum nafisan na kan qorafi da mitar yadda sumayya taki sakin jiki da ita bayan ta dauketa 'yar uwa,kan hakan har tasowa sukayi takanas ita da mai gidanta suka zo suka kawowa uncle farouq qarar sumayya wai bata sonsu,wanda tilas hakan ya sanya ta soma sakin jiki da itan,shima mijin nata auwal da yake dan taya bera bari ne ya biye mata,akwai tsantsar qauna shaquwa da fahimtar juna tsakaninsa da matarshi,qauna ce mai yawa da tsafta tsakaninsu,wani lokaci idan sumayyan taje taga yadda ake zuba soyayya kunya kamata take,takan ce bari naje gida,bazan iya wannan badalar taku ba,dariya nafisa ke saki
"Wallahi sister(haka take ce mata)sai kin fini tsula tsiya,bari kiyi auren" kyabe baki sumayya keyi
"Wane aure,ai mu mun bar muku shi,mu da shi sai a qiyama" kalaman da sun jima suna daurewa nafisa kai,ga tsammaninta sumayyan budurwa ce bata taba aure ba,sau tayi yunqurin tambayarta sai kuna taja bakinta ta tsuke,ba kasafai take son yiwa mutum shishshigi cikin lamuransa ba,randa taga sumayyan na waya da abdallah a ranar ta kasa daure tarin tambayoyinta
"Ke wallahi baki isa ba,kullum ki sani a duhu ki gudu,to yau kam sai kin gayan wace ke" nafisan ta fada cikin yin kicin kicin,dariya tayi mata
"Wace kuwa ni din bayan sumayyan da kika sani" sakinta nafisan tayi tayi baya ta zauna
"Shikenan tunda haka kika ce,na fuskanci baki daukeni yadda ni na daukeki ba,inda kin daukeni yadda na daukeki da ba zaki boyen komai dangane da ke ba,tunda dan uwa bai boyewa dan uwansa sirrinsa,naga har shawara nake dake sumayya kuma ina ganin haske cikin dukkanin shawarar da kika bani" shiru tayi ganin yadda fuskan nafisan ta nuna rashin jin dadi qarara,babu shakka dukkan wata qauna ta fisabilillahi nafisan ta nuna mata,bata shayi ko shakkar yin kowacce shawara da ita,ajiyar zuciya ta saki
"Shikenam kiyi haquri mom khalid,yanzu ki bari naje gida na yiwa anty abincin dare kinga bata nan sun fita da uncle,amma na miki alqawarin idan na kammala zan dawo na baki labari na" sake hade rai tayi don ta nuna mata gaskiyan abinda take fada
"Na amince saidai da sharadin idan kinzo nan gidan zaki kwana,tunda kin sani yau dadyn khalid bai gida kwanan makaranta zaiyi" dariya sumayyan ta bushe da ita ganin yadda ta hade rai tana mata muzurai kamar wadda ta hadiyi kunama
"Idan anty ta barni zan kwana"
"Zata ma barki saidai baki so ba" bata qara cewa komai ba ta miqawa khalid hannu dake kallonta,jira dama kawai yake tace su taho,wani shaquwa sukayi sosai da yaron,ganinsa take kamar abdallanta,ta sabi khalid din suka fice nafisa na binsu da kallo,murmushi ta saki tana jin dadi,jin sumayya take kamar ciki daya suka fito,Allah shike hada qauna da soyayya a tsakanin mutane har ma da jinsin dabbobi,haduwar jini wani abu ne na daban daga Allah.

      Tana zaune kan sofar dake dakin baccin nafisan sanye da nata kayan bacci cotton masu kauri riga da wando wadatattu,khalid na saman cinyarta yayi bacci,hannunta na saman sumar kanshi tana shafawa don bai jima da yin baccin ba,lokaci lokaci takan daga kai ta dubi nafisa dake tsaye gaban madubi tana ta faman shafe shafe da goge goge bayan fitowarta daga wanka,mamaki duka ya cikata bacci akewa wannan hidima haka,gaskiya mana ko yaushe fatar nafisan kamar ta dan jariri,duk da fara bace choculet ce,har haqurin sumayyan ya qare ta tanka
"Wai duka wannan wankan naki meye amfaninshi bayab wanda ake mawa baya nan mrs auwal kamar zaki sauya fata?" Murmushu tayi tare da ajiye body mist da ta fesa ta dubi sumayyan
"Au sai noor yana nan sannan zanyi haka,ai ya riga da ya zame min al'ada ta"
"To ai saiki bada himma,nikam na fara jin bacci,ina jin labarin nan bai yiwuwa sai gobe" ta fada tana gyarawa khalid kwanciya saman gado,da sauri ta zura 'yar saman rigar baccin nata ta qaraso inda sumayyan take itama ta haye gadon tana cewa
"Sorry,na kammala,kema dab kike daki fara wannan sanaben ai" baki ta kama
"Niii,rufan asiri,ku din dai sai kuyita yi,haka naga laila ma 'yar qwailarta da ita ta fara daukan course" dariya nafisa tayi
"Wallahi da gaske nake,jiya na hau internet,naga D&G sunyo sabbin mai na gyaran fatar fararen mata,set ne harfa perfume,sure,da subulunshi,na riga ma da na siya miki,jiran isowarsa kawai zamuyi,a yadda suka ce gobe zasu kawo min" shiru tayi tana saurarenta,wannan wace irin qauna nafisan ke mata haka?,daga ganin abu babu wanda ta tuna sai ita din?
"Am ready fa,ke nake jira" ta katsewa sumayyan tunani tana dubanta.

       Gyara zamanta tayi bayan ta jingina jikinta da bango,a hankali ta soma warware mata wace ce ita,babu abinda ta boye mata,sumayya kuka nafisa kuka,babu wanda zai rarrashi wani,bala'in tausayin sumayyan ya kama zuciyar nafisa,yayin da sumayya ta tsokano wani danqararren tabo da dama har yau bai ida warkewa ba,janyo sumayya tayi ta kifa kanta saman cinyar nafisan tana ci gaba da kukan tana bubbuga bayan itama tana tayata ba tare da ta tsaidata ba,cikin zuciyarta taba cike fal da mamakin irin rayuwar da sumayya tayi,bata taba hasashen zata iya yin rayuwa irin wannan ba,shi qunci da matsin rayuwa gami da QADDARA hadi da JARRABAWA kenan babu ruwansu da girma ko qanqantar shekaru?.


Sai da zuciyarta ta samu salama sannan nafisa ta soma magana
"Ashe akwai irin wannan rayuwar a duniya?,rayuwar da mutum mai kimanin shekaru kwatankwacin nawa zaya fuskanceta da tsanani har kamar haka?,na jinjina miki sumayya,Allah ne kadai yasan me ya tanadarwa rayuwarki,irin wannan yarda da qaddara da karbarta hannu bibbiyu bau tashi a banza,Allah ya jiqan mukhtar ya raya mana abdallah,kici gaba da haquri,amma kada ki sake hasashen ba zaki sake yin aure ko jin dadin rayuwarki ba,kin sani kowanne bawa da yadda Allah ya tsara masa zai rayu,dole kowa ya rayu bisa tsari da doron da mahalicci ya QADDARA,kici gaba da addu'a,zan tayaki da yardar mai duka,yayi miki zabin kyakkyawar rayuwa,ya cire dukkan qunci da damuwa da kika taba tsintar zuciyarki a ciki",ta jima tana fidda hawaye masu dumi wadanda suka dinga wanko zafi da radadin dake cikin zuciyarta maganganu ta dinga bata masu kwantar da hankali har ta samu nutsuwa cikin zuciyarta.


Washe gari ta tashi fuskarta ta dan tasa saboda kukan data raba dare jiya tana yi,baki daya nafisa sai ta damu tana ganin kaman laifinta ne,murmushi sumayyan ta dinga tana girgiza kai tana qoqarin nuna mata ba laifinta bane,dole ne ga duk mutumin da yake da miki cikin rayuwarsa ya koka duk sanda wannan ciwon ya motsa.








*mrs muhammad ce*👑

📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
[23/02, 11:51] Beesama Zamani Wrt Grp: ✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖


*~NA~*

*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*

*WATTPAD:HUGUMA*

*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)

6⃣7⃣

*Bismillahir rahmanir rahim*

Allah madaukaki yana cewa


*duk wanda ya sallamawa Allah dukkan lamuransa alhali yana mai kyautatawa haqiqa yayi ruqo da igiya qaqqarfa wanda bata tsinkewa(yankewa/rabewa)*

_____________________________________




        Wuni nafisa tayi ta kasa sukuni da tausayin sumayya,a haka auwal ya dawo ya taddata,baki daya wani qaunarta na sake shigarta,haqiqa bata yi zaben tumun dare na aminiyar qwarai ba.

         Washegari da kanta taje gidan anty dije dauke da ledar mayuka da turarukan data siya matan,dariya sumayyan ta dinga tana kallon tarkacen kayan,ko ba'a fada mata ba tasan cewa sunfi qarfin mai rangwamen gata irinta,saboda zuwa yanzu kanta ya soma budewa,tana iya gane abu mai tsada,balle ta san nafisan sarai,komai nata designer ne,kuma komai nata a set dinsa take amfani da shi
"Wai kina nufin ni kike so na dinga amfani da wannan kayan?"
"Qwarai kuwa da wace?" Kai ta kada tana dariya
"So nake naga kin sauya sis,so nake naga kin fara sabuwar rayuwa" kai taci gaba da kadawa tana dubanta,kafin tace wani abu anty dije ta shigo dakin,kayan ta dinga dauka tana dubawa tana dariya
"Allah yasa a baki hadin kai"
"Idan ma taqi ina kallon fatarta zan gane,don sun tabbatar min suna da kyau,suna gyara fararen mata" itama ta fadi tana dariyan,godiya anty dije ta taya sumayya,sun jima suna hira kafin nafisan ta koma gida don dora abincin dare,don auwal baison take away idan ba lalura ba ta kama.

        Anty dije ke jinjina tsadar kayan
"Bansan ya zata kaya ba idan kayan suka karbeki ba,suna da kyau amma akwai tsada" cewar anty dijen.


Kiran wayar daya shigo wayar sumayya ita ta katse hirar da sukeyi din,fuskar ta washe baki bude take fadin
"Amiran baabaa ce anty"
"Kice ina gaidata" inji anty dije tana miqewa don ficewa daga dakin ta fara jiyo hayaniyar minal da khalipha da alama rigima suke shi da ita
"Autan baabaa(haka take kiranta idan taso tsokanarta)"
"Mutanen uk,wai nikam yaushe zaku dawo,nifa na gaji wlh daga gida sai makaranta,ni daya kamar mayya,idan bakuyi wasa ba fa zaku ganni wlh na biyo sahu" dariya sumayya ta dinga yi ganij dududu watansu nawa ma da tahowa
"Kamar yaune fa zaki ga mun dawo din,yi haquri takwara" dariya sukayi baki daya sannan suka soma taba hira,amiran na bata labarin abubuwan da suka faru bayan tafiyarsu
"Amiran umman khalipha,baabaa fa ya karbi kudin aurena har da sa rana watanni shida masu zuwa dai dai sanda zan kammala degree dina" ta fada cikin nuna farinciki,cikn zumudi sumayyan tace
"Kai haba dai takwara"
"Wallahi amira,amma nikam tsoron yin auren nan nakeji takwara,duk da saifullahi na matuqar sona da qaunata,hakanan na amince da tarbiyya da halayyarsa" gefe daya na zuciyar sumayya itama jimamin da take mata kenan,saidai ba lallai abinda ya samu dan uwanka kaima ya sameka ba,kowa da tashi kalar qaddarar,bare amiran ita ba mai mata zata aura ba,ita daya ce a gunsa
"Meye wani abun tsoro?misali su ummee da sukayi auren su wani abu kika ga ya samesu?" Kai ta kada kamar tana kusa da ita
"Um um,kawai banson rabuwa ne da gida,ina son family na"
"Ba shakka familynki abunda zaka yi marmari da begensu ne idan ka barsu,duk wanda ya kalli yadda kuke son juna ba zaiyi mamakin haka ba" sumayya ta zantawa ranta,amma afili sai ta bagarar da zancan da nuna rashun muhimmancinsa
"Duk mace 'yar wani gidan ce,ko su su ummeen ce miki akayi gidanku ne gidansu,suna nasu familyn fa suka baro ko?" Sai amiran ta qyalqyale da dariya
"Kinji umme tace ah to,ashe taji me kika fadi,kinsan abinda anty maamaa ta gama gayan kenan dazu" itama dariyan tayi,ta shiga tsokanar amiran
"Kawai kice mu fara shirin baki,ina ga ba zamu wuce wata guda da dawowa ba zamu shiga hidima,ummm,bari na gayawa anty dije mu fara taru"
"Ahto,don kune amarori,shi yasa na dage saidai asanya wata shidan,daa qasa da haka za'a saka,nasan kafin sannan kun dawo"ci gaba da tsokanarta sumayya tayi a haka suka rabu cikin barkwanci.


Bayan ta aje wayar ta samu anty dije na sauyawa minal kaya da alamu bata wadancan tayi don ba'a jima da yi mata wanka ba
" nikam saura qiris na sauya qawa,wannan qawa tawa qazamiya ce"sumayya tayu maganar tana duban minal tare da yamutse fuska
"Yadai fi wallahi,duk gidan nan babu mai bata kaya kamar nata"inji anty dije,fuska ta kyabe tana shirin sakin kuka
" na daina anty,wayyo Allah na"ta fada tana bubbuga qafafunta zata hau bori
"To shikenan,ya isa,ai ke qawata ce ta amana,babu mai rabamu,uwata ce fa ta kaina" sai ta soma dariya tana tsallen murna sumayya na dubabta tana murmushi,duk yaron data gani tuna mata yake da abdallahnta,dauke kanta tayi ta maida ga anty dije
"Anty an sanya bikin amira fa,wata shida mai zuwa" sakin maballin da take ballewa minal tayi dama ta kusa gamawa ta juyo tana duban sumayya
"Tabdijan,kice akwai gangami kenan,bikin auta guda?,bikin amira ni 'yasu?" Antyn ta fada cikin jinjina lamarin,kai sumayya ta gyafa tana nade qafafunta saman gado tana murmushi
"Jar uba,kice abuja zata motsa,familyn baabaa prof za'ayi bikin da aka jima ba'ayi kamarsa ba,to ai ina ga da na su mahmoud za'a hada tunda suma wata bakwai ne inaga yayi saura cikin ranar auren da aka sanya musu ko,Allah ya nuna mana,sai mu fara shiri tun yanzu,sumayya kuna da biki" inji anty tana murmushu gami da jinjina kai
"Wallahi anty haka tace,ni kam mai zan iya cikin hidimar,ni da ban taba bikin qawa ba?"
"Aikuwa dole ki ware ayi komai da ke,yadda amira ta daukeki kada kuce zaki watsa mata qasa a ido,nasan halayyarki sarai" dariya sumayya tayi ganin yadda antyn ta camfata tana kwantar da kanta saman filo
"Allah ya bamu iko to anty" kan ta gama rufe bakinta kira ya shigo wayarta,lambar alqasim ne,tana mamaki da har


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login