Showing 114001 words to 117000 words out of 364327 words
takeaway saboda sumayya don ta lura bata ci komai ba ta amsa sannan suka wuce.
Suna shiga motar laila tace
"Lah,wallahi anty sumayya kinga har ya biyo mu ya koma,ta fada tana qyalqyala dariya"
"Waye ya biyo mu" anty dije ta tambaya tana qoqarin maida atm dinta jaka
"Ba kowa" sumayya ta fada da sauri sannan ta juya tana kallon laila,harararta tayi sannan tace
"Bana son surutu komai kika gani kiyi magana kai,idan ba haka ba bazamu shirya ba"
"Sorry anty sumayya" ta fada tana narke fuska don ta cikawa su hafiz baki ita ce ta gaban goshin anty sumayya bata son su gansu a rana
"Shikenan" ta fada tana gyara zamanta,sai da suka sake daukar hanya sosai sannan ta lalubi wayarta da niyyar kiran yaya yahanasu,sai taci karo da misscall din abdur rahman,sai kuma saqon SMS
_garin masoyi baya nisa,ina miki fatan alkhairi_ abinda kawai ya rubuta kenan,bata fahimci zaurencen nasa ba saboda haka ta share ta lalubi lambar yaya yahanasun ta danna kira,ringing biyu ta daga,cikin mutunci suka gaisa sannan aka nemo mata abdallah aka hadata da shi,hira ya dinga mata wani shirme wani abun dariya haka ta dunga dariya,daga bisani su laila suka amshe wayar suka yita shirmensu su da shi sai da suka cinye nata credit dinta tatas sannan suka haqura,bayanta ta maida makarin kujerar ta lumshe idanuwa zuciyarta fes tana jin dadi da jin muryar abdallah da tayi,tabbas d'a ba wasa bane,ababe ne masu wanke zukatan mahaifansu koda da shirme da quruciyarsu kadai,tunanin mukhtar shi ya ratso cikin farincikinta ya gusar da shi cikin yab sakanni qalilan,taje fuskarta ta sauya,damuwa ta lullube zuciyarta,taso abdallah ya rayu da mahaifinsa,yaci gaba da cin gajiyar gata da mahaifinsa ya tanadarwa rayuwarsa saidai ina,tsarin ubangiji shine daidai,tana jin hayaniyar su laila amma tayi fakare kamar mai bacci,bata sake bude idanuwanta ba har suka shiga garin abuja.
Qarfe biyar da rabi suka isa garin,bata mance yadda unguwar tasu take ba saidai an sake samun sauye sauye,sabbin gine gine da kuma sabunta tsoffin.
A falo suka zube baki dayansu wanda basu tashi ba sai da lokacin sallar magariba yayi sannan kowa ya debi kayansa zuwa daki,a dakin laila da minal ta zabi zama,kasancewar gado uku ne a dakin,daki ne madaidaici wanda ke shimfide da tiles da labulaye sai fenti dukkansu kala daya,wardrobe ce irin ta jikin bango wadda ta cinye bango guda,sai madubi a wani bangon daban,daya bangaren kuma gun ajitar takalma ne zuwa su jakankunan makarantarsu,daura da nan kuma qofar bandaki ne,sallah ta sanyasu suka fara yi sannan suka bude kayansu suka koma maidasu muhallinsu,a wanke a goge suke dawo da kayansu kamar yadda suka tafi da su.
Anty dije ce ta turo qofar dakin ta shigo,wannan karon ta sauya kayan jikinta da alamu ma wanka tayi don sai qamshi take zubawa ta dubesu tana zama gefan daya cikin gadajen dakin
"Sannunku da himma,hala ma ko wanka ba wanda yayi a cikinku ko?"
"Ummi sai mun gama gyaran kaya"inji laila
"eh kam bakwajin yunwa ne" anty dije ta sake fada,murmushi sumayya tayi din itakam ba yunwa tattare da ita,miqewa anty dije tayi
"Idan kun gama ga takeaway can da abban laila ya shigo da shi sai ku dauka kuci,nikam ina ga sai da safe zamu sake haduwa da ku"
Minal ce ta miqe da sauri
"Ummi zani gun abba"
"A'ah,ya shiga daki shima a gajiye ya dawo,abba sai da safe ki kwanta ga anty sumayya nan sumayya sai da safe,ayi kwanan baqunta lafiya" dariya duka sukayi sumayya tace
"Allah ya bamu alkhairi anty"
"Amin" ta amsa tana ficewa.
Kamin wani lokaci sun gama kintsa komai,sai da suka ci abincin sannan suka yi wanka kowacce tayi shirin kwanciya,tana saman gadonta lullube da bargo saboda ac da laila ta kunna wayarta ta soma haske sabida ta maidata silent,abdur rahman ne kamar ba zata daga ba saboda bacci take da buqatar yi,amma sai taga hakan bai dace ba,a mutunce ta gaida shi ya shaida mata ya kirata dazun kiran bai shiga,ta sanar masa,mai yiwuwa lokacin suna kan hanya ne ba service,qorafi ya shiga yi mata kan dalilin tafiyarta bata sanar masa yace
"A qalla ko addu'a sumayya na miki ko?,har yau kinqi gayan dalilin da ya sanya baki sona" baki ta bude kamar yana ganinta
"Ni bance ma bana sonka ba abdur rahman,kawai dai ina da buqatar hutu ne cikin rayuwata,har yau zuciyata da qwaqwalwata basu zama fresh ba,kuma ko baya ga haka ma banson na zalunceka,don banajin akwau mahaluqin da zanso kwatankwacin mukhtar,zanfi so na qarashe rayuwata a haka naje na tadda shi a inda yake" shiru ya ratsa wayoyin nasu kafin daga bisani ya sauke ajiyar zuciya
"Wannan ba hujja bace,amma har zuwa yaushe kike ganin qwaqwalwarki zata zama fresh din na daga miki qafa zuwa wannan lokacin?"
"Ban sani ba nima abdur rahman,ban da masaniya" ta fada da alamun ta fara karaya,shuru ya sakeyi,ta tabbata sumayya abar tausayi ce,hakanaj dole ayi mata uziri,amma ya ya iya bazai iya rabuwa da ita ba,tsakanin jiya da yau kawai lissafinsa ya dagule,aikin da ya tafi sokoto domin shi ya gaza aiwatar da komai
"Zan bar miki maganar da baki so har zuwa sanda zaki buqaci haka,saidai ina son don Allah mu maida dangantakar mu ta baya ta wa da qanwa,idan na kiraki ki amsamin kamar dan uwanki kin yarda?"
"Anya hakan ma zai yiwu?"
"Mai zai hana kin manta abdur rahman ne dan zaman dakinki?" Dariya ya sanyata wadda ta taho da hawaye,ya tuna mata wani abu can baya,wani abu da bazai taba goguwa cikin KUNDIN tarihin rayuwarta ba,dadi yaji cikin ransa da ya fuskanci ta sake,bai wani cikata da surutu ba sosai yace ta kwanta tayi bacci zaya kirata gobe yaji yaya kwanan abuja.
*WAI INA ZAINAB NE?*
Tun sanda aka kaita asibitin ta soma gane Allah da girma yake,ga cutar qanjamau dake cin kowane sashi na jikinta,ga qafa wadda ta tasamma rubewa koma ace ta rube,ga hannu daya kullum daurw da ankwa jikin qarfen gado,gwajin farko aka gano cancer ta shiga ciwon saboda haka tilas a yanke qafar kada dayar ma ta harbu,kuka ta dinga yi wiwi da idanuwanta sanda aka nemi kudin da za'a biya ma a samu a yanke qafar aka rasa,ita ta shawarci mamarta da cewa
"Mama,ko kadarorina dake cikin dakina za'a diba a saida a biya tunda ku kun kasa biyamin,bakusan bala'in da nake kwana nake tashi a cikinsa ba" kallon banza maman tayi mata ganin cewa har yanzu bakin zainab din bai gama rusuna ba,duk da halin da take ciki
"Wadanne kadarori kuma kike da su,bayan wadanda kika aiko zinatu ta diba ta saida miki ta kaiwa alqali kudin don ki samu nasara kan shari'arki,da yake Allah ba azzalumin bawa bane gashinan abinda kika aikata yana bibiyarki" ihu ta kwarara wanda ya janyo hankalin jami'an tsaron dake gadinta,wadanda basa rabuwa da ita koda tayi bacci,rantse rantse ta shiga yi kan cewa ba ita ta aiko zinatu ba,maman taje ta nemota duk inda take damfararta tayi,kudin da take sa ran za'a dinga juya mata ana aiko mata da su don tayi rayuwa mai kyau da'yanci cikin kurkuku(kujifa,ita da aka yankewa hukuncin daurin rai da rai amma zuciyar da sauran buri har wata rayuwa mai kyau take hangowa kanta),rirriqeta ta jami'an tsaron sukayi sannan suka sanya likita yazo ya danna mata allurar bacci maman na kallo,a hankali jikinta ya saki har bacci ya dauketa,kuka maman ta sanya bayan 'yan sanda sun aikata waje don basa bari ma a ga zainab din,tausayin 'yar tata kuma sai ya kamata,duk da irin tsiyar da zainab din ta shuka tun tana budurwa kawo yanzu,asirin data yiwa maman ma kusan sai da aka daureta gidan yari ya saketa, ta sani cewa maiyiwuwa zaluncin da itama ta tafka tsakanin kishiyoyi zamanin mijinsu na raye shine alhakin ke bibiyarta Allah ya sauko mata da wannan jarabawar,wato shi sharri kare ne maishi yake ba,hakana sharri dan aike ne,duk inda yaje gun wanda ya aikeshin yake dawowa.
******* ******** *******
Washegari da gyaran gidan suka tashi kasancewar 'yar aikin anty dijen itama ta tafi garinsu,babu tabbacin dawowarta ma don suna tsammani aure za'a yi mata,basu samu kansu ba sai la'sar sannan suka kammala komai,daki sumayya ta shiga tayi wanka sannan ta fito ta shirya cikin riga da zani na atamfa,ta zura hijabinta kenan zata tayar da sallah wayarta ta dauki ruri,mama ce sai ta koma bakin gado suka gaisa,sannan daga bisani ta buqaci ta kaiwa dije zasuyi magana ta kira nata layin a kashe,kiran ta katse sannan tayo falo don ta haura sama ta miqawa anty dijen wayar.
Kyakkyawar budurwa ce tsaye a bakin qofar falon,farace mai matsakaicin tsaho,sanye take da yadin material plain mai santsi da kauri ruwan makuba(maroon)tayi rolling da mayafi ruwan hoda wanda ya sauka iya kafadunta,takalmin qafarta mara tudu(plate)ne shima ruwan hodar,fuskarta fayau babu kwalliya sai kwalli kawai,kallo daya zaka yi mata kasan cewa akwai hutu kwainane da boko zalla a gun,a qalla zasuyi sa'anni da sumayya,minal na tsaye gabanta tana ta tsalle,yayin da budurwar ke qoqarin budewa minal choculet data shigo mata da ita,daga kai tayi suka hada ido da sumayya,sai ta maida kanta ga minal,hakan ya sanya sumayyan itama dauke kanta don bata santa ba ta nufi matattakalar benen don ta haura sama,sai muryar anty dije dake saukowa ta dakatar da ita
"A'ah amira ya kike tsaye,samu gu ki zauna mana"
"Ba komai umman khalipha,sauri nake zamu fita ne da anty su'ad,sai malam alqasim yace min yaga dawowarku na shigo inga mutuniya ta" dariya anty dijen tayi tana qarasa saukowa
"Mutuniyarki kam ai gata nan,yasu maamaa"
"Maamaa lafiya tace in gaidaki"
"Ina amsawa,kice su'ad anzo kenan" dan murmushi tayi
"Eh wlh,bari na wuce umman khalipha"
"Af tsaya mana na baki saqo wajen maamaa"
"Umman khalipha sauri nake,amma may be idan mun dawo da wuri zan biyo na karba mata,banso ma akai su'ad na nan" ta fada a shagwabe kamar wata qaramar yarinya,dariya anty dije tayi don tasan dawar garin
"To shikenan,sai kun dawo"
"Tom" ta fada tana jan kumatun minal tana mata bye bye bayan ta dan sake duban sumayya dake danna wayar ta tana laluben mama don ta kira ma anty dije ita sannan ta miqa mata wayar,karba anty dije tayi tana fadin
"Kun gaisa ne da amira" kai kawai ta kada
"Kai amma dai baki kyauta ba,da na ganku tare ai na zaci kun gaisa sumayya"
"Bansanta ba anty,kuma ko da na fito bata min magana ba,hasalima dauke kanta tayi"
"Qaniyarki,ba gidanku tazo ba" dariya tayi cikin tsokana tana rufe baki
"Af,na manta gidanmu fa tazo afuwa umman khalipha" itama ta fada,sai ta baiwa anty dijen dariya,saboda kusan da wuya kaga sumayyan na zolaya ba al'adarta bace sai lokaci zuwa lokaci,daki ta juya ta shige tana fadin
"Idan kin gama anty ki bawa laila don Allah ta samun chargy"
"To" anty dijen ta amsa tana amsa kiran wayar.
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
5⃣6⃣
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
*Wa wassainal insaana bi walidaini ihsaanaa*
*mun yiwa mutum dan adam wasiyya/umarni da kyautatawa iyaye(uwa/uba)kyautayawa(matuqar kyautatawa)*
________________________________
Tana idar da sallar minal ta shigo dakin da gudu
"Anty kizo ana kiranki a waya"
"Waye yake kirana?" Bata amsa mata ba yarinyar sai jan hannunta da ta soma tana nuna qofa da yatsarta,murmushi tayi don tasan halin minal din,sai kawai ta miqe ta bita,tayi tsammanin wayarta dake gun anty dije ake kira,saidai bata tsaya ko ina ba sai kitchen,ta dangana da ita zuwa bakin wayar su ta landline
"A nan ake kiranki" cikin mamaki tace
"A nan kuma,ba wayarku bace ta gida,saidai ko anty ake kira ko?"
"A'ah sumayya suka ce" inji anty dije dake shigowa kitchen din,cikin shakka da ko kwanto ta daga bayan wayar ta sake sakin qararrawa.
Nemam wajen zama ta soma yi jin muryar namiji,gabanta ya yanke ya fadi tsoro ya kamata,ta tsani abinda zai hadata da namiji,ta amsa gaisuwar da ake mata sannan mamallakin muryar ya soma magana
"Nasan baki sanni ba duk da kin taba ganina sau daya,amma nasam zaki iya tunani,shekaran jiya na ganku a wani restaurant dake kaduna ke da qannenki da yayarki,so naso na tare ki na miki magana sai kuma kunyar idon mamanki ya hana,na lura akwai sanayya tsakaninku da masu wajen,gurinsu na amshi lambarku ta gida"
"To sai kuma akayi yaya?" Ta fada gabanta na faduwa tana neman wajen zama saboda sanyi da jikinta yayi,tana mai fatan alaqar ta yanke daga nan,murmushi yayi wanda har sai data jiyo
"Haba yi a hankali mana beauty,ni da nake so mai qulla dangantaka da alaqa mai kyau?"
"Me kake nufi?" Ta tambayeshi gabanta na faduwa
"Kin gane,tun ranar da na dora idanuwana a kanki Allah ya dora min qaunarki,duk duniya naji babu wata diya mace da zuciyata ke so da qauna sai ke,hakan ya sanya na kasa haquri da ke,ina kuma fatan zaki karbi maganar da hannu bibbiyu"
"Hmmmm,Allah sarki" tayi qarfin halin fada tare da kife kan wayar ta miqe ta fice daga kitchen din,baki daya jin zuciyarta tayi ta quntata,itakam duk yadda take qoqarin killace kanta bata tsira ba?.
Kusan ragowar ranar baki daya a daki tayi ta,dadin abun ma suna tare da su laila,kwanakin qarshen mako ce,sai jibi litin zasu koma.
******* ******* *******
Washe gari tana zaune falo ita da hafiz da minal suna kallo,hafiz kuma na goge musu uniform dinsu,da yake da kansu suke wankinsu saboda suna da inji wanki(washing machine),sumayya ke girkin dare suna ta murna yau zasu ci tuwo saboda haka hankalinta ta rabashi gida biyu,anty dije ce ta sauko daga sama laila na binta a baya hannunta riqe da turamen atamfofi guda biyar,har suka qaraso falon laila na wa anty dujin rakin kayan sun mata nauyi
"To hafiz guga yake muku da ya rakaki,khalipha kuma nasan idan ya bikin ba dawowa zaiyi da wuri ba,kuma aiki ne da shi zaiyi gyaran jakankunan makaranta,idan kinje bakin get baba haruna ya karba miki ku qarasa ciki"
"To" lailan ta fada tana nishi ta fice,dariya sumayya ta dinga yi mata tana tsokanarta wai taji kunya.
Minti kusan ashirin shiru laila bata dawo ba har sumayyan ta kammala abincin dare,anty dije dake shirin shiga wanka ta sauko qasa tana duban sumayya
"Kinji lailan itama shiru kamar an aiki bawa garinsu?"
"Ko a tura khalipha ya ganota tunda har yanzu hafiz bai gama gugar ba?"
"A'ah,ai duk kanwar ja ce,sanya mayafinki don Allah ya rakaki ki gano min ita" fuska ta yamutsa
"Banson fita anty wlh"hararata tayi
"ke kam ko gajiya da zama a gida bakiyi,tun jiya da kika shigo ko waje baki leqa ba,to ba wani gu bane gidan Baabaa prof ne,gashinan yana kallon gidan nan" dan jim ta sake yi,haka kawai bata son shiga gidan,don tun daga qofar get din zaka ga banbamci qarara da sauran gidajen da ke dukka layin da kewayen unguwan,ba yadda ta iya ta shiga daki ta fiddo dogon hijabinta ta dora saman riga da skert na atamfa dake jikinta ta zura silifa ta fito khalipha ya biyo bayanta.
Khalipha na gaba tana biye da shi har bakin tamqamemen get din gidan,qwanqwasawa ya shiga yi a hankali,daga ciki taji ance cikin wata dattijuwar murya
"Kai,waye a nan"
"Khalipha ne"
"A'ah,khalipha khalipha 'yan kano" taji ana fadi kafin taji motsin bude qofar,dattijo ne wanda a qalla zaiyi shekaru sittin tsaye a gabansu hannunsa riqe da buta yana murmushi
"Ina wuni baba halliru"
"Lafiya qalau khalipopi,dazu naga laila ta wuce ai tana tafiya da qyar da kaya a hannu,sai haruna ne ya qarasa mata da su" baban ya fada yana basu hanya su wuce,russunawa rayi cikin girmamawa kamar yadda halayyarta take ta gaidashi amsawa yayi cikin fara'a,khalipha uban 'yan surutu yayi caraf yace
"Yayarmu ce baba daga kano muka taho da ita"
"Sannu da zuwa" baban yace ta amsa da yauwa sannan ta ja khalipha suka wuce ciki.
A darare taki bin bayan khaliphan wanda yayi gaba abinsa da alamun sabo da gidan a tattare da shi,girma da kyawun gida ya ratsata tare da bata mamaki,zata iya cewa kaf rayuwarta bata taba ganin gida kwatankwacinsa ba,ko ina ka kalla qasan gidan a shimfide yake da grass carfet,babban gida ne wanda aka tsara gininsa,sannan aka baje fasaha aka fidda sassa sassa a gidan a zamanance masu kyau da kama da juna,gidan na dauke da sassa biyu manya,kowanne sashe akwai sasanni a cikinsa guda uku masu yalwa da tsari kuma kowanne ma dauke da bene,babban sashin dake hannun dama sashi ne na mai gidan da matansa guda biyu,daya sashen kuma sashe ne da tun usuli yake mallakar yaransa maza su uku tun zamanin samartakarsu har ya zuwa yanzu da dukkansu sukayi aure mallakarsu ne suna amfani da shi lokaci zuwa lokaci,kallo daya zaka yiwa gidan ya burgeka saboda tsarinsa da yanayinsa,komai luf luf a tsaftace a killace,kama daga wajen hutawa dake gefe guda,gun ajiyar motoci wajej wasannin motsa jiki da lambun dake daga bayan gidan.
Sashen dake hannun dama khalipha ya dosa,ganin sun tunkari wata qofa ya sanya sumayya riqeshi
"Kai,wai ina zamu?" Dariya yayi
"Kiran anty laila mana"
"A wanne guri?"
"Gun ummee ko gun anty maamaa" sakinsa tayi tana kokwanto kafin daga bisani ta bishi.
Shi ya tura qofar falon da sallama kafin itama tayi tata,saka kanta kawai ya sanar mata akwai sauyin yanayi sosai tattare da gun,falo ne na alfarma wanda ya ginu ya kuma tsaru abun burgewa da sha'awa ga idanuwa,tsit falon yake babu kowa sai tafkekiyar t.v plasma dake barazanar mamaye bango dake manne tana aikinta a tashar sunna t.v,carfet ne mamaye da falon duk girmansa a maimakon tiles,labulaye da kujeru na alfarma kalar carfet din mai azabar taushi,flower vase ce masu kyau qirar qasar chaina a sakaye a kowacce kusurwa ta falon,sai tarin kayan turaren wuta da humra dake ajjiye cikin tsari gu guda,da qananun centre table dake tsakanin kujeru don ajjiyewa baqo abin sha,ba wani tarkacen qyale qyale bane a falon amma ya