Showing 282001 words to 285000 words out of 364327 words

Chapter 95 - KUNDIN KADDARATA COMPLETE HAUSA NOVEL

HUGUMA   

20 Aug 2024

40044

ta dubu su'ad
"Ina zaton ke din farin shiga ce kan tuggun kishiya ko?,to mu ba yau muka fara gani ba,zagi kuwa ban tashi naga ana yi ba,don nasan makomar wanda ya zagi iyayen wani,shawara kuwa da kike ambata ai ciwo ce,baya ga haka ma kina iya riqe abarki wataqila nan gaba zata miki amfani" daga haka ta juya kan qafafunta ta soma takawa da niyyar barin kitchen din,zage zage su'ad din ta soma yi,tana son yayuaba baqa kamar yadda aka gaya mata saidai babu cikakkar hausa,hakan ya sanya ta dinga hadin gambiza da turanci
"Idan baki wasa ba nice ajalinki" shine kalmar qarshe data shiga kunnen sumayya yayin da take niyyar fita,hakan ya sanya ta waiwayo tana sake jifanta da murmushi
"Idan numfashina a hannunki yake yau kada na kwana a duniya" ta juya ta fice abinta,sam ko a jikinta,tasan sarai zata fuskanci sama da haka ma daga wajenta,saidai ba yau farau ba balle zuciyarta ta quntaya,meye ba'a yi mata ba?,har farautar rayuwar tata anyi.


Toilet ta fada ta sake wanka,sannan ta shirya cikin atamfa plain zani da fitted riga,ta fuskancu shigar na yawan qawatar da almustapha,yakan yawaita binta da kallo duk sanda ta yita,tana tsaka da shafa mai bayan ta sanya kayan ta jiyo sallama,hakan ne ya sanyata fitowa daga dakinta ta ratsa ta corridor dinta ta fito falon,abida ce matar hamza,cikin farinciki ta tarbeta ta jata sukayi dakinta
"Wai wannan wawuyar ta dawo ne na sameta tana zirga zirga tsakanin falo da dakinta ta kasa zama" abidan ta fada sanda take shirin zama saman doguwar kujerar dake dakin,sumayyan na saman dressing chair tana kwalliya,baki sumayyan ta tabe kana ta saki murmushi
"Gata kuwa kin ganta"
"To Allah ya kyauta,sai ki sake zage damtse ki rungumi mijinki" dariya ma ta baiwa sumayyan har sai data dara,daga nan suka shiga hirarsu,tana gaya mata ai ta dan jima ma wajensu ummee,hamzan ne ya sauketa ya wuce wajen daurin aure su da lamin,ta nan zasu dawo idan an kammala daura auren.


Bata fi minti talatin ba ta jiyo sallamarshi cikin muryarshi mai cike da izza da kwarjini,kamar wadda aka yiwa allura ta miqe,dariya abida ta saki sumayyan ta kalleta cikin dan jin nauyi don ta tabbatar qila yadda taga tayi saurin miqewan take wa dariya
"Mene ne" kai ta kada
"A'ah babu komai jeki abinki ina nan ina jira" ta fada tana miqewa saman kujerar,feshe jikinta ta sake yi da turare sannan ta fice.


A hankali ta tura qofan dakin baccinsa dake sama cikin nutsuwa,idanunshi cikin nata bayan muryar su'ad da ta soma dukan dodon kunnenta,shike fuskantar qofa su'ad ta juya baya,magana take cikin bacin rai harda qwallarta a idanu,yayin da ya zuba hannunshi cikin aljihun wandon shaddarsa yana dubanta,tuni ya cire babbar rigar sai 'yar sama da dogon wando,baya ta koma a hankali da niyyar komawa tunda ta fuskanci wata magana suke wadda wala'alla abune da su'ad din bazata so taji ba,a hankali ya motsa baki har yau bai daina kallonta ba,ta masa kyau matuqa,komai nata mai nutsuwa ne da shiga cikin zuciya cikin wani irin sanyi
"Zo nan" ya kirata yana ci gaba da kafeta da idanu,maganan da yayi ya sanya su'ad yin shiru daga rattabo maganar da take yi,ta waiwaya a hankali idanunta kan sumayyan,bawinciki ya sake ninka mata fiye da na dazu,har wani canjin kwalliya take,ita har a nuna mata ado,gabanshi ta qaraso,kafin tace wani abu ya bata umarni
"Rage kayan jikina ki hadakin ruwa,ina sin yin wanka" idanu ta dan fiddo,ta yaya hakan zai kasance ga su'ad wajen na tsaye,yadda ya kafeta da idanu tasan zata jama kanta wani abunne hakan ya sanya ta nufeshi ta soma balle masa botiran gaban rigarshi cikin taushi da sanyi,idanunsa ya dauke daga kan sumayyan ya mayar kan su'ad
"Uhmmmm,ci gaba ina jinki,na taho da jama'a na jira na" kai ta kada tana yunqurin danne hawayenta don kada sumayya ta ganta bare ta rainata,ta sani sarai tunda har ranshi ya baci sai ya horata,koda zata ciyo kansa to sai ya hukuntata,wanda bai iya hukunci ta dadin rai ba,idan ya maka sai kaji babu dadi
"Ka barshi kawai,idan ka dawo mayi maganar"
"Ke kika tada maganan yanzu kk?,bayan na gaya miki cewa ki barta sai na nutsu,ki qarasa kawai idan ba gaka ba daga wannan muhallin banson na sake jin komai daga gareki,idan na dawo zan ganku ne kawai baki daya ina fata kin fahimta" ita kanta tasan indai har zaman lafiya take so da mustaphan to ta bar maganan,ta yarda ya gabatar da su wa juna,idan yaso ta ruwan sanyi zata dafa yarinyar,zata ga barikanvi,zata ganar da ita rainin america ba irin na nijeria bane,zata nuna mata akwai banbanci,za kuma ta nuna mata almustapha nata ne iya daya da ita kadai ya dace.

Busy busy,need ur prayers,we shall meet tomorrow in sha Allah.




*mrs muhammad ce*👑

📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
[23/02, 11:52] Beesama Zamani Wrt Grp: ✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖


*~NA~*

*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*

*WATTPAD:HUGUMA*

*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)



9⃣0⃣


*Bismillahir rahmanir rahim*

*YA UBANGIJI KADA KA JARRABEMU DA AZZALUMAN SHUGABANNI SABIDA ZUNUBANMU KAJI QANMU,YA ALLAH DUK MAI NEMAMMU KO NUFINMU DA SHARRI ALLAH KA MAIDA MASA DUK ABINDA YA YI TANADI A KAN KANSA YA KOMA MASA*
____________________________________




       Kai kawai ta kada ta juya ta fice daga dakin,bata so tayi wani abu da zai sanya almustapha yayi misbehaving dinta gaban sumayyar,don ta riga data sani ta bata masa rai qwarai,ta kaishi bango,hakanan fushinsa bai da kyau ko kadan,idanunsa ya dauke daga kanta bayan ta fice ya dubi sumayyan sanda ta gama,daga boxer sai singlet,da idanu ya nuna mata singlet din,a kunyace ta cire mishi,ya sake nuna mata boxer din,sai ta kauda kai tana turo baki,itakam ba zata iya ba,shi ko nauyin su'ad baiji ba zai wani ce ra cire masa kaya,zata juya kenan ya janyota jikinta,ya matseta cikin jikinshi yana goga fatar jikinsa jikin tata,tsigar jikinta ta zuba saboda yawan gargasar dake jikinsa
"Ina zaki baki gama ba?"
"Na gama mana,na bar baquwa ne a qasa"
"Idan ina nan kisa a ranki babu wani a gidan nan sai ni da ke,abidan ce baquwa?,ki tambayeta haka takewa hamza?" Shuru tayi murmushu na qwace mata,sakinta yayi ya nufi bandaki yana cewa
"Kayan nan akwai zafi,but akwai dadi da kyau kayan al'ada" kanta ta maida inda ya yasar da babbar rigar,kana kallonta kasan bata jima jikinsa ba,hakan yake ko a can din ma cireta yayi ya riqe a hannunshi,gefan gadon ta koma ta zauna,wayarshi ta soma ruri,musaddiq ke kira,ganin haka ya sanya ta daga ta shaida musu wanka yake
"Au shine ya zube mu a wannan da yake shine agwagwa sarkin wanka?,tell him muna jiranshi" murmushi kawai tayi ta datse kiran,abotarsu na burgeta,kawai sun dauki kansu daya ne baku daya su shidan,qaraso yayi ya miqa mata hannu sai ta dora wayan saman tafin hannunsa,ya fara shafawa yana tambayarta waye ta sanar masa,sai ya dan tsuke fuska
"Why you permit him yaji muryanki?"
"Afuwan" ta fada a sanyaye,sai ya dan saki fuska yana ajjiye wayar tare da takowa inda take zaune,gab da ita ya zauna har suna gugan juna
"Ina da kishi,matsanancin kishim da bansan ina da shi ba sai da muka kasance tare,please ki kiyaye"
"In sha Allah", mai ta dauko ta soma shafa masa bayan ta gama tsane masa jiki,duk inda ta zagaya ko ta gifta qamshinta na bibiye da ita tare da cika masa hanci,cikin wani cotton yadi fari qal mai adon ash ya shirya,ba qaramin kyau kayan suka masa ba,sai ta dinga satar kallonshi ba tare data sani ba,shigar na qawatar da ita,jikin bango ya rutsata tsaye,tana shirin yin qasa da kanta ya riqe fuskan
"gulma.....kema kin iya,me yasa ba zaki bude baki ki magana ba?" Murmushi ta saki,sai ta saka idanunta sosai cikin nashi ta juyasu tamkar mai yin faari,hakan ya rudashi,ya sanya tattausan lebbansa ya sumbaci idanun nata,qarar wayarshi ta katse masa abinda yake shirin yi,ummee ke kira,ta sanar masa baba na son ganin sumayya a falonshi,ya sauke wayar yana dubanta
"Baba ne ke kiranki,but bana so ki fita,a cike wajen yake,muje na rakaki"
"To" ta amsa ta juya da niyyar ficewa,har ta sanya qafarta waje yace
"Hey" juyowa tayi tana dubanshi,da hannu yake kwatanta mata
"Ina hijabinkin nan babba wanda ya sauko qasa?"kai ta gyada
" yauwa,shi zaki sanya"
"To" ta amsa tana ficewa,wayarshi ya ciro ya kira su lamin ya shaida musu yana zuwa zaije wajen baba ne ya dawo,a dakin ta tadda abida har ta soma gyangyadi abinta,tace tana zuwa
"Babu komai,gama uzurinki,ni wannan kwanciyar ta fimin komai dadi" murmushi tayi ta fice tana tausayin abidan,tayi nauyi qwarai,duka duka watanni kadan suka rage mata ta haihu,ba lallai ma tabi hamza a gida taje tunanin zama har sai ta haihu din.

       Tana gaba yana biye da ita kamar wani body guard,hakan ma yayi masa,tunda ko banza yana morewa kallonta,kasa control din kanta tayi sa'ar da taga malam da abdallah,da gudu yaron ya nufota ta duqa ta tarbeshi ya fada jikinta ta rungumeshi
"Ammi......ashe nan kika dawo kin bar gidan umman khalipha.....laaaaaa,daddy?" Ya katse maganar tasa ya dora da wannan sanda suka hada idanu da almustapha wanda ke tsaye hannayenshi harde a qirji,sosai abun ya masa,sai ya tuna sanda ya ganta da hijab cikin ranakun bikin amira,ta bude hannunta kamar haka yaran suka shige,kwadayin samun yaranshi ya taso masa ya kuma sake nunkuwa fiye da da,don a wannan lokacin haka kawai yaji yafison yara fiye da baya,yana jin dama ace abdallan nasa ne,yaron ya shiga zuciyarshi,amma tana nufin itace mamarshi?,Allah ne ya kiyaye bai kai mata bugu ba randa ta bugeshi kenan,sam bai sani ba,barin jikin sumayya yayi ya nufo almustapha,cak ya dagashi sama murmushi na subucewa daga fuskanshi,sama ya dinga juyashi abdallahn na dariya,yana son ayi masa hakan dalilin da yasa ya kasa manta almustapha kenan,dauke kanta tayi wani farinciki na ratsata ta isa gabansu baba ta duqa,cikin qauna ladabi da girmamawa take gaidasu,cikin kukawa baki daya suke amsawa kafin baba ya dora
"Haduwa tayi wuya mamana,tunda kuka dawo ban ganku ba" kai ta sadda qasa tan murmushi
"Ummee tace kaje jigawa ai sanda muka iso"
"Gaskiya ne kam,ina fatan komai lafiya?,ko da yake alamu sun nuna hakan,saidai muci gaba da binku da addu'a" murmushi taci gaba da yi ba tare data tanka ba,dai dai sanda almustapha ya qaraso ya durqusa gabansun kamar yadda sumayya tayi ya soma gaidasu suna amsawa,ta dan saci kallonshi sanda yake tambayar mama da yaya abubakar,baba ne yace a basu waje da sauri malam yace
"Haba muhtari,waye baqo cikinku,me zan gaya mata me zata gayan,ka daina min haka" dariya baba ya saki ya koma ya zauna,hira suka taba sama sama duk da sumayya ta kasa sakewa,daga bisani ta dauke abdallah ta basu waje,malam din ba sai ta kawo masa komai ba,idan ta aikata hakan ma kamar tayi rashin kunya kenan,don ita kanta ba zata iya qayyade yawan abincin dake gabanshi ba.

        Suna tafe abdallah na kafadarta duk nauyinsa,tana tambayarsa yana rattabo mata labarai kala kala
"Ummu abdallah" taji an ambata daga bayanta,almustapha ne,cikin kunya ta sauke abdallah,ya qaraso ya karbi hannunshi
"Don me zaki fito ki barni ni kadai,wuce sashenki" ya fada yana gyarawa abdallah hannun rigarshi,ba musu ta wuce ta barsu a nan.

        Wajen ummee ya wuce,kasancewar duka yau bai shiga ya gaidata ba,tana cikin baqi ta miqe ta bishi saman,ta samu daya daga cikin kujerun ya zauna,abinda ya burgesu yadda abdallan ya duqa har qasa ya gaida ummen,ji take da ana qwacen d'aa da ta qwace abdallah ta baiwa almustapha,saidai babu komai duka tushiya daya ce,tana fatan wadda ta samar da wannan ta samawa nata dan itama,cikin kulawa da juna suka gaisa sannan yace
"Su'ad fa ta shigo kun gaisa?"
"A'ah,amma wataqila ka ganta,ai ba tafiya zata yi ba yau din,ko zuwa gobe ma duka daya ne zamu gaisa" take ranshi ya baci har fuskarshi ta nuna hakan,dama ya zargi haka saboda baiji baba ya masa maganarta ba,duk yadda akayi shima baisan da zuwanta ba,ko zai lamunci komai amma banda bangaren iyayenshi,sun fiye masa kowa da komai a rayuwarshi,yana da azamar miqewa ta dakatar da shi
"Bance kaje kuyi bacin rai ba har hakan ya kai kunnen babanka gida cike da jama'a" ajiyar zuciya ya sauje,tafi kowa saurin karantarsa abinda yayi niyya kenan yaje ya sameta,ya dan jima wajen ummeen suna tattauna lamuranda suka jima basuyi hira akai ba kafin ya fita daga bangaren.

        Wajensu hamza ya koma,ya taddasu har sun gama ciye ciyensu,wanda duka sumayyan ce ta sa aka kai musu,ba qaramin faranta masa hakan yayi ba,a da aikin ummee ne,ga hidimar baqinta ga na abokanshi,wannan karon kam kafin ummeen ma ta farga har tasa an gama musu komai,musaddqi ke cewa
"Munci mun qoshi,saura a turo mana amarya mu gaisa" wani shegen kallo ya watsa masa,suka tuntsire da dariya baki daua,hamza kam murmushi kawai ya saki yana qarewa almustapha kallo,kusan yafi kowa cikinsu farinciki da samu sauyawar rayuwar abokin nasu,ko makaho ne kai kana kallonshi kasan cewa akwai sauye sauye masu girma tattare da shi.

         Sai yamma sannan malam yayi shirin komawa kasancewar a jirgi yazo a nan kuma zai koma,ba yadda baba baiyi da shi ya bari sai gobe ba amma yawi,yace zasu zo zuwa na musamman,lokacin sumayya na raka abida da nafisa wadanda suma zasu koma
"Amma malam da zaku bar mana shi ya kwana biyu wajenmu?" Murmushi malam ya saki yace
"Gaku nan gashi" ai kuwa yana jin abinda aka fada ya noqe kafada yana narke fuska,dariya malam ya saki shida baba
"Shifa kamar wanda aka haifa tare da gidansu,baison matsawa nan da can,ki baya ga haka ma abdur rahman na tabbata sai ya biyo sahu idan ba'a koma da shi ba,don yana dari dari ya bafa shi gani yake kaman bazai dawo ba" sumayyan tana ji tana gani cike da kewa abdallah ya tafi,taso qwarai ya zauna wajeta yayi wasu kwanaki,tana tsaye tana duban motar data daukesu zata kaisu airphort harda baba,sai da suka fice sannan ta saki ajiyar zuciya,ta baya taji an rungumota,ta dan firgita kadan,sam ta mance hana tsaye gefanta,tun daga sanda yarom ya tafi yaga sauyin yanayin fuskarta,habarshi a saman kafadarta ya rada mata
"Ba ke ba,nima ina buqatan yara,zakiyi himma ki bamu namu da wuri my wife?"tilas murmushi ya kubce mata,kunya ta kuma kamata,ta soma yunqurin raba jikinsu saboda idanun mutane,duk da wajen ba gun wucewar jama'a bane sosai,amma tana iya hango eesha na tahowa da alama hanya ce ta biyo da ita ta wajen,shima sarai ya ganta,ya kuma gane abinda yasa sumayya keson qwacewa,sai ya ma sake hade fuska ya kuma janyota cikin jikin nasa sosai
"baki amsa min ba my life"
"Am ready" da sauri ya juyo da ita suna fuskantar juna
"Really?"kai ta gyada a kunyace,sai ya soma juyi da ita wajen,cikin kunnenta ya rada mata
"ki zama cikin shiri yau"sai ta sinne kanta,ya soma manna mata kisses wanda hakan yaso tsaida bugun zuciyar eesha,qara sauri tayi ta bar wajen zuciyarta na bugawa,tsaki ya ja sanda ta gama wucewan
"stupid....ki kula da yarinyar can,banson wata hulda tsakaninku" inda ta wuce din sumayya tabi da kallo sai ta maida kallonta wajensa,gira ya daga mata kafin ya raba jikinsu,cikinsa ya soma shafawa da hannunshi yana yamutse fuska
"Yunwa" ya furta a hankali,sanoda tun safe rabinshi da abinci,idanu ta zari waje,shaf ta manta
"Am really sorry don Allah,Allah na yi maka abinci tun dazun na zaci kaci na bikin ne" ta fada cikin kwabe fuska,yana son salon maganar nan tata,sai ya sake mata murmushi ba tare da ya shirya ba
"Ban haqura ba" ya fada yan akwaikwayon salon maganar tata,dariya ya bata har sai da farareb haqoranta suka fito,idanu ya zuba nata yana kallon yanayin dariyar tata cikin ban sha'awa da burgewa,sai data gama tsaf sannan yace
"Zan turo a dauka min abincin" ya furta yana takawa kan qafafunshi ya matso dab da ita
"Wuce ciki tukunna" juyawa tayi sai da yaga ta wuce ciki sannan shima ya wuce

       Qarfe biyar da rabi na yammaci aka soma shirin zuwa dauko amare,dai dai lokacin ya shigo cikin gidan,kwance ya sameta saman gadonshi,idanunta baki daya sun tasa sunyi jajur da su,kanshi ya dauke daga bangarenta,su'ad ta cancanci dukkan wani hukunci daga wajenshi,abubuwan bacin ran data yi masa ba zasu qirgu ba,bai mata yadda baba ya bata lokaci yana musu nasiha ba,da kuma yadda shima yayanka mata warning amma hakan duka bai hanata tsallakewa tayi tafiyarta ba,bugu da qari kuma saboda ta raina mishi iyaye ta dawo cikin gidansu amma babu wanda ya isa ta nemeshi?.ta lura idan batayi da gaske ba wankin hula zai kaiya dare,don wasu takaddu ya diba ya juya yana da nufin sake ficewa,da gudun tsiya ta cimmasa,ta rungumoshi ta baya tana sakin kuka,cikin turanci tace
"Kayi haquri ka yafemin,nasan na bata maka na maka abubuwa marasa dadi,amma duka kai ka janyo da aka hada baki da kai aka dauko mana wata cikin rayuwarmu" dan janyeta yayi daga jikinsa ya waiwayo yana dubanta cikin bacin rai
"Har yau baki hankali ba,duk sanda kika fahimci kinyi kuskure mayi maganar da zamuyi" ya sake juyawa da nufin ficewa,maqalqaleshi tayi bakj daya wanda hakan ya tilasta masa tsayawa,cikin kisaa ta dinga fidda kuka tana bashi haquri,bata da wata mafita data zarve hakan,tasan bazai taba iya shallakewa kukanta ba,kasancewarsa mai yawan tausayi da rashin son kuka,a hankali ya janyeta zuwa gadon suka zube baki daya,hannunshi ya sanya ya goge mata hawayen,har yanzu tana maqalqale a jikinsa,sai da gama goge matan kafin ya dora
"Tun ba yau ba na baki damarki tafi a qirga kan ki gyara,idan baki gyara ba duk abinda ya biyo baya kada kiyi kuka da ni,duk da hakan kika sanya qafa kika shure maganata,mutum nawa kika tadda a nan gidan?,su me ya cisu da suka zauna tare?,me ya gutsiresu gayamin?" Ya fadabyana zuba mata idanu,wani abu ya takoreta,haushin su ummee ya sake kamata,ta tabbatar yana mata kwatance ne da su,tilas ta bude baki a cunkushe tace
"Ba komai"
"So ki iya bakinki ki kyautata kalamanki,kada ki manta wandanda suka sanya baki kan auren su su waye a wajena,iyaye na ne wadanda ba wani abu da matsayinsa yayi dai dai da su ko mene ne shi a duniya" shiru tayi haushi na cikata,tsanar


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login