Showing 117001 words to 120000 words out of 364327 words
tsaru,hakanan duk abinda ke cikinsa mai kyau ne da tsada,qamshi da sanyin da falon ke bayarwa kadai ya ishi zuciya samun nutsuwa.
Sallama ta qarayi tana wuwwurga idanuwa cikin falon jin shuru ba motsin mutane duk da tana iya jiyo qamshin girki dake tasowa bisa dukkan alamu kitchen din na cikin falon duk da bata iya gano qofar da kitchen din yake,jin still shiru yasa ta juya ta dubi khalipha
"Wai ina ka kawo mu nan ne khalipha,kasan dai nan babu alamun laila,inda tana nan da tuni ka jiyo ka......." Qarar takalmi da ta jiyo alamun ana saukowa daga saman benen ya sanyata yin shuru ba tare da ta qarasa fadar abinda takeson fadin ba
"Ha'an,khalipha ne?" Taji ana fada wanda hakan ya sanyata daga kai.
Farar mace wadda a qalla za'a kira da mai matsakaitan shekaru wanda hutu da tsabta suka kwakwashe shekarunta suka boye,a zahiri ta tasamma shekara hamsin da uku amma kai baka ce haka ba,fara ce tas kamar yadda nace a baya wanda har wani yellow takeyi,kallon farko zaka san cewa zamanin quruciya an kasa maza da yawa a kanta,akwai kyau da kansa zaune a fuskarta,duk da shekarun da take da su amma basu ci nasarar boye kyawun nata ba wanda hakan ke nuna na asali ne ko kuma ace na gado ne,tana da matsakaicin tsaho yayin da jikinta ke a murje,sam babu rama ko qiba tattare da ita,fuskarta a sake take saukowa daga saman tana sanye da jar atamfa da ta haskata dinkin riga da plain zani
"Ummee ina kwana" murmushi ta saki har sai da fararen haqoranta suka bayyana
"Ina kwana ko ina wuni khalipha sarkin shirme,ku zauna mana sai mu gaisa ko?,baquwa mukayi" an aosa masa inda ke masa qaiqayi
"Eh yayarmu ce muka taho da ita ummee,itama ta dawo nan ta zama 'yar gidanmu" dariya sosai ya bawa ummeen duk da kasancewarta mara son hayaniya,gu ta samu ta zauna,hakan ya sanya sumayya dake qame gu daya ta qaraso a hankali kanta a qasa ta samu gefan kujera ta zauna,hakanan take jin matar ta mata wani kwarjini da girma
"A'ah tashi baquwa ki koma saman kujera... Me sunanta khalipha?"
"Anty sumayya"
"Tashi sumayya ki koma sama" kai ta girgiza don ta qagu ta koma gida
"Yanzu zamu koma laila muka zo dubawa anty taji shiru" ta fada sannan ta soma gaidata,amsawa tayi tana cewa
"Na tsammaci ai ta koma tun dazun data kawomin aiken ta fita,amma ba mamaki suna wajen maamaa bilkisu,don nayi hayaniyan yaran gunta"
"To sai anjima" ta fada tana miqewa
"Yauwa rakata khalipha wajen maaamaanku,ki yiwa khadijan godiya naga sautu sunyi kyau"
"To zataji" ta fada suna nufar qofar fita daga bangaren nata,saidai kafin sukai ta shigo,budurwar rannan ce sanye take da gown mara nauyi wadda take armless bata da hannu,sai siririn mayafi data yane tulin tsefaffen gashin kanta da shi ,kumatunta duka biyun da hannunta jagale suke da wani abu kamar butter,sallama tayi tana dariya idanunta a kan ummee dake dubanta itama,harara ta watsa mata
"Da kyau,sannu shugabar masu shiririta,shine kika dora mishi girki sannan kika tafi kika tara yara kuna wani birthday din shirme,to sai ki wuce ki duba Allah yasa ya qone,wallahi ya shigo kada ma ki dosheni don baxan qwaceki ba a hannunshi" idanuwa ta qwalalo cike da tsoro,sannan ta kwashi sauri ta nufi hanyar kitchen din fuska a kwabe kamar zatayi kuka tana cewa
"Wayyo ummee na banu don Allah kada kicemin girkin ya qone"
"Ke kika sani" ummin ta fada.
Shikam khalipha fuska ya bata bayan sun fito
"Ina ga yau bithday din siddiqa shi yasa ma anty laila taqi dawowa gida tunda aka aiketa,tunda naga anty amira ma nasam da qyar idan ba yau bane,dama tun kafin mu tafi kano anty amira tace an kusa,wayyo mami duk ita ta hanamu zuwa" ya qarashe kamar zaiyi kuka,itakam sumayya bata ce komai ba,duban hanya take ganin sun nufi wani sashen na daban.
Tun kafin su shiga ta tabbatar akwai banbanci tsakanin waccen sashen da wannan,tun a qofa ta fara jiyo hayaniya da ifce ifcen yara,da banbancin kam,don wannan falon cike yake da yara sun kusa su goma sha biyu,qananu da matsakaita,baki dayansu sanye suke da gown suma mara hannu,dukkan rigunan irin daya ne,hatta safunan qafafunsu(socks)iri daya ne,yaran sunyi kyau gwanin sha'awa,tsakiyar falon qaton cake ne wanda suka dora kan center suna ta wadaqarsu da shi,da alamu shi ya bata jikin budurwar data gani dazu,kusan ba wanda yaji sallamarsu sai wata mata dake tsaye daura da su tana kallonsu idan zasuyi ba dai dai ba ta gyara musu,ita ta juyo murmushi dauke a fuskarta tana amsa musu sallamar idanuwanta kan sumayya,gaidata tayi tana duban laila da ta nufo gun saboda taga shigowarsu
"Wuce muje" sumayya ta fada tana mai juyawa tare da cewa sai anjima tasa laila a gaba.
Daf da zasu fice taji matar na fadi cikin daga murya
"kuyi maza ku kwashe kayayyakinku zansa a gyara gurin kada uncle ya shigo ya tadda wajen haka...." Bata qarasa jin me suke cewa ba don sun fice.
Suna gab da fita daga gidan baba halliru cikin gaggawa ya budewa motar wadda aketa faman danna horn kamar za'a tashi unguwar,baqar motace wadda ke dauke da baqaqen glass baqi wanda har baka iya hango wanda ke ciki ta danno cikin gidan a guje wanda badan grass carfet dake harabar gidan ba da anga tashin qura
"Hmmm,gata nan ta dawo Allah yasa an tashi ma" laila ta fada tana hararar motar sanda suke qoqarin fita
"Anty su'ad ko?" Inji khalipha ya tambaya yana kallon laila tare da tabe bakinsa
"Itace mana,nifa shi yasa idan tana garin bana son shiga gidan baabaa wallahi anty sumayya" ta fadi tana duban sumayya tana son bata labari,saidai hararar ta sumayyan tayi
"Ke kam laila ke da khalipha bansan wanda yafi wani surutu ba wallahi"
"Wallahi ya fini" inji laila tana dariya,take musu ya sarqe tsakaninsu da khaliphan har suka qarasa cikin gidan.
Shigarta ta tadda wayar gidan nata faman ruri anty dije na kuma saukowa da alama fitowarta kenan daga wankan
"Qarar wayar nan ce ta isheni,tunda kika fita aka dinga kira,hafiz ya daga akace ke nema ya gaya musu baki kusa amma basu daina kira ba,don Allah jeki daga ko kunnuwanmu sa huta" bata fuska tayi ranta na baci,jikinta ya bata mai kiran jiya ne wanda ya kira kansa da alqasim
"Ni wa na sani anty da zai kirani da lambar wayar gidanku,na gaya musu bani bace amma anqi daina kira"
"To amma ya akayi haka?,shikenan....bari na daga na musu bayani" antyn ta fada tana nufar kitchen,sai sumayyan tayi saurin barin falon ta shige dakinta haushinsa na kamata,haka kawai don musiba yana son ya zame mata jarfa,ta bar kanon amma don ta samu hutu ta nutsu amma bata samu nutsuwar ba,ina dalili,su qarke qalau da anty dijen.
*mrs muhammad ce*π
ππππβπ½βπ½βπ½βπ½
β *~KUNDIN QADDARATA~*β
πππππ
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
5β£7β£
*Bismillahir rahmanir rahim*
*wallahi tallahi billahil azim duk wanda baibi Allah ba ya shiga uku,duk wanda baiji tsoron Allah ba ya kade,duk wanda tsoron Allah bai hanashi bin son zuciyarsa ba yana cikin babbar musiba,dan adam ba kowa bane hakanan ba komai bane shi,kaji tsoron ubangijinka kayi biyayya a gareshi KAJI TSORON AZABARSA KAYI KWADAYIN RAHAMARSA sai ka samu rabauta,ka guji duk wani abu mara kyau,kayi riqo da kyawawan ayyuka, 'YAR UWA,KI KARANTA YADDA UBANGIJI DA MA'AIKI SUKA WASSAFA MANA JAHANNAMA,ALLAH KAYI MANA TSARI DA ITA BADON HALAYENMU BA,KADA KA NUNA MANA ITA KO NA QIFTAWAR IDO NE,KA BAMU IKON YIN BIYAYYA A GAREKA,KA KADE MANA ZUKATANMU DAGA TUNANI KO AIKATA DUK WANI SABO KO ZALUNCI*
______________________________________
Kwanaki nata tafiya,tun tana a takure da zaman garin har tazo ta fara sakin jiki,abu daya ke damunta kewar abdallah,tausayinsa take hakanam tausayinsa ya ninku a zuciyarta tun daga randa ya rasa mahaifinsa,kullum takan kira a bata shi su gaisa susha hirarsu,abinda ya sake kwantar mata da hankali a nan ba inda take zuwa bare ta gamu da wani yace mata yana sonta,hakanan kiran waya ma da ake ana nemanta tun ranar da anty dije tayi magana aka samu sauqim kiran,sai jifa jifa shi din ma ba dagawa take ba,abdur rahman ne kadai ke kiranta su sha hirarsu har ta riga da ta saba,babu wata rana da zata fito ta fadi bai kirata ba,ta sake sosai don bai qara yi mata wata magana daban ba banda ta zumunci,anty dije tayi ta mata tsiyar batasan muguwar kifin rijiya bace ita sai yanzu,bata son zuwa ko ina,ko gidan baabaa prof shigarta biyu kwata kwata shima da dalili na farkon kiran laila da taje,na biyu kuma da sumayyan tayi dambu gidan ba yara ta sata ta kaiwa anty maamaa da yake ita mai son dambu ce,kota shiga din ma bata wuce minti biyar ko goma ta fito,hakan ya sanya anty dije ta bada sautun kayan turare da humra aka kawowa sumayyan ta soma yi a nan,cikin designers kwalabe take zubawa,nan take kuwa ta soma ciniki,duk da wani gu ake kaiwa,'yan unguwar ne kawai ki zuwa siya cikin gida.
Yau ma kamar kullum babu yara a gidan suna makaranta,gab suke da fara jarabawa ayi musu hutu saboda gabatowar wata mai alfarma na azumin watan ramadan,suna zaune da anty dije a kitchen tana anty dijen ke girki yau sumayya na ganin yadda take yi din don bata iya irinsa ba,iya zamanta da anty dijen ta qaru da abubuwa da dama ta fannin zamantakewar gida,girki iri iri,gyaran jiki da kuma uwa uba iya gayu,wayarta anty dijen ta daga wadda ta fara ruri ta kara a kunne,ganin haka sumayya ta karbi yankan cabbage din da takeyi taci gaba,sai data gama sannan ta dubi sumayyan
"Sumayya,inaga fa ke zaki miqawa anty maamaa humrar nan,kaya take hadawa kuma kinga yaran basu dawo ba" kasaqe tayi,sarai anty dijen ta gane bata son zuwa ne,bata san me yasa bata qaunar shiga gidan ba amma sai ta shareta,ta gane mai anty dijen ke nufi tilas ta miqe tace to,dakinta ta shiga ta sanya dogon hijabinta har qasa sannan ta jawo ledar data jera humrorin wadda anty maamaa ta bata tayi mata,saboda umrar azumi da zasu tafi ita da maigidan da kuma ummee,sai babban yaron gidan shi da matansa biyu sai qaninsa da tashi matar,sai manyan jikokin gidan su biyar duk da basu wuce shekara sha hudu zuwa qasa ba,duk laila aku(sunan da idan taso take kiranta da shi kenan kusamman idan tayi hali ) ke bata wannan labarin tunda ita ba shiga take ba ballantana ta sani.
Kamar kullum a hankali ta dinga ratsa gidan bayan sun gaisa da mai gadin dake gadin wannan qofar sa suke shigowa da yake akwai wata qofar ta baya,mutumin ya haifeta shi yasa take ganin girmansa,mutum me mai faran faran da son jama'a,duk da ganinsa da sumayyan baifi uku ba amma yana yabawa hankalinta yadda take rusunawa ta gaidashi,duk da yasan iyalan gidan alhj umar farouq ba baya bane wajen tarbiyya.
Kanta a qasa qirjinta na bugawa ta dinga kutsawa cikin gidan,batasan me yasa take yawan faduwar gaba ba idan ta shigo gidan,ko don tana ganin kamar akwai banbancin matsayi tsakaninsu bai kamaci ta dinga shiga musu gida ba.
Tazo mararrabar sashin anty maamaa data ummee sai taso ta manta wane waje ne na anty maaman don bata rarrabewa da sunayensu,a hankali ta juya idanuwanta tana canki canki,karaf idanuwanta suka sauka a kansu,zaratan samari ne ke tsaye su biyu suna magana da junansu,dukkaninsu dogaye ne saidai daya yafi daya masu matsakaicin jiki,kowannensu na sanye da t.shirt da trouser masu mabanbantan kaloli kowa da kalar nasa,farare tas da su kamar yadda ta dan fahimci haka kalar fatar masu gidan take,fuskar daya kawai taje gani bata ganin ta dayan kasancewar ya juya baya ne yana magana da dayan,da alamu kuma duk hankalinsa na kanshi,shima ya ganta,idanu ya sanya yana kallonta har waccan ya kammala fadin abinda zaice yayi gaba ya shige daya sashen.
Rudewa tayi kamar mara gaskiya,jikinta ya soma rawa ta fara qoqarin juyawa ta koma inda ta fito ganin kamar yana takowa inda take
"Wa kike nema?" Ya tambayeta fuskarsa ba yabo ba fallasa,cikin qoqarin daidaita nutsuwarta ta hada kalmar
"Sashen anty maamaa nake nema"
"Ko gun amira kika zo?" Ya sake tambayarta yana kallon ledar hannunta,bata ma gane wace amirar ba,sai tave masa
"A'ah,saqo na kawowa anty maamaa" sai taga ya saki murmushi
"Yauwa,muje ma na rakaki,Allah yasa wannan turaren mai dadi aka kawo mata wanda tamin alqawari" ya fada yana yin gaba cikin mishadi,ta bishi a baya tana cike da mamakin sauqin kai irin nasa,batayi tsammanin haka ba.
Falon suka shiga yana sallama cikin daga murya,wannan budurwar da take zaton ita ce amirar ta fito da sauri daga kitchen tana dariya,bata lura da sumayya dake bayansa ba,ganinsa ya sanyata tsaya tana dubansa tana qyalqyala dariya,da alama wani abu da ya faru dazun tsakaninsu taje tunawa
"Ya akayi yaya mahmoud?" Ta fada tana sake tuntsira dariya
"Zaki zo hannu ai kin sani.....yanzu ba wannan ba ga baquwa nan tazo wajen anty maamaa" dan leqowa amiran tayi inda sumayya ke tsaye,sai tayi murmushi
"Ba baquwa bace a gidansu umman khlipha take,duk da dai baquwa ce a gidan nan saboda na fuskanci bata son mutane" ta fada tana murmushi
"Ke kuma gaki da shegen kwashe kwashe ko,ki bata guri parrot tukunna,ki gayawa anty zan dawo anjima,yanzun yaa man ya aikeni ne" ya fada yana juyawa zai fice,ganin haka yasa amira daga murya
"Don Allah ya mahmoud ka siyo min na tuba" ta fada a shagwabe tana kama kunnuwanta guda biyun,harara ya watsa mata yayi ficewarsa,sai ta narke fuska kamar zata yi kuka har ya bace a falon kafin ta maida kanta wajen sumayya.
Murmushi tayi mata sannan tace
"Ga waje zauna,amma sai kin dan jira antyn don tana wajen dan tsohon mijinta,kinsan ba'a kiranta idan ya shigo sai mutum ya jirata" ta fada cikin salon tsokana tana dariya,itama sumayyan sai ta saki murmushi,kusan haka halayyar anty dije take,take mukhtar ya fado mata,a hankali sai murmushin nata ya soma gushewa damuwa ta fara bijiro mata,take ta fada kogin tunani tana tuna wasu lokuta masu dadi daga cikin rayuwar da sukayi tare da shi.
"Ga lemo bismillah" amiran ta fada tana ajjiye tray data dora lemo da kofuna a kai,kai sumayya ta kada cikin murmushin yaqe tace
"Alhamdulillah,a qoshe nake"
"Al'adar gidan anty maamaa ne,dole kisha wani abu kafin ta fito" ta fada tana tsiyaya mata a cup,kallonta sumayya tayi tana yaba karamcin hakan,sai a sannan taga kamanni da wanda ta kira mahmoud a dazu,da alama kwai dangantaka ta jini mai qarfi tsakaninsu,hannu ta saka ta karba tana fadin
"Na gode"
"Ba komai,bari na duba girki kada ya kama"
"To" sumayyan tace,kurbe daya tayi masa ta ajjiye damuwa ke sakadarta,a haka taji an bude wata qofa dake can wani sashe daban na falon,anty maaman ce ta fito tana cewa
"Ayyah tun yaushe kika zo" murmushi tayi
"Ban jima ba,ina yini" ta gaidata amsawa tayi tana zama tare da amsar ledar humrorin,budewa tayi tana shanshanawa tare da yaba yadda sukayi bala'in qamshi,godiya tayi mata sosai tamkar ba biyanta tayi ba,miqewa tayi tana shirin tafiya
"Umhmmm,za'a gudun ne?" Amira take baro kitchen ta fada tana dan murmushi,waiwayawa tayi tana dubanta itama fuskarta qunshe da murmimushin,sam batayi zaton zata yi sauqin kai haka ba
"Na baro aiki ne a gida shi ya sa"
"Ayyah to sai yaushe?,ko sai na shigo?"
"Allah ya kawoki lafiya"
"Amin,ni sunana sumayya na gaskiya,sunan mamar babanmu ce ake kirana amira,kefa?" Murmushi ta saki
"Nima suna na kenan?" Idanu amiran ta zaro gami da rufe baki
"Kai kai,dama baabaa na kusa ya ganki,yaga mai sunan mamarshi,yana son mai sunan mamarsa wallahi,me ake ce miki to?"
"Shi ake gayan" kai ta kada sannan tace
"Gaskiya ni bazan fadi haka ba,zan dinga kiranki kema da amira,amiran umman khalipha" dariya sosai sumayya tayi
"Shikenan to" ta amsa mata sannan sukayi sallama ta juya da niyyar fita tana dariya amiran,kusan zasuyi shekaru daya da ita,saidai yanayin inda ta taso da gata sai take ganin kanta kamar qaramar yarinya,duk da aqalla zasuyi shekaru ashirin da daya.
A bakin qofar shigowa falon taji tayi karo da abu har yana bangazar kafadarta,da sauri ta ja baya tana fadin
"Subhanallah"
"Mtsweeeeww" taji an tsaki,baya ta sake ja tare da daga kanta tana kallonta wanda ita dinma kallonta take,saidai nata kallon yasha bamban da wanda sumayyan ke mata,kallon farko ta fahimci macace mai izza da jin kanta,haka yake don sumayya bata yi qarya ba,matashiya ce dake jin duniyarta dai dai,wadda a qalla ta doshi shekara ashirin da takwas a duniya,doguwa ce sosai hakanan siririya ce,fara ce itama sosai kamar yadda sauran suke,sanye take da wani baqin hight rise slim leg jeans da v neck t.shirt mai gajeran hannu,hakan shi ya fiddo surar ta da shape dinta baki daya,kanta yane da wani dan kwali mai santsi don ba za'a kirashi mayafi ba,idanunta saye da sun glases da ya kusa cinye rabin fuskarta,wani kallo take wa sumayyan na sama da qasa cikin izgilanci kafin ta zare gilashin nata,tsaki ta ja kafin ta wuce tana taku dai dai tana duban amira
"Maamaa fa?" Ta tambayi amira kamar bata son yin magana
"Ta haura sama" ta fada tana nufo sumayya dake gab da ficewa daga falon,da sauri ta daga murya
"Kiyi haquri sumayya" amiran ta fada cikin damuwa,sai ta waiwayo tana sake mata murmushi tare da fadin
"Kada ki damu", sai da sumayyan ta fice sannan ta dawo da kallonta cikin falon ta saukesu kan wadda ta shigo din,sai ta kada kai kawai ta shige kitchen ganin ta zauna saman kujera tana jiran saukowar maamaan,ta sani sarai ba zata iya haurawa saman ba dama idan ba da wani qwaqqwaran dalili ba,shi ya sanya tayi saurin komawa kitchen don kada ma