Showing 345001 words to 348000 words out of 364327 words

Chapter 116 - KUNDIN KADDARATA COMPLETE HAUSA NOVEL

HUGUMA   

20 Aug 2024

40130

to the point,akwai masu jira,meke damunki?" Ya tambaya yana rubuce rubucensa,sumayya na gefe dariya na son qwace mata,ya koma sak doctor almustaphan dan gidan baba prof data sani a baya,nuqu nuqu ta soma yi saboda ganin sumayya a wajen,tsaf ya karanceta,sai kawai ya rufe file din nata ya tura mata gabanta
"Zaki iya tafiya" ya fada yana kafeta da mayun idanunshi
"Ai..ai sirri ne" ta fada cikin in ina,juyawa yayi ya dubi sumayya da dariya ke ci,amma sai ka zata batasan meke faruwa ba
"I said the door is opened ko?" Ganin cewa da gaske yake ya sanya ta samawa kanta nutsuwa ta soma masa bayani,magunguna ya rubuta mata yace taje ta karba ya sallameta ta miqe ta fice.


Dariya sosai sumayya ta saki kafin nxt patient ta shigo
"Me?" Ya tambayeta yana kallonta,da kanshi kuma ya saki fuskar yana dariya,ya gane me takema dariyan,sai ya cafko yatsunta ya soma lanqwasa mata,ga dariya ga zafin lanqwasa matan da yake,da qyar ta qwaci kanta
"Ku kam mata wlh i dont know.....kai...kai" ya fadi ba tare da ya gama fadan me zaice din ba
"Duka ke kika jawomin,da tuni na gama mun tafi ina gida ina hutawa,ko baby bamu gaisa da shi ba" ya fada yana shafa cikinta,turo qofan da akayi ya sanyashi janye hannun nashi,a nutse yaci gaba da dubasun har ya gama sannan suka tattara suka nufi gida.


Cikin falon nashi dake dauke da dakin bacci biyu suka sameta kwance tana kallo,sanye da riga shimi doguwa zuwa gwiwa,gajeran hannu ne da ita hannun vest,ciki ciki ta amsa sallamar tasu sannan ta daga ido ta bisu da kallo.







*mrs muhammad ce*👑

📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖


*~NA~*

*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*

*WATTPAD:HUGUMA*

*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)



1⃣0⃣5⃣

*Bismillahir rahmanir rahim*

*Allah S W T yana bayyana kansa cikin qur'ani mai girma da*

*FA'AALIL LIMA YURID(mai aikata abinda yakeso*

*ya Allah muna gareka kayi mana jagoranci*
_____________________________________

*Wannan shafi sadaukarwa ne ga*

*HAUWA'U AG tare da diyanta AHMAD*





        Ba wanda ta amsa sallamarsa a cikinsu,hakan ya sanya sumayya tayi wucewarta ba tare data sake cewa komai ba.

        Satinsu biyu dai dai a kano suka koma dubai,bayan sun ziyarci gidan maimmartaba sarkin rano,mahaifin ummi,tsoho mai ran qarfe,karon farko kenan da sumayya ta kai ziyara,tsantsar soyayyar da tsohon kewa almustaphan ta shafi sumayya,kowa haba haba yake da su yana neman wajen ajjiuesu,taga kara taga karamci,ba qaramin dadi zuwan yayi mata ba,duk da bata samu zuwa gidajen sauran 'yan uwa ba,amma tayi alqawarin duk sanda tazo kano toba shakka zata sake zuwa musu,kyautar girma tsohon yayi musu shida matanshi,duk da mahaifiyar ummi ta rasu,amma matan baban nata sun daukeata tamkar diyarsu,suna farinciki da juna suka rabu,tun a sannan ummi taso riqe sumayya har sai ta haihu amma almustapha ya shafawa idonshi kwalli yace ba yanzu ba zai kawota idan lokacin yayi,yayin da cikin zuciyarshi ma sam ba haka bane,don baida niyyar kawota din,yana ganin meye amfaninsa a matsayinsa na likita kenan.

      A hankali kwanaki suka ci gaba da wucewa,ba abinda ta daga qafa ko ta sauya game da kyautatawar da takewa almustaphan,dukkan wani abu data sani cewa yana so takan sanyashi gaba da komai nata,lamarin su'ad kam sam baya damunta,duk wani iskancinta da tambotsanta basa gabanta,sai taga dama ma zata ganta bare wani sabga ya hadasu,abu daya take qoqari a kai shine tausar almustapha a duk sanda ta kunnoshi,sam bazata so ace su'ad din tabar gidan na,kullum fatanta shine Allah ya shiryata ta gane illar abinda take yi,ta tabbatar da cewa duk duniya bata da wata mafita matsawar almustapha ya sawwaqewa su'ad tofa za'a ce itace sila,bayan duk wanda zaiyi alqalancin baisan meke wakana game da zamantakewar auren su'ad din cikin gidan ba,saidai hasashe dai kawai.

       A haka cikinta ya shiga watanni tara har ya soma yunqirin shiga na goma,kallo daya zaka mata ba zaka so sake dubanta ba sabida tausayi,sosai cikin yayi wani girma har wani lokaci sai ta tallafeshi idan tana tafiya saboda girmansa da yadda ya sauko qasa,ta sauya kamanni sosai kamar ba sumayyan ba,munin da tayi a da nafila ne,har bata son kallon kanta a mudubi,sau tari idan taga almustapha na kallonta sai ta kau da kai tana tunanin munin da tayi yake kallp,saidai shi sam ba haka bane cikin zuciyarshi,tsananin tausayinta ke damunshi,ba don kada yayi riga malam masallaci ba da tuni ya yankata ya cire mata cikin ta huta,yakan tallafo fuskarta ya saki murmushi
"Ki daina boyen fuskarki,a hakan kinmin kyan da ban taba ganin kin yimin irinsa ba,kinsan me?" Sai ta kada kai cikin murmushi
"Da zaki sake zama haka nan da wata takwas ma bayan kin haife wannan cikin ina so,da nafi kowa murna"
"Kayimin addu'a Allah ya rabani da wannan ma lafiya"
"Yadda zuqar numfashina ya zamemin dole haka wannan addu'ar ta zamemin dole" ya fada yana karata da jikinsa tare da shafa bayanta a hankali yana ci gaba da yi mata addu'a cikin ranshi.

       Semina ce ta kamashi ta sati guda wadda za'a yi a china ta 'yan kasuwa,sam yace ba zashi ba,ita ta tausashi da qyar tace ba'a jiran haihuwa sai sanda Allah ya kawota,ko kadan baison tafiya don ko fita ya rage,tausayi take bashi matuqa,hatta tashi sai tayi da gaske take iya yinsa ko shi ya dagata,ita ta tayashi hada kayanshi tana yi tana tsokanarshi wai ya zama rago,jawota yayi jikinsa yana dan mintsinarta yadda ba zata ji zafi ba yana murmushi
"Laifin wa?uhmmm babe,bake kika maidani haka ba?" Dariya ta saki,ta jawo hannunsa ta dora saman cikinta
"Laifin wannan ne ba nawa ba"sake matseta yayi a jikinsa yana sakin murmushi,tasan duka hanyar da zata sashi nishadi.

       Sai da ya hadata da babban asibitin dake qasar wanda anan yake musu aiki lokaci lokaci,ya basu lambarta lambar gidan da adress,sannan itama ya bata number dinsu,sannan ya karba mata nurse guda daya wanda suka tanada saboda jinyar marasa lafiya wadda zata dinga zuwa tana kwana da ita,sam bai fadawa ummi ba don ya tabbatar cewa zatayi ya turota nigeria,shikuwa baison ko daya abinda zai rabashi da ita dai dai da minti daya

       Tattaki ta masa har zuwa cikin falonta,kasancewar ranar girkinta ne,ya jawota kusa da shi ya riqe dukkanin hannayenta cikin nashi yana duban qwayar idanunta
"Kimin alqawari zaki kulamin da kanki har na dawo,ba tunani ba damuwa,kinyi alqawari?" Murmushi ta sakar masa mai kwantar da zuciya ta gyada kai
"Nayi maka noor,Allah ya tsaremin kai ya dawo min da kai lafiya"
"Amiiin baby na" ya furta yana lumshe idanunsa sannan ya matso da ita gab da shi yayi kissing goshinta zuwa wuyanta.

       Tare da su'ad suka rakoshi har bakin mota,sai da driver ya ja suka fice sannan kowacce ta juya zuwa ciki,wani kallon banza take jifar sumayyan da shi gami da jan dogon tsaki,bata kulata ba don idan da sabo ta saba,tayi wucewarta ciki abinta.

   *******    ****   ********

     Bayan kwanaki biyar da tafiyarshi ne inda suke saka ran dawowarshi jibi,tun safe take jin ciwon mara kadan kadan,saidai bata gayawa ko nurse dinta ba saboda tunda cikinta ya shiga wata na goma take fama da irin hakan kadan kadan lokaci zuwa lokaci,yanzun ma fitsari ne ya tasheta,sai data dauki a qalla minti biyar ta iya yunqurawa ta miqe,mararta ta amsa sai data ce wash sannan ta iya miqewa a daddafe ta qarasa bandakin mararta na ciwo sosai,koda taje fitsarin kadan tayi sai ciwon da ya dadu,dawowa tayi cikin dakin ta soma kai kawo a tsakar dakin,a jikinta take ji tabbas naquda take,bata da maraba da abinda take ji lokacin haihuwar abdallah.

      Tsahon awa daya tana gumurzu babu sassauci,hakan ya sanya ta fito falo a daddafe,ta dauki waya ta kira lambar nurse din,cikin sakanni kadan ta iso ta dubata ta tabbatar haihuwa ce,saidai akwai saura,asibitin ta sanarwa,babu jimawa saiga mota sun aiko da ita suka daukesu suka wuce,su'ad taji motsinsu,ta dauka wasu ne ta leqo da taga sune ta koma tayi kwanciyarta abinta.

      Daki ne na musamman suka bata,dauke da na'urori kala daban daban bayan ta sauya riga zuwa ta asibiti,tun tana daure ciwon har abun ya soma wuce tunaninta,naquda take haiqan saidai haihuwa tawi zuwa,tun biyu na dare har gari ya waye haihuwa bata zo ba,daga gefan almustaphan ya kira wayarta yafi a qirga saidai ba amsa,saboda sun baro wayar a gida,ya kira su'ad tace bata sani ba,bata gama bashi cikakkiyar amsa ba ma ta kashe wayarta,yayita kira switchoff,take hankalinsa ya tashi,sai sannan yayi dana sanin me yasa ko baba uwani baisa an kawo ba?,kai tsaye ya kira asibitin nan suka shaida masa tana nan tun daren jiya,ranshi ya baci hankalinsa ya tashi,fada ya hauyi kan me yasa basu shaida masa ba?,sannan ya za'ayi su barta tun jiya har yanzu wayewar gari tana naquda har ta kusa cinye awanni da aqa'idar likitoci ba'a so ta gama su bata haihu ba,haquri suka shiga bashi,bai sauraresu ba ya katse layin ya soma tattara ya nasa ya nasa ba tare da ya kammala abinda ya kaishi ba,hankalinsa gaba daya yayo dubai,jinsa yake kaman yayi tsuntsuwa ya ganshi a can.

        Qarfe hudu na yamma ya iso dubai,kai tsaye ya yiwa drivan umarni ya wuce da shi asibitin,kai tsaye ya wuce dakin da take,kwance take saman gadon,kallo daya zaka mata kasan cewa ta jigata qwarai,duk sanyin dake dakin bai hanata gumi ba,muryarshi kawai taji ta daga kanta taba dubanshi,tuni ya ajjiye jakar dake hannunsa ya qarasa inda take,nurses din dake dakin suka fice daya bayan daya,tafin hannunta ya laluba ya sanya nashi hannun ciki,hannunsa saman kanta yana shafawa a hankali,baki daya zuciyarsa ta karye
"Baby......sannu baby" ya fada idanunsa cikin nata,ga mamakinsa murmushi ta sakar masa a wahalce
"Ka dawo?"
"Eh...." Maganar tasa ta katse sanda ta furta
"Hasbunallahu wa ni'imal wakil!" Cikin madaukakin sauti ta soma murqususu cikin matsanancin ciwon da ya taso gadan gadan,tamkar dama jiran zuwan almustaphan yake,yanayin yadda yaga tanayi ya sanyashi sake dubata da kanshi,nan ya tabbatar haihuwar ce,nurses din da suka fita ya kirawo don su taimaka masa,din bashi da qwarin gwiwar da zai iya karbar haihuwar shi kadai,yana riqe da ita yana gaya mata addu'o'i tana maimaitawa cikin wahala,a qalla mintuna goma kafin jaririyar ta samu isowa duniya,kukanta ya karade ilahirin dakin baki daya har zuwa waje,basu gama tantance komai ba ta sake wani yunqurin,wani sabon kukan ya sake karade dakin suka hadu suka cika ilahirin dakin zuwa harabar dakunan da kukansu,nurses din ne suka dauke yaran yayin da baki daya hankalinsa ya raja'a a kanta,gumin da ya mata sharkaf ya soma goge mata yana jero mata sannu babu qaqqautawa,dubanshi take yadda ya rude baki daya,kukan yaran na yawo cikin kwanyarta,tasbihi take wa ubangijin talikai,yau gata a karo na biyu ta sake samun diyoyi,diyoyin da suka fito daga tsatsonta,kasa dauke idanunata tayi daga shiyyar da yaran suke sankda nurses suka gama rabasu,kukansu suke sosai suna wutsil wutsil da qafafu da hannyensu,sakayau a yanzu take jinta kamar sun fita da duk wani ciwo dake damunta.

       Cikin mintuna qalilan nurses din suka soma gyara yaran,shi kuma ya gyara ta da kanshi a wani daki daban,komai ya kammala,aka maidata zuwa wani dakin ita da yaran baki daya.

        Zaune take saman gadon sosai tana jingine da bango,murmushi ne sosai kan fuskarta wanda har sai da ya sanya haqoranta bayyana,idanunta taf da qwalla sanda almustapha yake nufota dauke da daya daga cikin jariran wadda ke nannade cikin wasu irin kayan sanyi masu azabar kyau set da abun daukansu,gabanta ya qaraso shima idanunsa cike da qwalla yana dubanta tare da duban babyn,miqa mata ita yayi sai ta dauke idanunta qwallar data cika mata idanu tana gangaro mata saidai har yau murmushin dake kan fuskarta bai bace ba,da hanzari ua sake matsarta ya kama hannunta yana matsawa cikin rauni da rawar muryar da bata taba ji daga gareshi ba yace
"Kada kice zaki ji kunya babe....karbi diyarki ki gani in dauko miki dayar....duniyarmu ce baby duniyarmu....daga ni sai ke sai su karbi ki gani", ya qarashe maganar yana dora mata yarinyar saman cinyarta,tuni ta sanya hannu ta karbeta,cikin sakanni qalilan qaunar data ke musu taji ta soma ninkuwa cikin zuciyarta,sak jinin gidan baba prof,kana dubanta ko makaho ya shafa yasan jikar mutanen gwambe ce,photocopy na almustapha,sake komawa yayi ya dauko dayar ya dawo saman gadon ya zauna sosai kusa da ita yana bude mata fuskarta
" kalli usaina baby.....ba wadda ta miki kara?"ya fafa yana sakin dariya wadda ke qunshe da zallar farinciki,jinsa yake yau kaf duniya babu dan adam din da ya kaishi farinciki,ba wanda kuma ya kaishi sa'ar zuwa duniya,itakam murmushi kawai take bakinta ya gaza furta komai,Allah kenan,buwayi gagara misali,cikin rayuwarta kaf bata taba kawowa kanta haihuwa bama bare kuma aje ga haihuwar 'yan biyu,dai gashi a yau,Allah yayi mata kyautar da bata taba hasashenta ba,haqiqa Allah mai tsananin karamci ne,sosai almustaphan ya dinga sumbatu wanda tasan na tsantsar farinciki ne tana dubanshi tana dariya,ita din ma jinta take saman wata duniya ta farinciki tana yawo,ta kasa dauke idanunta daga yaram,ba don yaranta bane,amma zata iya cewa bata taba ganin jarirai masu ban sha'awa irinsu ba,sam ya mance da ya wanu kira gida ya fada sai data tuna mishi,a sannan ne ya dauko wayarshi,ummi ce mutum ta farko da ya soma kira,danda yake gaya mata tsaye ta miqe tana kabbara,bata qarasa jin zancan ba ta rankaya falon baba,saidai kash kafin ta isa tuni anty maamaa ta rigata kai labarin,wanda ta jishi je sanda take shigowa wajen ummi,a take baban ya mata kyautar kudi masu tsoka,ta dinga ma ummi dariya tana cewa saidai a tara a gaba,itama dariyan ta dinga tace rabonki ne,duk yadda baban yaso sakaya farincikinsa abun yaci tura,haka shima ya dauki waya ya dinga kiran abokai da 'yan uwa yana sanar musu,cikin lokaci qanqani labarin haihuwar ya karade kowanne sakaye,tsakanin baba da malam sai aka rasa wanda za'a yiwa murna,amira kuwa da anty dije kukan farinciki suka sanya,ta dinga kiran almustaphan tana roqonshi zata taho yace sam,sai ta saka kuka,tana so ace cikin dangi itace mutum ta farko data fara daukan yaran,abu daya ne ya saka mata haquri hoton yaran da ya dauka ya tura mata ta email adress dinta,don shi baya watsapp.

      Da kanshi ua sallami matarshi bayan ya tabbatar da cewa komai lafiya suka kama hanya zuwa gida,yana bayan motar shi da ita,baki daya yaran na hannunshi ya hana mata ko daya,ji yake idan ya rufe idanu zaiga kamar mafarki kamar almara,ashe duk arziqinka duk dukiyarka,duk farincikin da kake taqama kana ciki bai gama kammaluwa ba matuqar baka samu diyoyin da zaka alaqanta da jininka ba,ashe zallar farincikin da zata fadeshi sai randa ka ganka dauke da zuriya taka ta kanka.

        Daidai sanda suka nufi gidan su'ad na tsaye tsakar dakinta tana amsawa wayar da suke da mahaifiyarta
"Nifa gaskiya su'ad na soma sarewa,kinga tsantsar farinciki da doki da professor yake ciki sanda ya kira mahaifinki kamar ranar aka soma haifa masa jikoki,anya kuwa su'ad ba muyi kuskure ba?,ina da yaqinin Allah kadai yasan dukiyar da zasu samu su kuma mallaka tun suna qananunsu,wanda dukkan abinda suka samu zai koma fa hannun mahaifiyarsu ne" qatuwar ajiyar zuciya ta saki
"Bama wannan ba momy,wallahi na tabbatar na shiha uku,duk wani soyayya da tattali da adalci da almustapha ke qoqarin gwadamin ina da yaqinin sai ta ragu,tun cikin bai fito duniya ba kinga abinda yake?,ina ga ya fito sannan kuma twince mommy?,shi yasa nake tunani anya ba zamu sake plan ba?,na nemi dalilin haihuwa nima ko don na sake janyo hankalinshi zuwa gareni baki daya?"
"Dqlla can rufewa mutane baki,ke ta soyayyarsa ma kadai kike,soyayyar vanza,ana miki maganar kudi abokan tafiya qare magana,so nake fa ki zama cikin jerin attajiran da duniya ke lissafinsu kaman yadda a yanzu mijin naki yake,ke kadai ce fa 'yata ke daya na mallaka,saboda haka ina so naga kinyi shaharar da ko d'a namijin da yayi shekara arba'in yana gwagwarmaya baiyita ba"
"To yanzu ya za'a yi momy?"
"Cikin satin nan kisan yadda zakiyi kizo nan mu warwareta"
"An gama" ta fada tana katse wayar saboda motsi da taji kaman ana shigowa,a hankali ta tako ta fito zuwa falon,almustapha ne riqe da baby daya,wata mace mawociyarsu 'yar asalin qasar saudiyya dauke da dayan,fuskarta a washe tana tana yaba kyawu da girman yaran cikin harshen larabci,duk da bata fahimtar me take fada amma daga yanayin matar tasan tana yabawa ne da yadda yaran suke,idanu ta zuba musu tana karantar fuskar almustapha wanda bata san da dawowarshi ba saibyanzu,tunda sukayi magana ya tambayeta sumayya tace bata sani ba bai kuma kira ba hakanan bata bi ta kanshi ha itama,iya tsahon zamanta da shi bata taba ganinshi cikin wannan hali na matsanancin farinciki ba, saidai ba wanda ya kula da ita a cikinsu saboda tana daga bayan labule ne har suka shige.

      Yana fitowa daga dakin ya lura da ita,fuskarshi sake yake dubanta,bacin rai da take dannewa ya taso yafi qarfinta,sai kawai kuka ya qwace mata,sai ta juya da gudu gudu ta koma ciki,tausayinta ne ya sauko masa lokaci guda,yana tunanin rashin samun tata haihuwar shi ya motsa mata,wanda hakan zai iya faruwa ga kowacce mace,kowanne lokaci kuma yanayin kan iya motsuwa cikin zuciyarki har ki kasa controlling din kanki,sai ya rufa mata baya,samunta yayi kuwa zaune saman kujera tana buge buge da hannunta,dama ace dama ace ce fal cikin zuciyarta,zata so a ce itace ta samu wannan yaran ba sumayya ba,wai shin me ya hanata tsayawa ko guda daya ta samu ne?,ba shakka tana ji a jikinta lokaci yayi da zata tashi ta dawowa da kanta dama ta samun haihuwa a gareta,a tausashe ya zauna gefanta yana riqeta,baison idan wani abu ya sameta ta dinga irin wannan acting din dake nuna zallar rashin yarda da qaddara,cikin taushi ya soma ce mata
"Am sorry dear....ba kuka zakiyi ba,addu'a zakiyi Allah ya kawo mana,komai a duniya yana da lokaci sannan komai yai farko yana da qarshe banda ikon Allah,matuqar kina da rabo ta babu makawa sai kin haifa kema"
"Ko bani da rabo wallahi sai na yishi,sai na haihu


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login