Showing 303001 words to 306000 words out of 364327 words

Chapter 102 - KUNDIN KADDARATA COMPLETE HAUSA NOVEL

HUGUMA   

20 Aug 2024

40125

naci tuwo kuma sai kiyi batan dabo,inata nemanki na bada tukuici" qas tayi da kai tana wasa da yatsun hannunta kawai,ya tambayi lafiyarsu baki dayansu suka amsa mai,ganim almustapha sun soma hira da adam yasa almustapha yace suje wajen ummeen shi zaizo,su'ad ita ta fara yin gaba,sumayya na bayanta,ganin tayi wucewarta bata ko saurari bangaren anty maamaa ba ya sanyata ita shiga ta gaidata,taji dadi kuwa sosai,bangaren itama sai ita daya,dama can yaran mazan ba zama suka fiya yi ba,bare yanzu da kowa ya kama nashi gidan,don su a waje suke zaune,saidai kowanne yace idan yana sha'awa zasu zo suyi kwana biyu cikin gidan tunda suna fa wajensu,sosai taji dadi suka dan taba hira atsaitsaye ta wuce zuwa sashen ummee,tana gab da shiga su'ad ta fito tana hura hanci,ganin tana yunqurin bangazarta ya sanyata ja gefe,wani kallo su'ad din ta watsa mata sannan cikin harshen turanci tace
"Banza" murmushi ta jefeta da shi,cikin salon nuna qwarewa itama ta karya nata harshen da salon data koya a uk
"Banzayen ai suna da yawa ba daya bace,suna da yawa,bansan wacce daga ciki kike nufi ba"cewar sumayya sannan ta juya hankali kwance tayi shigewarta.

        Cikin kulawa suka gaisa ta samu gefan ummin ta zauna,bakin kowanme yayi nauyi,sumayya ya kunyar ummin ita kuma yau ummin surukuta ce ta motsa,saidai duk motsin sumayya tana lura da ita,sai take ganin ta soma sauyawa baki dayanta,jefi jefi suka dinga hira da ita har almustaphan ta shigo ya taddasu,baiyi zaton zai sameta har tsawon lokacin a nan ba,a sannan ummi ta shiga kitchen tana hanyar fitowa ta jiyoshi yace
"Baki gaji da zama ba?,akwai magungunan da zaki sha fa?"
"Me ya sameta?" Ta fada tana fitowa akitchen din tana fatan jin abinda zuciyarta keta faman raya mata,kanshi ya shafa yana jin nauyin ummin
"Ciwom ciki ne,kuma tana shan magani yanzu haka yana samun sauqi" ta san zurfin cikinshi qwarai,sai ta zauna tana cewa
"Allah ya sawwaqe,lallai kam ki kula da shan magani"ta miqawa sumayya wani dan bowl na plastic mai garai garai wanda akayi wrapping dinshi,maganar tata sai ya jita kamar a baibai,gaba yayi cikin jin nauyi yana cewa ta taso su tafi,ummi ta bita da kallo sanda ta miqe tayi mata sallama,sai taji tamkar ra tsaidata taji ainihin meke damunta,saidai kuma koma meye tasan indai da gasken ne abinda take zato to nan da wani dan lokaci qanqani zata fasu,suna ficewa ta samu kanta da yin sujuddushshukur,duk da bata tabbatar da cewa hakan bane,wani farinciki data jima bata ji irinsa ba yana ratsata,tamkar bata taba riqe jika ba.

*******     ******    *********

      Bai taba riskar kansa cikin farinciki ba irin na wadan nan kwanakin,bai taba tunanin haka samun d'a yake dadi ba sai wannan karon,ashe daa baki daya hasashene kawai yake yi,sumayya kam na fama da laulayi sosai,saidai Allah ya bata wata juriya da qwarin gwiwa,tana matuqar qoqari wajen boye ma almustapha,saboda kullum kwanan duniya tunaninshi na kanta ita da abinda ke jikinta,bai da sukuni yana gida koko baya gida,dawainiya yake da ita bilhaqqi,idan da yana da iko numfashi ma shi zaya yi mata,bata taba cin karo da soyayya kwatankwacin wannan ba,bata taba zaton ita din sumayya abar soce har haka ba,bangaren su'ad kuwa gani take Allah ya sita da bata taba gwada daukan ciki ba,musamman duk randa amai ciwon kai ko zazzabi ya make sumayyan,da yake sautari yanzun tana yawaita zaman falo,haka kawai sai taji bata sin zaman dakinta,a falo kawai take jin dadi,idan zata kwana tana amai ba abinda ya shalli su'ad,saidai ta watsa mata baqar magana
"waya kaiki da zaki cikawa mutane kunne da kakari?"ba yau ta soma gani ba balle ya dameta,saidai idan taga dama ta rama wani lokaci kuwa tayi banza da ita,abu daya ke damun su'ad shine yadda wani lokacin take vcin karo da zallar kulawa da sumayya ke samu daga wajen almustapha,tarairaya da damuwa,kalar wanda taci burin yayi mata koma fiye da haka,abu daya kawai ta sani shine indai sai ta dauki wannan kayan wahalar to kuwa ba zata samu wannan abun na,jira kawai take sumayya tayi nauyi kota haife,ta tabbatar a sannan duk wata gayya zata watse.

       Ko daya sumayya bata bari laulayinta ya hanata yin duk abinda ya dace ba,saidai abinda ba'a rasa ba wanda dole ka gaza saboda sauyawar yanayi,a hakan ma takan faki idanun almustapha ne ko,idan baya nan,idan kuwa ya dawo kaman yayi kuka,takan sanya dariya tace
"amman dai kai likita ne,ku kuke bawa matan mutane shawara su dinga motsa jiki sanda suke da juna biyu ko?"cafkota yake ya hukuntata son ranshi,ba hukunci na duka ko zagi ba hukunci ne zallar qauna.

       Ummi taso daurewa amma ganin dukkansu ba wanda ke da niyyar sanar mata komai bayan raga dukka wasu canje canje da suka wajaba ga mai ciki,randa ta gaji ta tsare sumayyan tazo gaidata da safe,kunya ta kamata,ta sumkuyar da kai,kamar zata nutse haka take ji,murmushin farinciki ummu ta saki tana furta alhamdulillah a fili kafin tace
"shine kika biye masa amiran umman khalipha zaku boye mana?,kyaci gidanku"itakam kunya take ji,don ko anty dije ta kasa gaya mata,da yake kwana biyu basanan sunyi tafiya ita da yara da mai gidan baki daya bikin 'yar qanin babanshi dake bauchi,kuma sun dan jima a can shi yasa ko rashin lpyr bata sani ba,zaunar da ita ummi tayi ta dinga zayyano mata dukkan wasu dabaru na kula da kai da ciki,ta kuwa qaru sosai,ummi tamkar ta jawo dare yayi haka takeji don wannan kyakkyawan labari ya isa ga kunnen baba prof.

        Yana zaune baban yana shan fura,jifa jifa yakan daga kai ya dubi ummi dake zaune gabanshi,ba don ya qoshi ba ya ajjiye mazubin yana dubanta
"Fadi kawai abinda ke bakinki....ummin su adam yau tunda na shigo naga bakinki nata motsi,tunda naga hakan nasan akwai magana sarauniyar miskilanci yau zan sha labari" murmushi ta saki,har yau baba bai daina tsokanarta ba,bai daina tuno mata gamonsu ba akaron farko wanda shi ya zama silar wanzuwar alaqar mai albarka dake tsakaninsu a yanzu
"Babban albishir ne wannan,bai kamata na baka shi haka ta sauqi ba me zan samu" murmushi yayi ya maida bayansa jikin kujera
"A'a a'ah,bazan fada ba sai naji girman albishir din tukunna"
"Kasan girmansa kuwa?"
"Har yakai na ganin sule na?"
"Yana da alaqa ai da sulen naka" jin ta ambaci sulensa ya sanya shi gyara zamanshi
"Wanne irin albishir ne haka zuwairiyya gaya min"
"Mun samu qaruwa fa agidan nan?" Dubanta yayi
"Ke ko maamaa?" Dariya ta saki yana toshe bakinta
"Kai.....haba prof..rufamana asiri don Allah,muna haihuwa surukai nayi....mamanka ke da juna biyu?"
"Maman tawa biyu ce ai wacce?"
"Mai dakin almustapha" daukewa wutar baba tayi kafin yace
"Allahu akhbar!,Allahu akhbar!!,kilishi.....da gaske kike ko da wasa,kada fa ki sani nayi abun kunya" dariya sosai ta dinga yi masa ganin yadda ya diriri ce
"Ta bakinsu nima naji,dama na jima ina zaton haka"kabbara hamdala da hailala baban ya dinga saki,tammat burikansa sun cika a rayuwa,Allah yayi masa baiwa ba shakka,a take ya daura alwala yayi sallah raka'a biyu ta godiya wa ubangiji,kallonshi kawai ummi take,gani take kamar yama fita jin dadi qwarai nesa ba kusa ba.


Daga daya bangaren sumayya ke fitowa daga bandaki bayan tayi wanka saboda kwanciya,wankan da bata samu yi ba sai a lokacin,ta hada har da kanta ta wanke,saboda sam ta tsani zuwa salloon,tunda almustapha ya taba gyara mata a gida taji tafi son nashi,yana zaune saman gado yana aiki kan system,fitowarta ya ja hankalinshi,ya daga kai yana dubanta,tayi kyau cikin rigar bacci,tana gaban mudubi tana daukan mayuka da hand drayer dinta ta zo dab da gadon ta jona ta sannan ta miqe,ta daga kai suka hada ido da shi,kusan ta saba da irin wannan kallon daga wajen almustapha,abun mamakin kuma idan suka fita sai ki wuceshi baima san dake ba,hakanan bai fiya gane mata ba,amma batasan ya akai ya koyi irin wannan kallon haka a kanta ita daya ba,iska ta hura masa a fuska suka saki murmushi tare
"baka sanni bane?"
"Kullum sabuwa kike koma min,daga zuciyata har idanuna,i dont know why?,ko kin iya sihiri ne?" Murmushi ta saki tana juya ido
"Yessss....tunda har na iya sihirce zuciyarka" kai yake gyadawa yana qaramar dariya
"Na yarda kam,tunda gashi kin hana mu koma wajen aiki....amma in sha Allah next week zamu wuce dubai baki daya,kinga...sai munfi sakewa ko?,saboda ina buqatar kulawa sama da haka gaskiya" fara'ar fuskarta ce ta ragu,baki daya taji baga qaunar sake komawa garin,duk da taji yana maganan gidanshi zasu wuce,amma tana ganin gwara kawai ita ya barta nan ya wuce da su'ad ita taji da kanta,system din ya ture ya amshi drayer din daga hannunta ya zaunar da ita a gabanshi ya soma busar mata da kan
"Nikam ko?,ina ganin kawai da zaka wuce da su'ad ni ka barni nafi son nan" wani abu ya taba zuciyanshi,tana zaton zasu iya raba gari shi da ita?,kwana biyun ma da yake ba tare da ita ba shi daya yasan me yake ji
"Ba haka na tsara ba" ya fada a taqaice,don bai son ta sake cewa komai
"Amma ko don yanayin jikina wai ko?"
"Na fiki sanin hakan ai"
"ina son cikina ya sake......."
"Shut up sumayya,kada ki gayan abinda kike ganin ya dace mana...."ya fada a kausashe.







*mrs muhammad ce*👑

📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖


*~NA~*

*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*

*WATTPAD:HUGUMA*

*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)



9⃣6⃣

*Bismillahir rahmanir rahim*

*wata rana annabi S A W yazo wucewa ta wasu* *qaburbura guda biyu,sai yace da sahabbansa*
*"haqiqa(mutanen dake cikin kabarin) ana musu azaba,ba kuma wani* *babban abu bane yasa ake musu azaba* *saidai(ma'abocin kabari daya)ya kasance baya suturtuwa daga fitsari,amma dayan* *SHI KUMA YA KASANCE YANA YADA ANNAMIMANCI"*

*sadaqa rasulul karim*

*qalubale ga munafukai,qalubale ga masu daukan zantukan wancan bangare su kaiwa wancan,su dauki naka su kai wa wani bangare,qalubale ga masu haddasa husuma,masu qiren qarya don su haddasa husuma da rigima tsakanin mutane,qalubale a garesu baki daya,GA MAKOMARKU NAN,RUWANKU KU GYARA RUWANKU KUCI GABA*

*FITINA AKWANCE TAKE ALLAH YA LA'ANCI MAI TADA TA*

*FADA CE TA MA'AIKI*

*ABINDA KUKA SHIRYA BAI YIWU BA,SAIKU SAKE SABON SHIRI,NI DA MAMUHGHEE DUKA BA JAHILAI BANE,MAIMAKON SHARRI DA KUKA SO QULLAWA SAI ALLAH YA JUYA ABIN YA ZAME MANA ALKHAIRI,GODIYA TA TABBATA GA ALLAH*

*ubangiji na cewa*

*YAKU WADANDA KUKA BADA GASKIYA DA ALLAH,IDAN FASIQI YAZO MUKU DA LABARI,TO KUYI BINCIKE KADA KU AFKAWA WASU MUTANE CIKIN JAHILCI/RASHIN SANI,SAI KU WAYI GARI KUNA MASU NADAMA AKAN ABINDA KUKA AIKATA*

*HAQIQA DUK WANDA YAYI AIKI DA UMARNIN UBANGIJI BA ZAIYI DANA SANI BA,MUN GODEWA ALLAH DAYA SA MUKA KASANCE CIKIN MASU IMANI*

*ALLAH KA SHIGA TSAKANINMU DA SU,KA FI KOWA SANIN BAMA NUFIN KOWA DA SHARRI,TSARKAKE ZUCIYARKA SAI ALLAH YA KUBUTAR DA KAI*

*muna muku fata Allah ya shiryeku,don wannan mummunan ciwo ne kuke dauke da shi,ciwon dake iya dawwamar da bawa cikin azabar kabari*

*ALHAMDULILLAH*
_______________________________________






           Shiru ne ya ratsa dakin,bata sake cewa komai ba,kamar yadda shima bai sake cewa komai ba har ya gama mata gyaran ya hade mata shi waje guda,tana kwance lamo tunani kala kala cikin zuciyarta,har ga Allah bata marmarin binsa,ba don komai ba saboda ta horu cikin abdallah,tana tsoron sake faruwar wani abun,su da zasu tafi can wata qasa wata uwa duniya,wazai tallafeta idan wani abu ya sameta wanda bata fatanshi?,shi da ba zama yake ba,ko yaushe aiki aiki?.

         Washegari ya sake birkice mata,sanda suka je gaida su baba da ummee,ya sanar musu komawarsu ranar lahadi kwanaki uku masu zuwa,ita dinma ummen so take ya barta nan cikin ya sake qwari tukunna,baya ga haka tana tunanin haukar su'adah kada ta yiwa sumayya saukarsa,tun sanda ta yanki almustaphan take jinjina batun,dannan daga bisani itama tazo raiwa kanta illa,to wayr ba zata iya yiwa ba kuma?,hakan ya sanya kamar tasan zaizo da zancan tafiya ta gayawa baba shawararta,yayi na'am da hakan,don shi kansa tsarin yayi masa,ya wuce da su'ad din ya bar sumayyan bayan wata biyu yazo ua dauketa.

       Sanda ummee ke rattabo masa bayanin kanshi na wasa,kusan tare suka daga kansu gaban sumayya na faduwa,kada fa yayi zaton qararshi ta kawo kan ba zata bishi ba?,da hanzari ya daga kanshi yana duban ummee,a hankali ya motsa bakinshi
"Amma ummee nan da can din duka daya ne ai,zata samu dukkan kulawar data dace"
"Ba daya bane almustapha,ka barta nan ta sake koyon yadda zata kula da kanta,a can fa kada ka manta bata da kowa..."
"Amma ummee tana da ni" ya amsa ummin bako kunyar nan fuskarshi,hankalinshi a tashe yake,kawai yadda zai tafi ya barta yake kwatantawa,ji yake sam ba mai yiwuwa bane
"Munsan da kai din ai,awa nawa kake zama a can din....kaga...magana ta wuce tashi ka tafi,kada ayi visa da ita" a hankali ya miqe bai ko dubi sashen da take ba,duba daya zaka yiwa fuskanshi kasan yana cin fushi,ya juya a nutse ya ficea binshi,binshi tayi da idanuwa kamar zata sanya kuka,bacin ran data gani kawai saman fuskarshi ya daga hankalinta
"Amirah" taji ummi na kiran sunanta,da sauri ta maida hankalita wajen tana amsawa
"Kada ki damu kinji,rabu da shi,ciwon 'ya mace na 'ya maca ne,kina wannan halin na yau lafiya gobe babu ta yaya zaki tafi inda baki da mataimaki sai Allah,qyaleshi ko yayi fushi zaya sauko,ni nasan bazai iya fushi dake ba" maganan ummin ta qarshe ta bawa sumayya kunya,sai tayi qas da kanta tana amsawa da to,duk da haka zuciyarta bata nutsu ba.

       Sallamar amira kamar wadda aka jefo ita ta katse maganan da ummi ke gaya mata,da gudunta ta kwaso bata zube gaban kowa ba sai sumayya,ruqunqumeta tayi tana cewa
"Wayyo matar yaya na,kin biyamu wallahi,Allah jiya kasa bacci nayi,labarin yazo mun katsam,anty farida ce ta gayamin,sai naga gari kaman da gangan yaqi wayewa don kada nazo na ganki" kunya ta kama sumayya,zungurinta take kan tayi shiru amma ina amira ma ba fuskantarta take ba,ganin yadda kunya ta kama sumayya ya sanya ummi miqewa tsam ta basu waje,ummi na fita ta dalawa amiran duka a cinya,wajen take sosawa tana dariya
"Ba komai,wallahi koda zafi ni banji zafin ba,bakya laifi ai ko kin kashe dan su'ad" dariya suka bushe da ita baki dayansu sannan sumayya tace
"Kefa iskancin naki ma naga sabon lasisi kukaje ke da saifu aka yi masa,antyn take ma kin daina anty saidai su'ad gatsal,ke kin isa ki kashe mata daa ba sai tayi gunduwarki ba" dariya ta sake saki harda tafa hannu
"Wa ya gaya miki son 'ya'yan take,ai ni tuni na san da wannan.....ke mubar zancan waccar.....amiran umman khalipha da gaske anty farida take?"
"Shafa kiji" ta bata amsa tana hararta,dariya ta saki
"Ai wlh duk wanda ya kalleki yasan da magana.....amma fa kin rame da alama kina shan jiki....Allah ya raba lafiya,kai Allah ya nuna mana wannan rana,zamu karya qugu da kwankwaso"
"Ki komawa saifu a gurguwa ko?"
"Ba komai sai ayi maleji......can na gano mai dakin naki"
"Amira baki da mutunci,waye mai dakina"
"Waye banda yaya maan,waishi kuwa har yau bai daina wannan shegen dacin ran nashi ba,na gaidashi ko amsani baiyi ba ya figi mota ya fice kaman wanda aka yiwa dan banzan duka?" Shiru sumayya ta danyi,wato a fusace yake kuma cikin fushi ya fita kenan
"Ranshi ne a bace amira"
"Haka kullum yake"
"Malama ki kiyayi zagarmin miji a gabana......" Ta fada tana hararta,dariya ta saki sosai harda kwantawa qasa
"Ikon Allah....yau da bani da aure da nasha haushi,gayamin me akayi masa"
"Anqi din" ta fada tana tureta
"Habba....nice fa ta hannun daman" ta fada tana lallashinta,sai data ga dama don kanta sannan tace
"Dubai yakeso mu koma ni shi da su'ad,daren jiya nace mishi su tafi ni sai cikina ya dada qwari zan taho,ya nuna bai amince ba,yau ummi tace masa ya barni a nan,kaman yadda jiya nace masa.....amira zaiyi tunanin na kawo qararsa ne"
"Dai dai kenan....kina zaton a barki cikinki bai qwari ba kibi waccan mai qirar amurkawan ta murqushe mana baby?,sai jikinki yayi qwari yadda baki buqatar mataimaki....ya almustapha kuma qyaleshi,tunda ummee ta fada haka dole zai haqura" shiru tayi tana nazari,kusan maganarsu na kan hanya,ba yau tasan mugun halin kishiya ba,ita sam bata ma yadda da yadda su'ad ke nuna cikin ko a jikinta ba bai dameta ba.

        Fitowar ummi ta sanya amira miqewa ta daneta tana cewa
"Ummina,i missed you"
"Nikam bansan me yasa saif ke biyewa shirmenki ba,duka duka yaushe kuka zo gidan nan wai?" Rai ta bata tana janyewa
"Wai ummi nufinki tun yanzu kin fara gajiya da ni,kinsan bazan iya zama ba banzo naga matar yaya ba,qaruwa fa muka samu" ta fadi tana maida kallonta gun sumayya data kauda kai tana mata dariya
"Gaskiya ne,kun kyauta ai" ta fadi tana zama amiran ta zauna tsakaninsu suna gaisawa.

        Kusan nan ta wuni saboda ba ranar kwananta bane bare ta koma gida aiki,zuwan amiran ya debe mata kewa sosai,sunsha hira kaman ba gobe,abinda bata sani ba shine,dawowan almustapha gida uku yana dubata ya tadda bata nan,abinda ya sake qona masa rai kenan,gani yake ita ta kai maganan wajensu ummi,abinda bai duba ba shine daga daren har wayewar gari suna tare baiga ta fita ba,ta ina zata iya kai qararshi.

         Sai bayan magarib ta baro bangaren,a sannan yana saman dining zaune da niyyar cin abincin dare,ya tasa abincin ne kawai a gabanshi,abu goma da ashiri ,ko kusa baya son abincin kuku,sannan ga damuwar sumayya a gefe guda,da sallama ta shiga falon,yana daga can saman dining,binta yayi da kallo cikin bacin rai ba tare da ya amsa sallaman ba,tun kayan safiya ne a jikinta abinda bai taba gani ba,hali take so ta sauya?mema taci wunin yau bayan yasan banda nama saiko shinkafa 'yar kadan take iya sawa cikinta,magungunan ta na yau ya duba baki daya ba wanda tasha,tana dab da shiga balcony da zai sadata da dakunan baccinta ta jiyo dakakkiyan muryarshi a atsawace yana kiran sunanta,hanjin cikinta ya kada ta runtse idanunta kafin ta waiwayo
"Daga ina kike?"daga kai tayi ta dubeshi don maganar ta mata banbarakwai,yana zaune ya hade hannayensa cikin na juna yana dubanta
"wajen.....waj....ummi"ta fada cikin dan daburcewa,sai ya miqe tsaye yana zuba hannayenshi a aljihun wandonshi ya dan tako kadan zuwa bakin step din dining din
"Ba sai kinyi haka ba zaki nuna baki qaunar kasancewa tare da ni,duka ba wannan ce damuwata ba...me kika baiwa babyna yau?,....tsaftar jikinki wanda


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login