Showing 30001 words to 33000 words out of 364327 words
ya qarasa gefan gadon ya tsaya,duk da cewa ransa a matuqar bace yake,ji yake kamar ya janyo fa'izan ya yi mata dan banzan duka ya watsar amma sai ya dake
"Fa'iza,me yasa ba zaki bar yaya ta zauna dakinki ba,ai ina ganin bai kamata ba" hura hanci take tana tunanin ko yanzu mukhtar ya soma tsoronta,inko haka ne kowa tasa ta qare,tabbas sai kowa ma yaci ubansa cikin gidan
"Mukhtar banga dama bane,bari kaji" ta fada tana miqewa zaune kan gadon
"Na farko bansan sa ido gaskiya kuma na fuskanci su sun fara koyar wannan halayyar,na biyu na fuskanci ni aka rainawa wayo,ga mai daki ciki da falo can ba'a dosheta ba saini mai daki daya kamar zuciyar talaka" ba qaramin dukansa maganar tayi a zuciya ba amma ya hadiye don so yake ya jata aje gun ta dora da
"Saboda haka su nemi gurin kwana don ni bazan zauna da wadan nan qattan a daki na ba" wani qullutun abu ne ya tokare masa wuya qanda ya hanashi sake magana,sai yaya yahanasu da tace
"Haba ke kuwa fa'iza,kwana nawa ne duka duka mun koma gidanmu,ai ban zaci ko wani na turo gidan nan ki masa sauki a dakinki ba zaki kasa,kada fa ki manta nice silar zuwanki gidan nan" zabura tayi tana dakatar da ita
"Kinga kada ki sake kice zaki mun gori,don ke kika kawoni gidan ai bake kike aure na ba,buqatar maje haji sallah kuma da taku buqatar ai ba haka siddan kika kawoni ba,sabida haka kuje ni don Allah kada ku cikan kunne,tunda kun nace sai kun zauna a dakin kuje zanyi tunani,ko kwana daya ne kuyi kafin ku koma inda kuka fito".
Ba qaramin daurewa kan yaya yahanasun yayi ba da kalaman fa'iza,duk yadda fadima ke gaya mata sai yau ta sake tabbatarwa da lamba daya ce ita wajen rashin mutunci tsiya da tsiyataku
" fa'iza ni kike gayawa haka"kanga tsaye babu kunya tace
"Na fada din,ke kike aurena ne nace wai kawai da zaki takuran,wannan fa kamar kina lissafin sau nawa nake kwanciya da mijina ne"tuni maganar ta sake dora yaya yahanasun kan dokin zuciya
" ke qaramar mara kunya,ko bani nake aurenki ba kinsan ina da power din da zan sa ungulu ta koma gidanta na tsamiya ko?"
"Bismillah,sai mu gani " ta fada tana murguda baki gami da turo daurinta gaban goshinta ta dage kanta idanunta na kallon ceiling din daki.
tabbas tana jin yau idan bata nunawa fa'iza isar da take da ita a wajen mukhtar ba bata huce takaici ba,idanunta taf da bacin rai ta dubeshi
"Mukhtar,ina so a yau yau din nan ka sawwaqewa fa'iza,yanzun nan" ta qarashe cikin daga murya.
Duk da cewa ranshi ya kai qololuwa wajen baci kan abinda fa'izq ta yiwa yaya yahanasun amma sai ya danne komai tamkar bai b'aci ba,ai dama duk wanda ya sai rariya yasan zata zub da ruwa,to ya kamata yaya yahanasun taga yadda tata rariyar ke zubar da nata ruwan,ruwan kuma da baiyi qasa a gwiwar malalowa ya jiqata sharkaf ba,kai ya kada sannan yace
"Kan me zan saki fa'iza yaya,ni babu abinda ta yimin,hasalima fa'iza ai zabinki ce,kinga bai kamaci na wofantar da ita ba,zan riqeta hannu bibbiyu kamar yadda kika umarceni" tsawa ta daka masa
"Mukhtar,kai makaho ne?,ko kuwa kai kurma ne,baka ganin abinda ta yimin ne,ni na umarceka nace ka saketa kamar yadda na umarceka ka aureta a baya" kai ya sake kadawa tare da yin tattaki don barin dakin yana cewa
"Ki gafarceni yaya,amma yanzu na fara zama da fa'iza,don ni bata aikata min komai ba" sai ya fice abinsa ya barsu ana kallon kallo.
Kira ya qwalawa sajida ya sanyata suka dinga jidar kayayyakinsu yana tayasu suna kaiwa dakin sumayya wadda ke zaune kurum tana ji da ganin sarautar Allah,sai da suka kammala tsaf yaya yahansun na dakin fa'iza suna cecekuce,ganin abun na sake qamari ya sanyashi shiga dakin ya janyeta yana fadin
"Kiyi haquri yaya yahanasu,kizo ku zauna dakin sumayya tunda itan da kuke so ta qiya" sai ta waiwayo ta bishi da ido galala tana kallonsa,mukhtar din da baison bacin ranta?,mukhtar din da baiso a tabata amma yau an mata cin kashin data jima rabon ta da irinsa amma ya kasa cewa uffan,kardai mallaka fa'iza tayi masa wadda baya iya qetare umarninta?,ranta ya shiga suya ta shiga fatar cewa Allah yasa ba haka bane,bata da wani zabi a yanzun illa ta bishi,idan yaso daga bisani tayi tunanin mafita a tsanake.
Bayan sun shiga dakin ta zauna sannan ya kira sumayya ya fice zuwa dakinsa.
Zaune ta tadda shi dafe da kansa,a hankali cikin kasala ta zauna gefansa,ta sanya tafin hannunta tana shafar bayansa a hankali,tasan fushin mukhtar din,saboda haka ta tabbatar ransa na a bace ne,kusan minti goma baice komai ba kafin daga bisani ya dago ya dubeta
"Sumayya" ya kira sunanta,a tausashe ta amsa sannan ya dora
"Gasu yaya yahanasu nan zasu zauna dakinki,kinsanta sarai ita da yaranta baki daya,baki buqatar muraja'a kansu,na shaideki da haquri wannan halinki ne,to amma don Allah ki nunka haqurinki,baqunta zasu mana na wani d'an lokaci,insha Allah zanyi qoqari na kammala musu gyaransu cikin qanqanin lokaci,idan da na kammala ma gini na sabon gida na can zan ara musu su zauna gudun fitina,kiyi haquri da su don Allah ki sake ninka kawaicinki" kai ta girgiza
"Haba ya mukhtar,ai ba roqona zaka yi ba,umarni kadai zaka bada,da kai da kaya ai duka mallakar wuya ne,nima yaya take agurina,insha Allahu babu wata matsala ko damuwa"
"Na gode,Allah yayi miki albarka"
"Amin yaya" ta fada tana sakin qayataccen murmushinta wanda har sai da ya sanyashi tsura mata idanu,hannu ta turo sautin idanunsa kamar zata tsone masa yaja baya suka saki dariya baki dayansu.
Cikin dakin ya barta ya fita sallah,kasancewar tana faashin sallah sa'an nan kuma dakin nasa na hargitse don fa'iza ba kasafai take tsayawa ta gyara ba ya sanyata tsayawa tana dan kakkabe dakin haka ya dawo ya cimmata,kafin ya kai ga zama fa'iza ta fado dakin hannunta riqe a qugunta,shi ya fara cewa
"Me aka girka" ran nan nashi a hade tsaf wanda ita a nata zaton aikin da take kansa ya fara tasiri,saboda haka kanga tsaye tace
"Yau duka ma banyi girki ba wlh a gajiye nake" ta fada tana yatsina,sam ya tsaneta har yau ya kasa jinta dai dai da qwayar zarra cikin zuciyarsa,bata dameshi ba dama bisa lalura kawai yaje rabarta,qoqarin adalci ne kawai irin nasa tunda ta riga da ta rataya a wuyansa bisa alfarmar igiyoyinta uku dake hannunsa.
Hannu ya miqa mata a daqile yace
"Bani muqullan locker din kayan abinci na" ba musu ta fice don dauko masa,ya juya ya dubi sumayya
"Yau ba'ayi girki ba gida na,me kuka bawa yaya taci ita da iyalanta?" Kanta ta duqar qasa sannan tace
"Ka mance na tambayeka zani kitso?,tunda na fita ban samu na dawo ba sai bayan la'asar,dana shigo kuma nima yadda ka taddasu haka na taddasu" kai ya gyada ba tare da yace komai ba,ta dawo da muqullin ta miqa masa,kai tsaye ya danqa su ga sumayya
"Jeki ka samar mana da abinda zamuci" hannu biyu tasa ta amsa kana ta danyi jim,da kamar taqi abinda ya sata din,sai kuma taga hakan bai dace ba,idan bai isa da fa'iza ba ita ai ya isa da ita,miqewa tayi zata fice fa'iza ta saki wani mugun murmushi,ga zatonta sumayya ta shiga cakwakiya mukhtar zai soma azabtar da ita kenan,fadawa tayi saman katifar kusa da shi tana fadin
"Ammmmm......idan kin gama kizo na gaya miki me mi kuma zaki dafamin" wannan karo kasa hadiye takaicinsa yayi sai da juyo yace
"Da yake baiwar gidan ubanki ce ko,wato saboda kinga na miki shiru ne ko......hmmmmm.....ki kiyayi ranar qin dillanci wallahi,wuce kije sumayya",sai ta juya ta fice din,itakam ta ma rasa na cewa gaba daya,gaban fa'iza ya fadi,kaddai jiya i yau ne dai mukhtar din,sai ta kasa hadiye qanin zagin da yayi mata ta miqe tsaye
" wacce rana ce ranar qin dillanci,ba ranar da hajar mai gari ta bata ba?,idan ba'a ganta a gun fa'iza sai me?"ta murguda baki tana niyyar ficewa,zuciya ce ta ciyoshi ya miqe cikin zafin nama ya fincikota ya zabga mata wani lafiyayyen mari,a gigice ta dafe kuncinta don bata zaci haka ba,karo na farko da mukhtar din ya soma taba lafiyarta,ashar ta danna sannan tace
"Ni ka mara muntari,kayyasa kace yau da bala'i,wallahi baka daki bulus ba sai na rama" .
Daga hannunta tayi da niyyar kaiwa fuskarsa mari ya cafe hannun tare da murdeshi har sai ta qashin hannun ya bada wani qasss da alamu ya targadata,tsananin azaba ya sanyata sakin qara wadda ta sanya sumayya dake kitchen barin abinda take ta taho dakin cikin hanzari,dadin da taji data lura su yaya yahanasun da suka qure kallo cikin t.v dinta basu san me ake ciki ba,tun fara masa rashin kunyar duk cikin kunnenta ne saboda muryar fa'izan na sama ne sosai.
Sanda ta isa dakin ya daga hannu da niyyar sake bata wani marin,cikin hanzari ta shiga tsakiyarsu taba riqe hannunsa,cikin taushi ta langabar da kanta tana duban tsakiyar idonsa wanda hakan shi ya karya lagonsa,ya zare hannunaa daga nata,bakinta bai mutu ba sai data wurga masa kalmar
"Wallahi wallahi sai kayi dana sanin dukan fa'iza,sai ka biya farashin duka na da kayi,zaka gani,ke kuma ku zuba mu gani" sannan ta fice.
Tabbas ba don har tanzu bai cimma qudirinsa ba akanta da yau babu abinda zai hanata kwana cikin gidan ubanta,gefensa ta zauna ta sanya hannunta cikin nashi sannnan tace
"Sam hakan ba girmanka bane ya mukhtar,tunda nake ban taba gani ka daki wani ba ma bare matarka ta aure,yin hakan ba daidai bane,na roqeka don Allah kada ka sake sai ka fara bani tsoro ai" ta qarasa fada a shagwabe,sai ya dago yana dubanta da murmushi,take kaso saba'in cikin dari na bacin ransa ya zabge ga fadi sai ya dora hannunsa shima saman nata
"Banaso ki fara jin tsoro na sumy ta,idan kika fara tsoro na na zauna da wa?,bazan sake ba,kiyi haquri" kai ta girgiza tana murmushi
"Kai ya kamata nace kayi haquri yaya ka yafe mana,yau mun sanyaka cikin bacin rai" kasa magana yayi sai ua rungumeta kawai cikin jikinsa yana jin duminya,yana ganin girma da qimar wannan halitta mau tsananin hankali da biyayya a gareshi,shikam mai zai hana shi faranta nata matuqar yana da iko?,me ya isa ya hanashi sonta a duniya?,babu shi,babu shi ko mene,koda QADDARA ce baijin tana da wannan qarfin ikon,baya fata ma QADDARAR tazo masa ta wannan sigar,gwara ta kowacce siga amma banda wannan,wala'alla ya iya jurewa.
Sai da suka fara jiyo qaurin girkinta sannan ya saketa ta miqe da hanzari ta fice tana ce masa tana zuwa.
*mrs muhammad ce*
📚📚📚📚✍✍✍✍
✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
1⃣7⃣
________________________
*Bismillahir rahmanir rahim*
*ma asaba min musibatun fil'ardi wala fi anfusikum illa fi kitabim min qabli an nabra'aha*
_______________________
Cikin mintuna qalilan ta kammala jallope din taliyar ta rarraba cikin coolers,mukhtar din ta fara kaiwa,tana niyyar juyawa ta fita yace da ita
"Wannan cooler din fa na waye?" Ta dubi cooler din sannan ta dubeshi
"Na fa'ixa ne a ciki"
"Ajjiye a nan" ya fada yana gwada mata inda zata ajjiye din da idonsa,bata kawo komai cikin ranta ba ta ajjiye din ta nufi dakinta.
Can ta taddasu sun baje suna kallo,duk da cewa kallo daya zaka yiwa yahanasun kasan tabbas har yau ranta a bace yake,ta dire cooler din tana cewa
"Ga abincinku yaya" wani banzan kallo ta watsa mata
"Eh zamu ci ai kuma zamu ambaci sunan Allah,in sha Allahu babu abinda zai samemu,makira,idan ma shiga kika tsakaninmu da fa'iza har take wannan tashan rashin kunyan to ni zanyi maganinku ke da iyan baki daya" kai ta kada ba tare da tace komai ba ta shige uwar dakinta,ta tube kayanta ta sauya na bacci,sai tayi zamanta gefan gado ta janyo RIYADUL JANNAH littafin addu'o'inta da malam ya bata wanda bata rabi da shi ta soma duba wasu shafuka.
Sumayyan na fita ya dauki cooler din baki daya ya fita da ita waje,wasu almajirai da rabonsu ya rantse ya samu qofar gida zazzaune ya basu,take suka karba suka rabe a tsakaninsu suna zabga godiya banza ta faadi garesu.
Yana kammala rufe gidan sukayi karo da fa'iza wadda ta dawo daga dakin sumayya ta bankade labulenta ko kallo su ya yahanasu basu isheta ba ta qwallawa sumayya tambayar ina abincinta,tana daga cikin dakin ta gaya mata yana gun yaya mukhtar.
Dubansa tayi"ina abinci na?"banza ya bawa ajiyarta yayi wucewarsa,sai ta bishi da kallo,bata haqura ba tabi bayansa tana sake tambayarsa,wani wawan birki yaci wanda sai da ya sanyata ja da baya
"Baki daku ba kenan ko?,tare muka hada muka siyo abincin?,ko kinzo da bayi ne daga gidanku?,uban wani ne ya hanaki dafawa kici,ki fice min daga nan tun kafin na hasala na sake kikkifa miki mari" tana qunquni ta juya ta fice ranta qunci fal,ga uwar yunwar dake sakadarta,abinka da mutum mai shegen ci ta riga da ta saba.
A tsakar gida taci karo da jamila na wanke hannunta,da gayya ta bangajeta tayi taga taga ta fadi,sai ta miqe kuwa ta lailayawa fa'izar ashar abinka da itama tana ji da tata rashin kunyar,ai kuwa fa'izan tayo kanta zata huce bisa kan nata,dai dai sanda yaya yahanasu ta qaraso tayi hanzarin riqeta ta gabza mata mari dama tana ciki da ita ne,tana waiwayowa kuwa ta cakumi wuyan yaya yahanasun take jamila ta shigarwa uwarta nan fada ya kaure tsakanin su ukun.
Sumayya ce ta fara fitowa,cikin tashin hankali taje dubansu idanunta a waje,dambe da yaya yahanasu?,tab,lallai fa'iza ta kai,dakin mukhtar ta nufa da hanzari tana mamakin me ya hanashi fitowa,ga mamakinta yana tsaye bakin window yana kallonsu,saidai idanun nan sun kada sunyi jazur,a hankali ya juyo ya zuba mata su,itama sai jikinta yayi sanyi,tausayinta ya kamashi,babu shakka wata jarrabawa ce ta fado rayuwarsu,idanunta suka cika taf da qwalla ta tausayin mijin nata,sai kawai ya saki labulen ya taka a hankali ya fita tsakar gidan,wata gigitacciyar tsawa ya sakarwa fa'iza dake tsakiyarsu tana cin na jaki wadda tsawar sai data sanya hanjin sumayya hadewa ya cure guri guda,ta runtse idanunta tana jin ruguginta na ratsa kunnanta.
Nuni kawai ya yiwa fa'iza da hanyar dakinta yana mata wani irin kallo mai cike da tsana,ba musu ta wuce jikinta na rawa,ya juya ya dubi yaya yahanasu sai kawai ya kamata yayi dakin sumayya da ita.
Bakin rijiya ta zauna,sai ta kasa daurewa idanunta ya shiga fidda qwalla,wannan wacce iriyar masifa ce lokaci guda,duk wani farinciki da zaman lafiya na gidansu yayi qaura lokaci daya?,tana share hawayen idanunta tana tausayin mukhtar dinta.
Tana zaune a nan mukhtar din ya fito ya shige dakin fa'iza,a nan ne ta jiyo tashin muryarsa saidai nan din ma bata ji duka abinda yake fadi ba,daga bisani ne ya fito,ta miqe tsaye ta isa gabansa tana kallonsa,tabbas taso ace yau ranar girkinta ne,ta lallashi mukhtar din,saidai sam bata da wannan damar,karyar da kai tayi murya a tausashe tace
"Kayi haquri don Allah yaya mukhtat,komai na duniya mai wucewa ne,jarrabawa ce daga Allah" murmushin qarfin hali ya saki ya shafi gefan fuskarta
"Babu komai my sumy,kije ki kwanta,kuma ban lamunce ki sanya abun cikin ranki ba,ki kwanta kiyi bacci sosai" ya sanya bakinsa yayi kissing goshinta,sai ya bata kunya har ta dan murmusa,yana tsaye har ta wuce dakinta sannan ya juya nashi.
Ko da ta isa dakin tuni ta taras da su sun rarrashe kan gadonta,sai yaya yahanasu dake zaune gefan gadon tana huci,abinda take da buqata ta dauka zata fice taji sakin qwafar da yaya yahanasu tayi,ranar kan doguwar kujerar falo ta kwana,saidai tayi qoqari kamar yadda mukhtar ya buqace ta tayi bacci ta qoqarta tayi na 'yan awowi.
*******************
Cikin kwanakin gaba daya mukhtar ya fita harkar fa'izan duk da cewa daman can ba shiga yake yi ba,saidai duk wani abu da yake haqqinta ne kansa yana sauke mata bakin gwargwado.
Zaman yaya yahanasu a gidan ya dauki sabon salo,wani irin zama ake a gidan,sosai yaya yahanasun kejin haushin fa'izan gami da ganin baikenta tun farko data daure gindin dan uwanta ya zama miji gareta,sai dai kuma duk da wannan bai hanata jin haushin sumayya ba,gani taje tamkar itace ta shiga tsakaninsu.
Duk kwanan duniya gari na wayewa da zarar mukhtar din ya sanya qafa ya fice itama fa'izan ke ficewa,ba zata dawo ba sai yaba gab da dawowa koda kuwa ranakun girkinta ne,sai a sannan zata tsiri girkin dare shima tsoron hukuncin mukhtar din ya hau kanta take,ba qaramin horata yayi ba lokacin da ya amshi maqullin locker din abincinsa daga hannunta ba,da rana kuwa saidai kowa tashi ta fishsheshi,shiga su jamila suke kitchen kansu tsaye su girka duk abinda suka ga dama,su din ma ba baya bane wajen iya barnar abinci da ta'adi,sam ko sau daya sumayyan bata taba daga kai ta dubesu ba bare ta gwadawa mukhtar abinda sukeyi cikin gidan,dakinta kam tuni ta sallama musu shi,ta dauke kai baki daya da shi saboda yadda suke abinda suka ga dama cikinsa,wani abun da gayya da gadara suke mata,koda bata tankasu ba sukan bude baki suce "kayan dakin da kudin dan uwansu aka sauya su" sau tari dariya abun yake bata,ta kuma godewa Allah da ya sanya iyayenta masu rufin asiri da zuciyar yiwa iyalinsu ne,suma sun san da haka,babu shakka da Allah kadai ne yasan halin da zata tsinci kanta ciki,hatta da kayan sawarta sai suka fara dauka dai dai da dai dai suna sanyawa idan zasu fita wata unguwa ko biki,ranar da mukhtar ya soma gani ransa ya baci matuqa,bai iya