Showing 309001 words to 312000 words out of 364327 words

Chapter 104 - KUNDIN KADDARATA COMPLETE HAUSA NOVEL

HUGUMA   

20 Aug 2024

40094

take riqe da hannunta,yaran baki dayansu sanye suke da qananun kaya,sam gori da rashin mutuncin fahariyya bai hana anty ni'imah riqon 'ya'yan tamkar ita ta haifesu ba,bugu da qari ya adam din tsayayye ne a tsaye yake hakan shi ya sauqaqa tsiya da wariyar launin fata da fahariyya taso koyawa yaran,fuskokinsu ita da sumayya dauke da murmushi suke gaisawa,su hibba suka gaidata suka shige kitchen kiran ummi,murmushi ni'imah ta sakeyi tana duban sumayya
"Sannu anty amarya(yadda yaran sukan kirata wani lokaci kenan),ashe qaruwa muka samu" a kunyace sumayya tayi murmushi ba tare data amsa ba
"Allah ya inganta ya raba lafiya ya kawo na 'yan baya" nan ma bata masa ba saboda kunya,dubanta tayi
"Ina miki addu'a kice amin wallahi,haihuwa ai babbar ni'imah ce" ta fada wani abu na taba ranta,yanayin fuskarsa ya dan sauya,dubanta sumayyan tayi tana karantar yanayinta,wani yanayu data taba tsintar kanta can baya shekaru biyar zuwa shida a baya ya soma dawo mata,tasan me take ji,ba shakka ba kowanne mutum ke iya fuskantar yanayin da mata irin su ni'imahn ke ciki ba sai wanda ya taba tsintar kanshi ciki,al'amari ne mai taba zuciya da tsayawa a ran dukkan wata diya mace sata tsinci kanta cikin irin wannan jarabawar,sai ta tsinci kanta da kamo hannun ta,ta daga kai suka hada idanu,tuni qwalla ta cika idanun ni'imah,qaqalo murmushi tayi sumayya ta maida mata
"Kada ki damu anty ni'imah,lokaci wataran sai kinga gamkar ba'ayi ba,kinsan na taba tsintar kaina cikin yanayin da yafi naki muni?" Cikin mamaki take duban sumayya,kai ta jinjina mata alamar tabbatarwa
"Kan na samu abdallah na sha wuya anty,ba wanda ya taba tsammatar abdallah zaizo duniya....amma yanzu fa.....kinga kamar ba'a yi ba ko?,to kema kusan hakane in sha Allah"
"Allah ya amsa amiran yaya musty...don yanzu bata umman khalipha bace" ta fada tana qoqarin maida qwallarta tare da jin sanyi cikin zuciyarta da addu'ar da sumayyan tayi mata,daidai sanda ummi ta fito tana cewa
"Wai tafiyar ce ne?"
"Eh wlh ummi" anty ni'imah ta fada cikin girmamawa tana murmushi,qarasowa ummin tayi ta zauna sukayi sallama,sannan ta miqe suja fice sumayya na dagawa su hibban hannu.


Da dare sai ga babbar 'yar anty farida sajida,ummu tasa aka daukota duk don sumayya taji dadin zaman gidan,tunda gidan ya dade babu kowa,sajida akwai hankali nutsuwa da wayo,hakan ya sanya sumayya ta fara jin dadin zama da ita sosai,akwai surutu,a qalla zatayi shekara goma sha biyu,ta nan gidan take tafiyarta makaranta,idan ta dawo sumayya tayi mata qarin karatun addini,tunda a sannan an musu hutun islamiyya.


*Bayan sati daya*



Sha biyu saura na sare tana saman gadonta,sajida na gefanta kwance,tuni ta jima da yin bacci,kamar kullum tunaninsa ke faman yi mata kaikawo cikin zuciyarta,idan har cikin sati gudan tace ta samu walwala ta minti biyu tayi qarya,duk da tsantsar kulawa da take samu daga bangaren mutane ukun nan,ummi anty maamaa da shi kanshi baba prof,tun daga randa ya kira ummi ta sanya dukkan kulawarta kan wayarta ko zata ga kiranshi amma babu shi ba alama,ko saqon tafi da gidanka bata ci nasarar ganin gilmawarsa ba daga gareshi balle kira,kusan sau uku tana jinsa suna waya da ummi amma bai taba nemanta ba,wayar tata ta janyo ta bude tana duban lambobin wayarshi data dauka daga wayar ummi,amma gefe daya na zuciyarta ya hanata kiranshi,akan me ma zata nemeshi bayan shine a haqqu daya nemeta,ya sani ai tana son binsa amma dole subi umarnin na gaba da su,haka taci gaba da juya wayar a hannunta wanda ba jimawa wani zazzafan a mai ya taso mata,tuni ta miqe cikin hanzari,saidai bata kai ga kaiwa toilet ba ta durqushe a nan ta soma kelayashi ba qaqqautawa.


A daidai wannan lokacin almustapha ne zaune bakin system yana aiki,tun yanayi da qarfinshi tuquru har ya soma gazawa,baki daya ta tafi da dukkan wani walwala da karsashinsa,hatta da manya da qananun ma'aikata sunsan walwalar yallabai ta ragu,duk da dama can shi ba mai yawan fara'a bane,amma karsashinsa da son aikinsa cikin kaso dari babu hamsin,hannunshi ya dora saman kanshi yana shafa bayan ya jinginar da bayanshi jikin makarin kujerar,a hankali zuciyarshi ke masa quna,wani bala'in qishirwarta na ratsashi,ji yake a lokacin da yana da ikon komawa tsuntsu ba abinda zai hanashi yin fiffike ya isa gareta,duk wani qwarin qwiwa da burin yin aiki da ya taho da shi babu su duka sun yi nasu guri,duk wani alwashi da yaci na nesantarta tunda bata buqatar zama tare da shi ya ruguje,kwanaki bawaki kacal da baiji ta jinsa yake tamkar wani dabaj cikin jinsin mutane,yanzu haka cikin jikinshi zuciyarsa ke gaya masa idanunta biyu batayi bacci ba,idanunsa ya bude ya janyo wayarsa kamar ko yaushe,ya bude hotonya tun wanda tayi cikin wayar sanda suna dubai da doguwat riga,hotunan da yayi mata a dubai garden glow wanda batasan da su ba,wadanda sukayi bala'in yin kyau,tamkar ta kirata ta amsa,hannunshi ya sanya yana shafar fuskar tata,kewayaen labbanta wadanda idan ya tuna taushinsu tsingar jikinsa ke zubawa,kyakwawan idanunta da kwantacciyar sumarta,tamkar wanda aka bawa aikin zana taswirar fuskarta haka ya dinga zooming yana qare mata kallo,wata wawuyar ajiyar zuciya ya saki tana jin zuciyarshi kamar zata fito waje,ba tare da ya shirya ba ya samu kanshi da yin dialing number dinta,ya zubawa wayar ido yana sauraren jin koda saukar numfashinta ne,saidai wayar harta qaraci rurinta ta tsinke ba'a daga ba.


Sumayyan na zaune dirshan a inda tayi aman tana maida numfashi,ta hangi wayar na haske,saidai ko data miqe ta dauko taga number dinshi ce sai ta maidata ta ajjiye,ranta na wani irin baci,sai yau zaya nemeta,sai yau yaga daman magana da ita?,wato kota mutu ko tayi rai ko?tunda yana da wata matar,zuciyar kishi ta soma saqa mata wannan maganan,hawaye ne ya balle mata wani mahaukacin kishin su'ad na ratsata,ta shiga toilet ta dauko mopper ta gyara wajem fes sannan ta dawo saman kujera ta zauna tana maida numfashi,tana kallon wayar nata fidda haske alamun kira ne,amma saita lumshe idanunta ma ta daina ganin wulgawar haskenta baki daya,hangoshi kawai take shi da su'ad cikin walwala wanda hakan shi ya sanya kenan ita ya bagarar da ita.


Baki daya hankalinsa ya dugunzuma,tunda yake ita ce mutum ta farko a duniya daya taba kira sama da sau biyu,duka shi ba wannan bace damuwarshi,me ya hanata daga kiranshi bayan jikinsa na bashi idanunta biyu?,tun yana zaune har sai da ya miqe tsaye,baisan sanda ya samu kansa yana kiran layin ummi ba ha tare daya tuna cewa dare ya fara nisa ba ko kuma tana wajen baba,cikin tsakiyar baccinta taji qarar wayar tata,dama ba wani nisa can baccin nata yayi ba,gama sallolin nafikarta kenan ta kwanta din ko hijabin jikinta bata cire ba,macace mai yawan tashi dare,bata fiya kashe darenta baki daya wajen yin bacci ba,sunan almustapha data gani ya dan sata faduwar gaba
"Lafiya dai almustapha sha biyu da minti biyar na dare?" Sai a sannan hankalinshi ya koma jikinshi,ya dan gyara muryarshi
"Aaaa.....dama....ba komai...inata kiran sumayyah bata daga bane" ajiyar zuciya ta saki
"Ka sani fa lokacin bacci je yanzu,kuma kasan muhimmancinsa wajen mace mai ciki,ka bari da safe ka kirata ko ita ta kiraka don na tabbata yanzun ta dade da yin bacci,don yau ana gama sallar isha'i taje ta kwanta" gabanshi ya soma faduwa,addu'a yake kada Allah yasa ummi ta tursasashi kan ya bari sai goben,shi kadai yasan me yake ji a qirjinsa game da ita,muryarta kawai yake da muradin ji,Allah yasa ta fahimceshi
"Batayi bacci ba ummi.....don Allah ko zaki hada....." Sai kuma ya kasa qarsawa,nayin ummin yake ji,itama a nata bangaren kasaqe tayi,tausayi irin na d'a da uwa ya kamata,ta tabbata ba zaya samu rabin kulawar da yake samu wajen sumayya ba,tsanin miji da mata sai Allah,kada kuma ta shiga haqqinsa da yawa
"Barin kai mata" cewar ummi
"Yauwa ummi thanks" ya fada cikin wani irin zumudi tare da sauke ajiyar zuciya wadda har sai da ummin ta jiyo,murmushi ta saki tana saukowa daga saman gadon,tasan halin yaronta sarai,tun yana qarami bai iya son abu ba,bai iya sanya abu a zuciya ba,duk abinda yake so bai riqonsa da wasa,hakan ya sanya tun da can baya ta duqufa masa addu'ar samun mace ta gari wadda zata masa yadda yake so ba tare data wahalar da shi ba.



Qofar dakin data ji an turo shi ya sanyata bude idanunta,suka hada ido da ummin sanda ta kunna wutar dakin
"Me kike zaune kikeyi amira?,da gasken ashe baki bacci ba"murmushi ta dan qaqalo
"gajiya nayi da kwanciyar sai na zauna na dan huta"
"Ko dai wani abu ke damunki?,ki gayan gaskiya" kai ta kada kanta a qasa
"A'ah ummi babu komai,kawai na gaji da kwanciya ne"
"To ko dakina zaki koma?" Ta fadi tana qarasowa gabanta
"Nan din ma yayi fa ummi"
"Indai akwai wani abu da bai miki dai dai da yadda kikeso kada kiyi nauyin baki ki sanar min......mijinki ne dama ya tasoni....maimakon ya kira taki wayar" ta fada tana dan murmushi tare da miqa mata wayar sannan ta juya zata fice
"Idan kin gama ki barta nan wajenki ko zuwa safiya na karba" ta fada tana ficewa tare da rufe mata qofar,wayar sumayya tabi da kallo sanda ta sake ruru,sunanshi ya fito baro baro,sai ta kauda kai kibiyar kishi na sukarta,wani kiran ne ya sake shigowa,a hankali ta shafa wajen amsawa ta daga ta kara a kunnenta
"Sumayyah!" Ya fada a tausashe cikin salon muryarshi dake ratsa zuciyarta,muryar nan da take mutuwar so,
"Sai yau kaga daman nemana?,ba ruwanka da hakin da nake ciki ko?,dama ba sona kake ba baka damu da ni ba...."
"Sumayyah" ya sake kiran sunanta karo na biyu ya katse ta a tausashe,kiran sunanta kadai ya karya mata zuciya kawai sai ta saki kukamai hade da sheshsheqa,idanunsa ya lumshe bugun zuciyarsa na qaruwa
"Ya salam!" Ya dinga furtawa can qasa tana shiga cikin kunnenta,ita kanta batasan me ya saka ta kukan ba,daga inda yake tsayen sai tsaiwar ta gagareshi,komawa yayi saman kujerar shima yayi kwance rigingine,wani dafi take zubawa zuciyarshi ba tare da ta sani ba,nadama ta kamashi,me yasa ya watsar da ita don kawai taqi binshi,shi kansa yasan cewa kansa da kansa ya hora,yama fita jigata,sabida shi din ya rasa komai,duk wani abu data sabar masa da shi a yanzu babu,sannu a hankali ta soma tsagaita kukan don kanta,bayan taji zuciyarta ya soma yin sanyi
"Kiyi haquri" ya fada kamar yana mata rada
"Ki yafemin.....na kasa sabawa ne.....na kasa daurewa rashinki....kamar maraya haka nake jina....am really sorry banyi da niyya ba" ajiyar zuciyar itama ta sauke,tana jin yadda kewarshi ke illatata,kalamanshi kamar sake tunzura qaunarsa suke cikin zuciyarta,saidai sarautar ta motsa,sai tayi mishi shuru kaman bada ita yake ba
"Summy....kice wani abu mana" yadda ya kira sunan nata sai taji kaman mukhtar,sake narkewa tayi cikin kujera ta kuma qi cewa komai din
"Samayyahh...." Ya kuma kiran sunanta,ya gane cewa kawai azabtar da shi take sonyi,kamar ya saki mata kuka haka yake ji
"Ki kulani ko don babynmu mana,i missed him alort shima fa" nan ba amsa,amma can qasan ranta wani sanyi na ratsata,wanda yayi tasiri har saman fuskarta,ta soma fidda wani boyayyen murmushi
"Wallahi tallahi na rantse idan baki ce min komai ba a gobe zaki ganni abuja" dariyar da take boyeea ta qwace mata,zata fi kowa son hakan,saidai bata masa adalci ba idan har tasa daga komawarsa cikin sati guda ya kashe kudin ticket dinshi ya sake dawowa,me zata cewa su ummi ya kawoshi
"My happiness...." Ta amsa mishi cikin wani irin salo wanda ya saukar da gungun farinciki wa zuciyarshi,ya sauke qatuwar ajiyar zuciya
"Ki tabbatar min da cewa kina lafiya keda baby na"a shagwabe tace
"ba wani.....bayan baka damu dani ni da babyn ba...."
"Ya ilahi....daina fada don Allah kada ki sani cikin wani hali.....ki fadi abunda zai miki yanzu wanda zan wanke kaina,wanda zai nuna miki tsantsar damuwar da nayi da ku"
"Just kiss me...." Ya subuce daga bakinta ba tare da tasan ta fadi hakan ba,wani wawan kiss ya bata ta cikin wayar wanda babu inda bai aika saqo ba cikin gangar jikinta da ruhinta sannan ya dora
"Ku raba ke da baby na"
"Baby yana godiya.....ka kwanta da safe mayi waya,sabida su'ad" ta hada kalaman da qyar,idanunshi ya daga ya dubi qofar bedroom din da take ciki,tunda suka zo ungulu ta koma gidanta na tsamiya,wani abun ma don yana taka mata birki ne
"Ban yarda ba" ya maidawa sumayya amsa
"Da gaske my happiness.....kaga idan ni kama haka ko bazanji dadi ba" shiru yayi yana murmushi kamar tana gabanshi,sunan data kirashi da shi ya tsaya masa
"Da gaske ni happiness dinki ne?"
"Sosai.....ban kuma sake tabbatar da hakan ba sai yanzu,na rasa farinciki da walwala na tsahon sati guda sabida batan dabo daka yiwa rayuwata,sai gashi cikin mintina qalilan da jin muryarka komai ya dawo min,farinciki na yadawo,sai tsananin kewarka da nake ji kamar zata rabani da ruhina..." Ta bashi amsa kai tsaye tare da katse kiran saboda tana ji tayi amfani da kalamai masu nauyi,mutuwar zaune kawai yayi daga wancan bangaren,kalan soyayyar da yake da buqata,kalan soyayyar da yake nema ido rufe yau gashi Allah ya bashi,baki daya ta gama kasheshi,dan qaramin ihu ya saki shi kadai kaman wanda ya soma zaucewa,gaskiya wannan karon baya jin zai iya bin umarnin su baba,ko sato matarshi sai yayi,bazai iya jurewa zama ba tare da ita ba,haka ya dinga jera kiranta amma tawi dagawa,daga bisani ta tura masa saqo tana shaida masa bacci zatayi sai da safe,wanda ita kanta bata gaji da jin muryarshi ba,tayi hakanne kawai don kada ta shiga hurumin su'ad.


Bacci tayi wanda ta jima bata yi irinsa ba,cikin nutsuwa da kwanciyar hankali da walwala,wanda har kusan makara tayi sallar asuba,ita kanta ummi washegari taga canji sosai,komai nata cikin walwala da kuzari take,kaman yadda kowa yaga sauyi tattare da almustapha har cikin kamfani,ciki har da su'ad,wadda ita bata lura da bai cikin walwala ba,koda ra kura ma watsar da shi tayi ta tsammaci miskilancin nashi ne ya motsa,koma shi dinne ita ba damuwarta bane tunda dole ya zauna da ita,hakanan kuma kudi taba samunsu fiye da yadda ma takesl,abu daya ke damunta yadda ya tikastata saka digayen kaya,haka duk inda zata sai ta tambayeshi,ko zuwa cinema ma ya hanata baki daya,yadda taci burin sakewa da qawayenta bata isa ba,saidai suzo gida su sameta,shima dole su kama gabansu gab da lokacin dawowarshi.


******* ****** *******


Baki daya ya zame mata wani chewing gum din waya,indai ka ganta da waya tofa almustapha ne,har sajida ta soma ganewa,da taga ta soma waya zata basu sarari,duk wani motsinta ha san da shi,wani sa'ilin har kukan shagwaba yake mata kan ta gudo zaya shirya mata komai,saidai kawai taci dariyarta tace bata iyawa,da wanne idanun zata kalli ummi da baba?,.


Cikin sati uku kacal ta soma sauyawa,jikinta yayi bul kamar ka taba jini ya fito,laulayi ya fara sauqi sai dan abinda ba'a rasa ba,yanzun kuma sai shegen kwadayi data koya,ci wannan ci wancan,duk da bata rabu da na hannun daman nata ba wato nama,ita kanta mamakin sauqin wannan cikin take.


Kwananta shirin anty dije ta dawo,ta gaya mishi zata wajenta,bai hanata ba yace ta gaidata ta kuma kula masa da kanta,sajida ta dauka suja tafi bayan ta yiwa ummi sallama,ummi ta bada wasu tararuka masu kyau ta kaiwa anty dijen.



Da minal mutuniyarta taci karo suna wasa da khalioha,dukansu suja durfafota da gudu,ta daga minal tana mata waqarta ta tsokana tana ta dariya abinta tana cewa
"Anty sumayya na girma fa yanzu"
"Ai naga alama,irin wannan kumatu haka?" Sumayya ta fadi sanda anty dije ke fitowa zuwa falon
"Kai kai kai,sauketa....sauketa nace" anty dije tace da sumayya,murmushu tayi tana sauke minal din,kaddai antyn har ta gano ta,numfashi anty dije ta sauke
"Ki rufan asiri sumayya don Allah kizo gida na lafiya ki koma lafiya" wannan karon dariya ta baiwa sumayya sai data qyace
"Kai anty....kai anty.....wai meye don ma dauki minal,naga ko da can ina daukanta" daquwa antyn ta watsa mata
"Da kika ce amma banda yanzu,na haramra,idan baso kike almustapha ya saka mu a black list ba ko ya dauremu baki daya" yatsina fuska sumayyan tayi
"Habawa,shi ya fara" ta bi bayan antyn zuwa dakin hara bayan abida ta gaidata nan ta barsu da minal da khalipha.


Laila da hafiz ne a dakin suna gyaran kaya,rungume sumayya laika tayi niyya anty dije ta harareta tana mata gargadi,ita dai bata gabe ko meye ba ta gaida sumayyan daga bisani ta hau zuba mata surutu,hafiz dama ya gama abinda yake cikin dakin,shi dama ba gwanin surutu ba,suja gaisa da sumayyan suka dan taba hira ya fice,laila kuwa sai da anty dije ta koreta ta hadata da qarasa girki a kitchen sannan ta fice,fuskar anty fes,farinciki kaman ta hadiye sumayya,kallo daya zaka mata maga sauyi baro bari tattare da sumayyan,ta zama wata matar hutu
"Waini zaki boyewa ciki sumayya?,to amira ta gaya min tun muna can" dariya ta saka tana kama baki.
"Oh su amira an iya gulmaaaaa"
"Abin farinciki ai ba'a biyeshi,ko abbansu khalipha bakiha dadin da yaji ba,yace ko shi yasa rannan da suka hadu da man fuskar nan kaman gonar auduga,abinda bai taba gani ba" dariya suka sanya baki dayansu,ranar hira suka yi sosai da anty dijen,basu koma gida ba sai bayan sallar magariba.


A falon ummi tayi sallama tana riqe da hannun abida suna hirar masu tsaron gidan da suka ga an sauya,ummin ce zaune tana kallon labaran duniya,ta amsa musu dai dai lokacin da eesha ke fitowa daga daya daga cikin dakunan dake falon,sanye da gown mara hannu,kanta ba dankwali sai waya riqe hannunta tana dannawa,bisa dukkan alamu bayan fitarsu gidan anty dije ne ta iso gidan,idanu suka hada eeshan ta jefeta da wani kallo,yayin da sumayya ta dauke kanta ta waraso ciki ta yiwa ummi murmushi,ta zauna kan kujera kaman yadda eesha ta samu kujera daya ita ta zauna
"Wato gida dadi ko?,sai yanzu?" Murmushi tayi tana cewa
"Bansan lokaci yayi haka bama ummi,umman khalipha


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login