Showing 126001 words to 129000 words out of 364327 words
cin abinci idan akayi buda baki har sai an kawo na gidan umman khalipha,yace shikam bai gane mana wannan wayon namu ba da muke maqale masa a kwanon,har gwara ni gauro ne shifa yaayaa fa" dariya ya bata har sai data murmusa,ta fuskanci mahmoud irin mutanen nan me masu barkwanci faran faran da saurin sabo da mutane.
A falon anty maamaan suka ci burki,wasu 'yammata ne zaune a falon biyu na saman kujera biyu na qasa,kowacce ta baje kayan kwalliya suna makeup,baki daya sun cika falon da hira da karadi,kayan sawarsu na aje gefe da alamu fita zasuyi wata unguwa,kana dubansu zakasan suna daga cikin baqin da gidan ke karba a irin wannan lokaci,sallamar mahmoud ita ta janyo hankalinsu
"Anty maamaa" kawai ya fadi,daya daga cikinsu wadda ke qoqarin daura dankwalinta tace
"Tana G-kitchen" juyawa yayi ya dubi sumayya
"Idan baki gaji ba muje bata cikin nan" bata ce komai ba tabi bayansa yayin da 'yammatan suka bishi da kallo,wadda ke daura dankwalince ta tabe baki,kishi ne fal bayya ne a fuskarta,ta kusa da ita ce ta zungurota ganin yadda take binsu da kallo
"Uhmmm,yadai?" Qaramin tsaki ta ja
"Nikam baisan me yasa Allah ya zubawa mazan gidan nan girman kai ba,suna jin kamar su kadai ne halittar maza da Allah ya qirqira a ban qasa,jibi,kamar baisan wace ni ba" dariya wadda ke shafa powder ta qyalqyale da ita sannan ta tsaya da abinda take yi
"Kema kinsan su isa sun kai suyi girmankan,karfa ki manta su su waye?,kina zaton samunsu a bagas ne,nikam banga laifi ba don sunyi girman kai sun kai suyi ne,kibi a sannu idan da rabonki zaki shiga familyn prof,nikam tuni na sallama" ta fadi tana ci gaba da murza hodarta,shiru tayi bata sake cewa komai ba sai taci gaba da gyara daurin dankwalin nata cikin sanyin jiki.
Bayan suka zagaya sai gasu cikin wani qaton kitchen wanda idan ba wajajen kayi ba ba lallai kasan da zamansa,kitchen ne babba mai dauke da electrics kala daban daban da manyan tukwane,kayan girki nau'i daban daban,kitchen ne da ma'aikatan gidan ke haduwa suyi amfani da shi duk lokacin bikin sallah irin wannan,biki ko suna na gidan idan ya tashi,gaidasu sumayyan tayi tare da yi musu sannu da aiki,antyn na tsaye sanye da jar shadda wadda keta maiqo da qyalli dinkin bubu da aka yiwa adon baqin zare,duk da ta tasamma shekara arba'in da kusan biyar amma sai ka zaci 'yar talatin ce,anty mama kam badai ado ba,tana sabe da wata kyakkyawar yarinya wadda aqalla zatayi shekara daya,an mata kwalliya cikin riga da wando,gashin kanta kuwa adin ribbom ne kala kala,ma'aikatan take sanarwa mai za'a dafa a mazaunin abincin dare a gidan baki daya
"Ah mahmoud yadai?,kun fasa tafiyar ne?" Ta fada bayan sun gama gaisawa da sumayya,shi kuma yana jan yarinyar dake kafadarta din da wasa wadda da alama itama jikar gidan ce,sumayyan na tsaye gefanta antyn riqe da hannunta daya
"A'ah,wannan mai tsoron shigowa gidan nan din na rako zata gaida baabaa" murmushi tayi ta juya tana kallon sumayya,haka nan sumayyan take burgeta tun ganin farko,da alamu zatayi nutsuwa,bata da rawar kai da fi'ili irin na 'yammatan zamani,shigarta kadai ta tabbatar mata da cewa daga babban gida ta fito,koda ba gidan da suke da kudi da ababen more rayuwa ba,a'ah,babban gida na nufin gidan mutunci da karamci,gidan da aka san dattako,gidan da usuli ilimi tarbiyya da wadatar zuci,gidan dake cike da tarbiyya da daraja
"Ba tsoro bane,baqunta ce" inji antyn tana murmushi,kusa da antyn ya matso bayan ya ajjye mata kwanon
"Nidai anty gashi nan,a tuna da ni idan baabaa zaici abinda ke cikin kwanon nan" hararsa tayi
"Haka fa,anqi aure anbi an takura mana miji,kunqi barinsa yayi auki,komai zaici sai kun tayashi" dariya ya sanya yana ficewa tare da fadin
"Wannan tsohon mijin naki anty ana ji da shi" itama dariyar tayi sabida tasan halin zolayar mahmoud,qarasa lissafa musu abinda ya dace tayi sannan ta dubi sumayya tace
"Bismillah" ta soma qoqarin tafiya tare da daukar kwanon,ganin haka ya sanya sumayyan matsawa kusa da antyn ta miqawa yarinyar hannu,zubawa sumayyan ido tayi tana kallonta,dariya anty tayi
"Wannan uwar qyuyar,Allah yasa ta yarda,uwarta na can ta tafi yawon saloon din da ba'a yishi ba sai yau ta barni da rigimamma" kamar taji kuwa abinda antyn tace sai ta miqawa sumayyan hannu alamar ta dauketa,ba antyn ba har masu aikin ta basu dariya,saboda kowa yasan qyuyarta ba da kowa take yarda ba
"Lallai kin ciri tuta mai sunan umma" ta kira sumayyan da haka saboda tuna sunan wace garesu,murmushi ta danyi tabi bayan antyn tana duban yarinyar,sai ta tuna mata abdallahnta,ko yanzu me yake?,tana kewarsa sosai,ta qagu lahadi tayi ta ganshi,sai kuma ta tuna yaranta wadanda ke tayata zama tun suna tsohon gidansu da mukhtar,su naana kam tasan yanzu sun girma,tana saka ran in sha Allah da zarar ta koma zata ziyarcesu,itakam tasan cewa son yara a jininta yake haka halittarta take,duk inda taga yaro ya dinga burgeta tana kallonsa kenan.
A hankali suke ratsa gidan anty maamaan na janta hira kadan kadan,jefi jefi suna gaisawa da mutane a kan hanya wanda da alama basu hadu bane tun safe sai yanzu,ba mamaki saboda girman gidan wanda ya iya hadiye duka baqin dake ciki,tun daga farkon sashen ta tabbatar da cewa akwai banbanci da sauran sasannin gidan,antyn dai na gaba tana bin bayanta,yarinyar na ci gaba da kallon sumayya tare da yi mata shirmen surutu irin na yaran dake son koyon magana ita kuwa na biye mata anty na binsu da murmushi har suka isa qofar da zata sadasu da babban falon dake mallakin mai gidan ne.
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
6⃣0⃣
*Bismillahir rahmanir rahim*
*SHIN KO KUNSAN DUK LOKACIN DA AZABA TA TSANANTA GA DAN WUTA,FATAR JIKINSA TA KWASHE TA QONE,ANA SAUYA MASA WATA FATAR NE SANNAN ACI GABA DA GANA MASA AZABA*
*Allahumma la tada a lana zanban illa gafartah*
____________________________________
Dattijo ne mai kimanin shekaru sittin da biyar zaune kan daya daga cikin kujeru na alfarma dake zagaye da falon,haiba kwarjini da kamala sun bayyana qarara kan fuskarsa,Allah yayi masa baiwar furfura tun daga gemu zuwa kansa,farin gilashi ke saye a fuskarsa baya ga shaddar dake jikinsa fala sol,dogon wando da riga mai gajeran hannu iya gwiwa,da alamu akwai babbar rigarsu wadda bai sanya ta ba,gefensa daga hannun dama samari ne guda uku,wanda ke daura da shi yana fuskantarsa sosai,bisa alamu magana suke mai muhimmanci,kyakkyawan matashine mai cike da kyau kwarjini izza da haiba,sanye yake da irin kayan tsohon bisa dukkan alamu anko sukayi,shi dinma fuskarsa sanye take da gilashin,daya hannun nashi ma wasu matasanne su biyu sai mata guda biyu.
Tunda suka shigo falon gabanta ke mugun faduwa,sosai ta dinga qoqarin baiwa kanta qwarin gwiwa saboda haka sai ta sadda kanta qasa har suka qaraso cikin falon suna sallama,dattijon ne ya amsa da wasu daga cikin mazauna falon,idonsa na kan antyn da sumayya har suka qaraso,gefe ta samu ta zauna daga qasan carfet din,da sauri baabaa yace
"A'ah,tashi ki koma saman kujera mana" murmushi tayi kanta na qasa,ta soma gaidashi tare da yi masa sannu da zuwa,fuska sake tamkar ya santa ya amsa mata,anty ta dubeshi
"Nasan baka santa ba" sake dubanta yayi yana gyada kai
"Gaskiya kam,koda na santa to ta kwanta min,kinsan shekarun sun fara turawa sai a hankali" sauran dake zaune sukayi danyi dariya banda mutum daya da tun shigowarsu ya dauke kansa ya maida hankalinsa kacokam kan wayarsa yana tura saqonni,hakanan ransa yake a bace.
"Itace wadda ka dinga bamu labari ka kwashi girki na kwana ashirin ka dinga zabga santi" baki daya dariya suka kuma saki wanda hakan ya dan ja hankalinsa,har ya sanyashi daga kai ya mata kallo daya tak ya sake maidawa kan wayarsa yaci gaba da abinda yake
"Masha Allah,Allah yayi albarka,naji dadin abinci kam qwarai da gaske,Allah yayi albarka"
"Amin baabaa,na gode" ta fada cikin jin dadi bisa dabi'arta ta son na gaba da ita wanda take saka ran addu'arsa zata iya binsa ya sa mata albarka,hannu ya miqawa husna wadda ke hannun sumayya,ta kuwa lafe a jikinta tamkar ta santa,qememe taqi zuwa,sai ya zura hannunshi cikin aljihun rigarsa ya zaro alewa,kasancewarsa mai yawan kyauta,musamman a irin wannan lokaci da jikokinsa ke kasancewa a gidan tare da shi,hakan ya sanya baya rabo da alewa da sabbin kudi,miqa mata yayi take kuwa ta tafi gurin nasa,hannu yasa ya dagata yana dariya jama'ar falon na tayashi,tsaki ya ja qasa qasa yana miqewa,shikam bai san me yasa abun dariya bai yiwa su mu'azzam wuya ba,shi baki daya ma baiga abun dariya ba,yarinyar ma tunda ta shigo baki daya ma yaji ransa ya baci,musamman katse musu hanzarin da tayi kan muhimmin batun da suke tattaunawa,tun dazun dama yake addu'ar kada wani ya shigo saboda baison abinda zai katse masa bayanin da ya daukowa baban,ya san mutum ne shi mai mutunta baqo,kome yakeyi yana iya katsewa ya saurari baqonsa,sarai baaban ya ganshi amma sai ya qyaleshi,yasan halin kayansa sarai,da idanu ya rakashi har ya fice,ganin ya fita ya sanya sauran miqewa
"Baabaa kada fa ya tafi ya barmu"
"Jeku,don tsaf zai iya aikatawa,musamman da kun zo da tsarin da baiyi masa ba"dariya suka yi sannan sukayi sallama da baban suka fice,tattambayarta baabaa yayi kan wasu abubuwan tana amsa masa,har alokacin kanta na duqe,ta miqe bayan wasu mintuna ta masa sallama,sai anty ta ajjiye masa kwanon tana masa bayani,qwarai da gaske yaji dadi,domin shi mutum ne da baya raina alkhairi komai qanqantarsa,koda yafi qarfin abu ka bashi shi yana ganin girmansa abun agunsa,dakatar da ita yayi yana fadin
"bari na baki zamzam da bagaruwa ko"
"To" ta fada tana murmushi,antyn yama kwatance cikin dakinsa,cikin sakanni ta shiga ta fito da wata jarka
"Ba ita ba,zamzam din da nayi dawafi da shi" mamaki antyn tayi,don irin wannan zam zam din ba kowa yake bawa shi ba,dashi yaje dawafi da addu'o'i,yakam zama magani cikin ikon Allah ga duk wanda ke jin lalura ya bashi yayi amfani da shi,duk da kasancewarsa tantagaryar dan boko amma akwai ilimin addini mai yawa tattare da shi,jarka ce guda tayi tsawon ta faro qarami ya zuba mata,sannan ya cika mata leda da bagaruwa da dabino,godiya tama baban sosai ta kuma ji dadin kyautar tasa,tare suka fito da antyn
"Anty zan koma"
"Haba daga shigowarki,kodai tsoron kike ji kamar yadda mahmoud ya fada,naga ko mutuniyar taki amira baki gani na,bayan ita tunda muka dawo take maganarki,na tabbata baqi ke suka hanata fitowa da tuni kin ganta,sannan baki shiga kin gaida ummee ba" sam bata so antyn ta debo mata wannan bayanin ba,amma sai ta sadda kai tace
"To,bari na shiga"
"Yauwa,ki gaida ummam khalipan don Allah idan kin koma,nasan itama baqi ke suka hanata leqowa,dukkanmu irin wannan lokacin sai haquri baqi muke ba dauke qafa"
"To zataji" ta furta sanda antyn ke yunqurin amsar husna,nan ma qi tayi,dariya antyn ta dinga
"Shikenan kuje da ita kin samu qanwa,idan tayi kuka ko laila kaya bada ta kawota"
"To anty" tafada tana dariya tare da yin gaba.
Baki daya falon ya sauya ba kamar waccan karon data shigo shi ba,da alama gyaran azumin ne,komai ya canza a falon,saidai tun kafin ka kai ga qarasowa cikin falon zaka jiyo muryarta,tana tsaye tsakiyar falon hannunta riqe a qugu tana zuba masifa,bisa alamu da 'yanmatan dake zaune a falon take,sun kusa su hudu harda amira dake gefe tana shan ice cream hankalinta kwance kamar ma bata falon
"To bani cike da iskanci,ran kowa sai ya baci wallahi,bazan dauki raini ba,kuma wanda ya fasa karbo greeting cards na 'yammata yana kawowa bai cika ba mu zuba ni da ku,aikin banza kawai" tana gamawa ta juya a fusace tana taku kan tsireren takalminta mai igiya,kowa sanye da suturar al'ada banda ita,wando ne a jikinta irin straight leg din nan,sai riga one shoulder a jikinta,gefe sumayyan ta janye tana dubanta,dariya taji 'yammatan suka saki bayan fitar tata banda amira fake ci gaba da abinda take,daya daga cikinsu tace
"Duk wayon amarya wallahi sai an sha manta"sai a lokacin sumayyan ta maimaita sallamarta,amira ce ta amsa cikin fara'a ta miqe
"amiran umman khalipha kinsan kina raina,sannu ga guri zauna" tana mata nuni da wata kujera dake can gefe babu kowa,qarasawa tayi tana zaman amira ta sake cewa
"Ina kika tsinto wannan uwar qyuyar,daina kallona kina wani saukar da kai ban daukanki zanyi ba nima" ta fada tana dan daga murya da zaro ido da alamu tana jin haushin irin qyuyar husnar,murmushi sumayya ta saki tana dafe kan husna wadda ta kwantar da kanta aqirjinta
"Dole fa ta miki qyuya,kina mata irin haka"
"Allah bata da kirki" gaisawa sukayi ta mata sannu da zuwa sannan ta tambayi ummin
"Ummi na sama,bari na miki kiranta"
"To" ta amsa,satar kallonta 'yammatan suka ci gaba da yi itakam hankalinta na kan husna tana mata wasa a haka amira ta dawo ta tadda su,ba dadewa ummin ta sauko,abinda sumayya ta dan lura da shi shine,ummen irin mutanen nan ne da basu son hayaniya da yawan surutu.
A mutunce ta gaidata ta amsa mata fuska a sake itama tana son daukar husna,saidai itama husnar ta watsa mata qasa a idanu kamar sauran,tilas ta barta sumayya na mamakin qyuyar yarinyar,bata wani jima ba tayi musu sallama ta fice sabida yadda 'yammatan ke kallonta.
Anty dije ma tayi mamakin ganinta da husnar,goyata tayi bayan ta bata abinci,ba jimawa kuwa tayi bacci a bayan nata,gab da magariba sukaji sallama a falon,sumayyan ce ta fito goye da husnar tana amsawa,magidanciya ce wadda zata doshi shekara talatin da hudu,fuska a sake sumayya tayi mata sannu da zuwa,leqa bayan sumayyab tayi tana riqe baki cikin fara'a
"Wai lallai raino yayi dadi,ashe kam da gaske tana nan din,ni ina can hankalina na kanki uwar qyuya ashe ke kin haye bayan mutane kina bacci abinki" dariya sumayya ta danyi sai alokacin ta fuskanci mamarta ce,yunqurin saukota tayi tana fadin bari ta bata ita
"A'ah,barta mana idan ba'a matsa miki ba,haba sai kace bare,da nan da gidan baabaa ai duka daya ne,kawai dai idan ta tashine nasam zata taba miki darunta,sai azo a dauketa"
"To" ta amsa tana gyara goyon
"Ina anty dije" ta ambaceta da sunan da suke kiranta a kano sabanin yadda taji mutan gidan na kiranta da umman khalipha
"Yanzun nan ta shiga wanka"
"Sarkin kwalliya wa miji,idan ta fito kice ina gaidata" ta fada da sigar zolaya,bisa alamu sun saba sosai.
Bata farka ba sai bayan magariba sumayyan ma na shirin tada isha'i,daukota tayi daga kan gadon ta cire mata pampers tare da zuba abinci ta bata,sai da taga ta qoshi sannan ta sabata a kafada ta zura hijabin sallarta wanda ke kusan sharar qasa tace khalipha yazo ya rakata.
Tarwai gidan da haske kamar kowanne lokaci,saidai yau akwai yawaitar mutane a harabar gidan,sashen anty maamaa ta shiga tacu sa'a ko ta tadda maman husnar,amsarta tayi tana yiwa sumayyan sannu tare da godiya.
Tunda ta tako daga sashen anty maaman ya zuba mata idanu,haske gidan kadai ya wadatar masa ya gane wace ita,mahmoud da ya gaji da yi masa magana ya dafa kafadarsa wanda hakan ya sanyashi daga kai da sauri yana dubansa
"Mahmoud,sumayya ta nake gani a gidanku" waiwayawa yayi zuwa inda yaga alqasim din na kalla,tabbas sumayya ce ke tahowa
"Wannan sumayyan ce sumayyarka dama?"
"Wallahi itace" alqasim ya fada a rude,dariya mahmoud ya saki
"Ai tazo gidan sauqi,amma fa ba abune mai sauqi ba shawo kanta haka na fuskanta"
"Please mahmoud" alqasim ya fada cikin damuwa yana hade hannayensa ganin sumayyan na gab da su
"Don't mind"mahmoud ya furta yana waiwayawa yadda zata iya ganinsa idan ta qaraso,sam bata lura sa su ba duk da hasken da ya wadatar da gidan tamkar raba,hanakalinta na gefe can inda wasu 'yammata ke zaune suna hira,kusan basu suka dauki hankalinta ba ma yaran dake wasansu kusa da su ne,wanda daya daga cikinsu keta kiran abbanaa da alama labarin abban nasu yake basu,tana ganin sa'o'in abdallah a ciki,cikin ranta ta raya suna cikin farinciki da gata,sabanin abdallah da take fatan zai tashi cikin farinciki saidai baisan dadin uba ba,qwalla ta taru idonta sai tayi hanzarin sadda kai da qara sauri a tafiyarta don ficewa daga gidan,tun jiya ranta a jagule yake,hakanan ta wuni da tunaninsa cikin ranta,wanda ya haddasa mata kasala da mutuwar jiki wunin baki daya,shi ya qara mata qyuyar fitowa waje
"Yi a hankali kada ki fadi" mahmoud ya fada yana dubanta,cak ta tsaya tana dubanshi tare da qaqaro murmushi
"Hala sauri ake a fice daga gidan namu"dariya ma yaso bata saidai bata yin ba sai murmushi saboda damuwar da zuciyarta ta shiga daga tuna mukhtar
" kadai camfani"
"Ko kadan,to daina saurin,ga baqo kinyi,yanata nemanki wata da watanni sai yau Allah ya qaddara haduwarku" a zabure kamar wadda ta yiwa sarki qarya ta daga kai,suka hada idanuwa da alqasim,farinciki yake ji sosai cikin ransa,takowa yayi gefanta yana dubanta
"Zakaran da Allah ya nufa da cara sumayya,mai yiwuwa Allah ya qaddara wani lamari ne mai girma tsakaninmu,shi yasa ya kado hankalina abuja gidansu abokina mahmoud,ashe rabon na ganki ne" ba shakka tana ganin girma da qimar mahmoud,tunda shi ya soma tsaidata,banda haka da tuni ta yankawa alqasim warning cikin daqiqun nan tare da kaucewa.
Saye yake da quater zip sweater mai dogon hannu ta kamfanin armani maroon colour saboda sanyin da ya soma busawa sakamakon hadarin da ya hadu dazu bai zub da ruwa ba sai ya bada sanyi wa garin baki daya,wandon jeans baqi,sai high top sneakers,hannayensa saye cikin aljihun wandonsa ya fito zuwa harabar gidan yana duddubawa,kusan al'adarsa ce wannan a lokaci irin wannan,kafin yaje ya kwanta sai ya dudduba ko ina saboda baqin dake gidan,ya tabbatar babu yarinyar data fita yawo balle akai ga zuwan saurayi zance gidan,yace duk mai buqatar hakan ta bari idan ta koma gidansu tayi abinda taga ya mata amma ba cikin gidansu ba,tsarin ya yiwa baabaa prof saboda haka baice komai ba,a irin hakan wasu daga 'yammatan wadanda suke zaton wayewa ce garesu,iliminsu da gogewarsu ta kai wani mizani,sukan fita ciye ciye ko siyayya da samarinsu,wani lokaci sukan kai goma ko tara na dare basu