Showing 9001 words to 12000 words out of 364327 words

Chapter 4 - KUNDIN KADDARATA COMPLETE HAUSA NOVEL

HUGUMA   

20 Aug 2024

40079

Gamawarsu yayi dai dai da bugun qofa da ta soma ji,ta miqe ta fito tana tambayar waye tare da nufat soron,tun kafin ta kai ga budewa taji cikin kakkausar murya
"Malama ki bude bana son salo kin wani kama qofar gida kin rufe,bayan kinsan akwai wadanda zasu zo,dadin abun saura 'yan kwanaki naga ta iyayi" da sauri ta qarasa bude qofar domin tuni ta dauki muryar wace,yaya bara'atu ce sai fadima tsaye a bayanta,dai sauran da bata san su waye ba,tasan dai ba zasu wuce dangin amaryar ba tunda ita daga amaryar har 'yan uwanta babu wanda ta sani,iyaka dai tasan cewa amaryar 'yar aminiyar yaya yahanasun ce.

      Saura kadan yaya bara'atun tayi gaba da ita badan tayi gaggawar matsawa gefe ba ta wuceta saura suka biyo bayanta suka bar mazan da zasu shigo da kayan katakon da kujerun.

     Bata qosa ba tabi bayansu zuwa dakin da aka bawa fa'izan wanda tuni yasha fentin farar qasar data siya tayi da kudinta,babu komai a dakin a share yake fes kasancewarta gwanar tsafta ce,tun kafin tace wani abun yaya bara'atun ta galla mata harara yayin da sauran suka mata caa da ido
"Uban me kuma kika biyo mu ki mana?" Ta tambayeta tana huci,qasa tayi da kanta saboda yaya bara'atun ta girme mata nesa ba kusa ba cikin ladabi tace
"Zuwa nayi mu gaisa ne"
"Riqe gaisuwarki bama so"
"Uhmm,wallahi kuwa" fatima tayi caraf ta karbi zancan
"Allah ya baku haquri" ta fada sannan ta juya ta fice kai tsaye falonta ta shige taci gaba da kallonta.

       Miqewa tayi zata dauko wayarta dake uwar daki tana ringing ta hangosu suna kici kicin budw kwadon dake rufe da dakin ya mukhtar wanda da kansa yasa ya rufe ya tafi da abinsa,da taga a kulle yake sai ta saka tana fadin
"Lallai,kaddai yaya mukhtar daki daya ya bayar,tabdi lallai,yana nufin ita a falle daya zata zauna waccar tana da ciki da falo....haka ne....mu shirya mata kayan idan muka koma ma sanar da yaya yahan",bata ce uffan ba don ba mas'alarta bace,ko tata din ce ma basu sako da ita ba.

      Ya mukhtar ne ya kira yana tambayarta komai lafiya ko tace eh sannan sukayi sallama ya kashe wayar.

      Kafin wani lokaci gidan nasu ya cika da 'yan jeren,ko ina sai shewa ke tashi da qananun magan ganu,take tsoro ya cika sumayya,ta dinga kiran lambar maman naana kan ta shigo ta tayata zama amma wayar a kashe take,ta dinga leqe ta window dinta taga ko akwai hanyar da zata ratsasu ta fice.

      Bata samu sararin gurin ba sai da suka fara daura alwalar sallar azuhur,tayi hanzarin shiga uwar dakanta ta dauko hijabinta tare da padlock  ta sanyawa qofar dakin nata ta fice.

     A qofar gida ta tarad da su naana suna tsaye,suna ganinta suka nufota da sauri,ta dubesu tana cewa
" me kuma yau kuke tsaye a qofar gida?"bilkisu ce tace
"Hanamu shiga anty akayi?"
"Waye ya hana ku shiga?"
"Masu jeran amarya"inji nana,take taji ranta ya baci,sam bata son abinda zai taba mata yaran,ba zata juri haka ba sam,bata ce misi komai ba sai
" kuzo muje,qila fitina zaku shiga kuyi musu shi yasa suka hanaku shiga don kada ku bata masu kaya"
"Wallahi anty a'ah" inji aysha
"Shshshshah" sumayya tace da su,sun san me take nufi ko batayi magana ba,bata da son su kawo mata hirar wani dama.

      Gidan mamam naana ta shiga,ta taras da ita tana kwashe abinci cikin kula
"Ina zaku haka ke da gayyar yaran naki,ina kika baro baqin naki,ai yanzu nake shirin shiga kinga girki ya tsayar da ni ina so na kammala na turasu islamiya sannan na shigo" murmushin yaqe tayi ta ja kujera 'yar tsuguno ta zauna daga bakin qofar falon maman nanan,yaran nata suka zazzauna kusa da ita
"Eh wlh,na gaji da zama ni daya nace bari na leqo"
"Banda abinki sumayya aiko baki aiko na shigo miki ba kyayi waya a turo miki halima da zainab ko su tayaki zama"
"Wallahi maman naana bansan haka akeyi ba ai" murmushi tayi tana tausayawa sumayya da quruciyarta
"Ai shikenan,Allah ya bada zaman lafiya,ya kade fitina tsakaninku"
"Amin" sumayyan ta fada cikin faduwar gaba.

     Duka yaran ta zubawa abinci suka ci sannan ta tura kowa ya gida saboda ganin lokacin tafiya islamiya yayi,ta shirya su naana ma suka tafi sannan suka daura alwala sukayi sallar azahar ita da sumayyan.

     Shinkafa da miya har da salad da kifi abinda ta dafa ta zubo musi cikin plate
"Sauko sumayya maza muci" kai ta girgiza don a cunkushe take jin cikinta babu space din abinci
"Na qoshi maman nana" tausayinta ya kamata amma ta dake tayi murmushi
"Sauko muci akwai abinda nakeson gaya miki" bata da jan doguwar magana saboda haka ta sauko ta sanya hannu suka soma ci.

      Cikin hikima maman nanan ke kwatantawa sumayya dabarun zama da kishiya,qissa dabara da wayo kala kala,ta dora da yi mata nuni da haquri,kau da kai kara da alkunya,gaskiya da amana,zama na tsakani da Allah,sai gashi sun tashi da abincin tas,har sai da hannayensu ya fara bushewa da miya saboda sun kasa tashi a gun darussan maman naana sunqi su qare,saiga sumayya na kwasar dariya saboda wani abun idan maman nanan na gaya mata kunya ce ke kamata ko mamaki.

     Hararta maman nana tayi dariya itama nason qwace mata itama amma ta dake saboda yadda taga sumayya na dariya wani abu da ta gaya mata
"Au dariya ma nake baki ko?,zaki ci gidanku wallahi idan baki dauke duk abinda nake gaya miki ba" cikin dariyar ta dafe baki
"Yi haquri maman nana,abunne wallahi" ta kuna saka dariya,kada kai maman nana tayi itama dariyar ta qwace mata,ba shakka sumayya danyace har yau,ta miqe ta dauke plate din da suka gama cin abincin ta fice da shi.

     Basu ankara ba sukaji ana qwala kiran sallar la'asar,nan suka tashi sukayi,maman nana ta dubeta tace
"Ba zaki koma gida kiyi girki wa mukhtar bane"
"Ina som in koma maman nana amma ina zaton har yau basu tafi ba,bari na kira ya mukhtar din naji mai zai ce".

     Koda ta kirashi cewa yayi tayi zamanta kawai idan ya dawo din ya kirata ta dawo,a nan tayi zamanta suka ci gaba da hirarsu har su nana suka dawo daga islamiya,sai qarfe shida kiran mukhtar ya shigo wayarta,ta yiwa maman nana sallama ta wuce gida.

      Kaca-kaca ta tarad da gidan tun daga qofar gidan tamkar bata taba shara ba,kwalaye da ledojin abubuwan da suka jera duja ko ina a gidan,ga kwanukan abinci nan nata har da sabbi da bata taba amfani da su ba,da alama ma girki sukayi saboda kitchen din na bude zasu jerawa amarya nata kayan a ciki,mukhtar na tsaye a tsakar gidan riqe da qugu cikin bacin rai,da alama ransa ya baci da irin abinda sukayi,ga abincin da suka dafa din ma basu iya cinyewa ba sun kuma lalata bare a bawa wani,zai soma sababi ta shige jikinsa ta soma lallabashi,sai da ta sauke masa temper dinsa sannan ya tayata suka fara kintsa gidan fes.

     Kafin su kammala anyi kiran sallar magariba,ruwan wanka ta dora musu sannan sukayi alwala sukayi sallah,bayan sun idar ta juye musu ruwan sukayi wankan tare,ta shirya tsaf tayi kwalliya cikin qananun kaya,zata dora musu girki yace ta barshi kawai ya zura jallabiyyarsa ya fita.

    Cikin minti a shirin ya dawo da ledoji a hannunsa,ya ajjiye kan kujerar yana cewa
"Dauko faranti ki juye mana wannan,ki hado da cups,hala ma yau duka bakici abinci ba" murmushi tayi sanda take fita daga falon tana cewa
"Naci mana ya mukhtar a gidan maman naana" ,ta dawo dauke da plates din ta juye abinda ke cikin ledar.

     Tsire ne da zafinsa sai zuba qamshi yake,sai rabin gasashshiyar kaza,ta bude dayar ledar,lemon roba ne na fanta sai maltina wanda tasan ta mukhtar din ce tunda ita bata dameta ba.

       A nutse suke ci suna hirarsu jifa jifa kamar babu wani abu dake damunsu.

      Suna tsaka da ci wayar sa ta dauki qara,sumayya ta miqe ta isa inda take chargy ta ciro masa kana tazo ta miqa masa,baquwar lambace,yayi kamar bazai daga ba amma yadda kiran keta nacin shigowa ya sanyashi dagawa ya kara a kunnensa.




*mrs muhammad ce*


📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
✍🏽 *~KUNDIN QADDARATA~*✍🏽
📖📖📖📖📖


*~NA~*

*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*

*WATTPAD:HUGUMA*

*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)

_________________________

_Bismillahir rahmanir rahim_

*_la yadillu rabbi wala yansa_*
_______________________


*_ina taya maman farida(dan maliki,baya tsami banza,hanyan ruwa)murna sauka lafiya tare sa samun zan kadeden baby boy,Allah ya raya mana shi cikin musulunci,ya albarkaceshi,ya qara musu lafiya ita da babyn,sannan kuma muna kamu tun yanzu,lol_*




0⃣5⃣





    Sallama yayi maimakon ya amsa hello da ake faman cewa,yayi jim yana jiran amsa sallamar tukun,fahimtar abinda yake nufi da akayi ya sanya aka sa sallamar
"Da wa nake magana?",cikin karyar da murya akace
" mukhtar baka ganeni ba,fa'iza ce fa"
"Fa'iza?,wacce fa'iza" wani murmushi akayi mai fidda da sauti cikin siga ta nufin jan hankali
"Fa'iza amaryarka mana".

       Hade rai yayi kana cikin dakiya yace"ok,ya akayi?",sake marairaice murya tayi
"Haba mana mukhtar,ai ko gaisawa ka bari muyi tukunna ko?"
"Yayi kyau,ina gajiya?"
"Gata nan muna fama da ita mun fara shiga sabgogin biki,amma mukhtar ko marmarin sake zuwa guna bakayi,haba"
"Wannan ne dalilin da yasa kika kira ni?" Kai ta girgiza kamar tana gabansa,cikin ji haushin yadda yake amsa mata da qyar kamar wanda aka tilastawa
"A'ah ba shi bane"
"Fadi uzirinki kai tsaye".

      Gyara zama tayi sannan cikin salo da kisisina ta fara magana
"An ce daki falle daya ka bani,haba mukhtar,ya zaka bani daki falle daya sannan ka bawa uwar gidanka ciki da falo alhalin nice amarya ni nafi cancantar ciki da falo"tana direwa ya dora
"Ko?,a wanne hadisin?".

     Fara quluwa tayi amma ta dake"haka na ya dace ai"
"To ai babu damuwa,sai ki gayan nawa muka hada muka gina gidan sai na fidda miki haqqinki" ya fada cikin jin haushi da sigar gatse,da sauri tayi saurin cewa don kada kwabarta tayi ruwa
"Allah ya baka haquri ba nufina kenan ba" tayi saurin katse wayar,cilla wayar yayi gefe yana jan tsaki kana ya tsame hannunshi daga tsiren ya wuce daki.

      Itama kasa ci gaba da cin tayi,saboda haka ta tsame nata hannun ta fada wanka,ta gyara jikinta ta sanya kayan bacci sannan ta lullube farantin tsiren ta bishi da shi,cikin kwantar da murya da tausasa harshe ta sanya shi suka cinye tare.

      Ranar alhamis ta siyi relexer,nan saloon din dake bayan layinsu ta shiga aka wanke mata kanta aka busar mata cikin drayer,da yake tana da gashi babu laifi sai ya sake kyau ya kwanta sosai,daga nan bata shiga gida ba,gidan maman nana ta shiga wadda ta kwaba su madara ruwan kankana qwai su dilka da kurkur tana jiran dawowarta,ita ta gyare mata jikinta fes,zuwa la'asar ta fito shar,fatarta ta sake wani kyau da haske.

    Tsokanarta sosai mukhtar ya dinga yi,yana mata waqa
"Uwar gida na,amarya ta,amanata ki damqeta(waqar my habib(muhammad)" dariyar itama ta dinga yi.

     Ranar juma'a aka zo aka mata lalle ja da baqi,ta aika halima da zainab suka karbo mata dinkinta data bada kala takwas cikin kayanta,duka sai data gwada babu wanda bai mata kyau ba,a nan su halima suka kwanar mata da anty dije qanwar mamanta saboda washe gari asabar zata yi wuni saboda ranar sukace zasu kawo amarya.

       Wuni tayi babu laifi ta dan tara jama'a,sosai mutanen unguwar suka yi mata kara sun shishshigo,maqotanta na kusa da gidan ne suka zauna mata suna jira a kawo amarya su karbeta.

       Ana gab da sallar magariba ta shiga tayi wanka,ta sauya wasu kayan cikin kayanta,shadda ce ja wadda aka yiwa baqin stone work,kwalliya tayi mai kyau da tsari,sosai tayi kyau saidai komai da take yi cikin sanyin jiki take yinsa,haka nan take ta fama da fargaba da faduwar gaba,anty dije nata azalzalarta kan ta shirya kada 'yan kawo amarya su iso bata gama shiryawa ba,ta dauki turare ta feshe jikinta sannan ta nemi baqin mayafinta mai kyau da kwalliyar duwatsu ta yafa ta dawo falo.

       Tun magariba suke zuba idon ganin amarya har qarfe takwas na darw babu ita babu alamarta,hakan ya sanya maqotam suka fara tafiya da dai dai da dai dai saboda dawowar mazajensu,wasunsu kuma sun bar yara a gida,har tara shiru hakan ne yasa 'yan uwanta suka fara mata sallama suma saboda tafiya nasu gidajen,babu wanda za'a bar mata saboda anty dije tace hakan baiyi tsari ba,sai taji zuciyarta ta raurawa qwalla ta cika mata ido,bata san me zata yi ba batasan ya zata yi ba hakanan bata san yadda akeyi ba,anty dije da maman nana ne suka dinga kwantar mata da hankali tare da bata shawarwari wadanda suka sake sanya mata nutsuwa,sukayi mata sallama suka tafi,maman nana kawai ta rage.

       Qarfe goma na dare maman nanan na shirin tafiya itama ganin shirun yayi yawa sai ga hayaniyarsu da ta motocinsu,hakan ya sanyata ta koma ta zauna tana tsumayin isowarsu,saidai ga mamakinta yadda akeyi a al'adance a fara kai amarya ga uwargida su ba hakan bane,dakinta suka bude kai tsaye suka shige da ita suna faman yada kirari tamkar jinin maroqa
"Shiga da bismillah uwar 'ya'yan mukhtar".

       Da sauri maman nana ta soko ma sumayyan wata hirar don ta hana kunnuwanta jin abinda suke fadin,saidai ko kadan bata cimma nasara ba saboda wani tashin hankali da taji ya ziyarceta,gudun zuciyarta ya qaru,sai ta kalli maman nana
" maman naana,qirjina bugawa yake bansan me ya sameni ba"dan murmushin kwantar da hankali tayi mata
"Kada ki damu,wannan shi ake kira kishin,kiyita ambaton hasbunallahu wa ni'imal wakeel,ni'imal maula wa ni'iman nasir" kai ta kada hawaye na silalo mata,ta sanya hannunta ta share tana mai bawa kanta qwarin gwiwa tare da hana kanta da kanta kuka.

     Labule aka bankade aka shigo,fiddausi cs goye da 'yarta,ta dubi sumayyan sannan tace
"Kije dakin amarya,yaya bara'atu na son ganinki",cikin mamaki maman nana ta dubeta
" a'ah,ai ba'a haka,amaryar ai ya kamata tazo ko?"duban maman nanan tayi sai ta juya ta fice ba tare da tace komai ba.

     Ko minti daya ba'a qara ba saiga yaya bara'atun ta shigo
"Baiwar Allah ke a suwa kuma,wacece ke da har zaki hanata zuwa,to bari kiji,idan ma irin masu shige da fice ne gidan kishiyoyi suna hurewa kishiya kunne wahalar da sumayya kawai zakiyi,don zama fa'iza tazo yi ta kuma hayayyafa,ba mun kawota ne don ta tafi ba,saboda haka ke sumayya ina jiranki", wani abu yazo ya tokare maman nana a wuya,tamkar zata tanka sai taga hakan bashi da wani alfanu,tayi qoqarin kai zuciyarta nesa,saboda koda ta tanka din qila qarshe abun ya juye kan sumayyan wanda bazata so hakan ba,sai abun ya mata yawa ta rasa da wanne zata ji.

     Itama ta riqe hannun sumayyan cikin kalamai na qarfafa gwiwa ta mara mata baya har zuwa dakin marya,babu laifi dakin ya cinye komai nata kasancewar yana da yalwa,kuma ba wasu uban kaya suka mata ba,tunda gaba daya sun daga hankali ne anyi bikin cikin matsatstsen lokaci ba tare da sun gama shiryawa ba su kansu.

   
       Gefe daya suka samu suka zauna,sumayyan ta gaidasu daidaikum cikinsu suka amsa,maman nana kam babu wanda ta duba cikinsu don dama darajar sumayyan ya sanyata shigowa dakin,wata 'yar tsohuwa ce dake zaune gefan amarya wadda ta lullube fuskarta da mayafi tace
" to sumayyatu,ga 'yar uwa nan mun kawo miki,abokiyar zama,Allah ya baku zaman lafiya,muna fata zaku hada kanku ku zauna lafiya"
"Kowa ya kwana lafiya ai shi yaso ato,fa'iza dai gata nan zama daram ila yaumut takunu" yaya bara'atu ta karbe zancan daga gun tsohuwar,rai bace maman nana ta daga kai ta dubi yaya bara'atu,mamaki take bata,wai 'yar yarinyar da duka duka take cikin shekaru na sha takwas take zagewa babba da ita tana yadawa wadan nan habaice habaicen da suka girmi kanta,babu lallai ma kan nata ya iya dauka,ina laifi ma ta bar yaranta masu shekara sha hudu sha biyar su gayawa sumayyan?,wata qila ace wadan nan sine dai dai da ita,amma ba ita ba wadda ta kusa linka shekarun sumayyar ba.

      Ta tabbatar idan taci gaba da zama cikin dakin tabbas za'ayi batacciya da ita,bata so kuma wani abu na tsiya ya hadasu,tunda duk tsiya tafiya zasuyi ba zasu shekara ba,kuma gidan dan uwansu ta shigo sunci albarkacinsa,tunda mukhtar kowa ya shaidi halinsa,sai ta kama sumayyar ta miqar sannan ta ari bakinta ta ci mata albasa,don ta fuskanci ba zata iya magana ba kuka take qasa qasa kanta duqe
"Insha Allahu baba babu wata matsala,don sumayya bata da damuwa mu mun shaideta tun tana tatsitsiyarta muke tare da ita,zaman lpy an sameshi an gama da izinin Allah"
"To Allah ya yarda 'yar nan" cewar tsohuwar.

       Da sauri ta janye hannun sumayyan suka fice saboda ta soma ganin bakinsu yana motsi suna shirin fara qananun maganganu,sai data tabbatar sumayyan ta samu nutsuwa kana tayi mata sallama ta tafi,zuwa lokacin suma 'yan kawo amaryar suna qofar gida suna shirin tafiya.

      Sha daya na dare agogon falon nata ya nuna mata,gidan yayi shiru kowacce na dakinta,sauqinta daya akwai wutar nepa da ta haskake ko ina cikin gidan,ta sauke ajiyar zuciya tana ci gaba da jan hasbunallahu wa ni'imal wakil,har zuwa lokacin da taji an turo qofar gidan an shigo,sai ta miqe tsam a tsorace kasancewar basu taba barin qofar gidan nasu haka ba.

      Tana ji aka rufe qofa ta biyu hakan ya alamta mata cewa mai gidan ne,ta aauke ajiyar zuciya duk da cewa tana tsayen bata zauna ba.

      Da sallama ya daga labulen dakin idanunsa ya sauka a kanta,ta kowa yayi a hankali ya shigo dakin yana dubanta yadda tayi carko a tsaye,cikin sanyin murya yace
"me kikeyi a tsaye haka kamar wadda taga wani abun tsoro" ta saki ajiyar zuciya,muryarta a sanyaye tace
"Ji nayi ana taba qofa ne",murmushi yayi yana ajjiye ledojin hannunsa
" ke kam farar kura ce sumy"sai tayi murmushin yaqe tana kawar da kai,ta qarasa inda yake tana masa sannu da zuwa ya amsa yana zama kan daya daga cikin kujerun falon
"Hada min ruwan wanka sumayya" ta danyi sororo kamar tace wani abu sai kuma ta fasa tace to.

    Wanka yayi


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login