Showing 270001 words to 273000 words out of 364327 words
ta shiga wani hali" ta fada abun na tsumata,ci gaba sukayi da tattaunawa kowa na fadin albarkacin bakinsa,'yammata ne dabkowacce ke jin ta burunqasa,kowacce tana burin zamantowa suruka cikin gidan,wadda dukkansu sun kwana da sanin cewa a gurinsu babbar sa'a ce ka zama wani ahali na jini cikin gidan,ko yaya sha'ani yake na gidan basa wasa da shi,mutane ne masu son budawa da kuma babbar harka,idan kuwa suka iso gidan suna samun dukkanin yadda suke so,duk da kowaccensu mahaifinta ba baya bane shima,saidai hausawa sunce baba ma da babansa,kafi wani wani ya fika,haka Allah ya qaddari rayuwarmu,yadda da hakan kadai shi zai sama maka rayuwa mai cike da wadatar zucci,da kuma cikakkiyar godiya ga Allah bisa dukkan wani bigire da ya azaka,Allah kasa mu dace,ka bamu wadatar zuci wadda itace babbar wadata itace babban arziqin duniya.
Sannu a hankali suke takowa zuwa bangaren ummi,jifa jifa suna wuce mutane da suka yo sammakon zuwa bikin tun farkon satin,sanye take da abaya baqa mai zubin dinkin buba,ta yane kanta da mayafin rigar,yayin da yake sanye da qananun kaya shirt da trouser baki daya shima baqaqe,zo kaga wani kyau da sukayi,musamman da yake riqe da hannunta saboda yadda ya lura akwai yawaitar 'yan sanya idanu,takanji wani nauyi duk sanda ta tuna yadda ya ritsata awa daya da suka shude a toilet daure da towel tana shirin yin wanka,yana jaddada mata wajibcin yin wankansu tare fuska daure,saidai baki daya yanayin da ya ganta ya sakar masa da jiki,ya zuba masa kasala da wani irin feeling a jikinsa,yayin data yayibi wani towel din ta rufe kanta hakan ya tunzurashi ya dinga takowa inda take har ya qureta a bango
"Yau zaki san kinyi kuskure,me kike boyemin" ya ambata yana dauke towel din dake kanta,gashinta ya bazu zuwa kafadarta,abinda ke sake burgeshi da tafiya da shi kenan,baya ta sake ja taha qoqarin boyewa cikin jacuzzi,cikin sa'a ya samu nasarar danqo ta,idanunta suka fito ganin yana niyyar sanyata cikin bathtube,tsoron dama yake son gani cikin idanunta,wani abu daban take koma masa mai kyau,bai bari ba kuwa sai daya sanyata sannan ya soma rage kayan jikinsa
"Saiki jira na gama nawa wakan sannan kiyi naki tunda baki son muyi tare sannan kuma cikin toilet dina kike ba naki ba"
"Amma ka bari na fita idan ka gama na dawo"
"Is too late" ya fada ko a jikinsa yana tubewa abinsa,idanuwanta ta runtse sanda yake qoqarin cire bixer din da shi kadai ya rage,sai qyarma take,bata taba ganin jiki mai lullube da siffar qarfi haka muraran a gabanta ba,gargasar jikinsa kawai abar kallo ce,karon farko data soma ganinsa a hakan,ko a jikinsa ya kammala wankansa tas sannan ya nade jikinsa da towel ya fice.
Dawowa tayi daga duniyar data tafi sanda taji yana matsa hannunta,tuni sun iso qofar falon ummeen ita yake jira ta cire takalmanta,a nutse ta zaresu sannan suka sanya kai ciki,shi yayi sallama yayin da suka jiyo muryar ummee tana amsawa,kunya da nauyi suka cika sumayyan,kamar ta koma bayanshi ta boye haka ta dinga ji,tana qoqarin zame hannunta dake cikin nashi amma yaqi bata dama,saima rada daya soma yi mata
"I want to show them i care with amanar da suka bani,nasan haka ne so ya kamata suma su gani,sai suyi alqalancin waye ya kasa kula da tashi amanar ko?" Sunne kai tayi ganin idanun ummee na kansu,fuskarta dauke da murmushi da kuma mamaki,don ta taji yara na fadin zuwan nashi bata yarda ba,don an riga da an saba,yawanci sai ana ya gobe daurin aure yake zuwa,wani lokaci ma sai ran daurin auren,awa daya kafin a daura ko minti talatin,musamman idan na yaran 'yan uwa ne,suma sai na kusa saboda tsabar busy,amma yau sai gashi kwanaki shida saura a daura auren,wannan wane irin gagarumin canji ne haka ke tunkarar rayuwar yaron nata,bata gushe ba tana musu barka da isowa fuskarta tamkar gonar auduga,yayin da eesha dake gefe bata daga kai ba tana danne dannen waya har sai da taji muryarshi,karaf idanunta suka fada kansu,zumbur ta miqe tsaye tana rarraba idanu,kada dai ace ta fara samun matsalar idanuwa,wannan yarinyar ya aura?,ko daga bacci ta tashi duk sauyawar da taji da samun cikakkem hutu dake kwance a jikinta ba zata manta ta ba,haka kawai yarinyar ta tsaye mata a rai
"Mutanen UAE" haka ummin ke fada wanda wannan kawai ya isheta amsa,sai ta hau girgiza kai ta shige dakin da ta sauka da gudu,sai sannan hankalin ummen ya kai kai,takun gudunta yaja hankalin almustapha da ya kai sumayya har gaban ummee,kunyarta ta sake burgeshi karo na biyu musamman sanda ta zame daga samn kujera zuwa qasa gaban ummeen,abinda bai taba gani kenan ba wajen su'ad,yana zama kujerar dake daura da ummin yace
"Waccar fa?,sunzi zasu fara haukar nasu kenan ko?"
"Kai kuma kazo zaka fara kenan ba"
"A'a ummi ni ban da case da kowa,just su kiyaye rules din da na sawa zuwansu gidan nan"
"Allah fa ya kawo mu,amiran umman khalipha ya fama da wannan" ta fada tana duban sumayya,alamun qarfi taba ga mai qiba,daga yanayin fuskar almustapha kawai ya isa ya sanar mata akwai gagarumin sauyi daya fara nasar rayuwarsa,yanayinsa baki daya akwai sauyi koda shi din bai san ko ya lura da hakan ba,kunya ta sake kamata tayi qas da kai tana gaidata,ta amsa cike da kulawa da farinciki,shima tashi gaisuwar ya dora ta amsa cikin jin dadi tana tambayarsu ya suka baro dubai
"Sai kuma gaku tun yau?" Ta tambaya cikin mamaki,satar kallonta yayi wanda ummin ta kula da haka
"Eh ummi,akwai wani aiki da nakeson yi,shi ya taso ni dole,tunda naga yayi daidai da date din daurin auren" ta fahimci salon magana ce kawai ta qwatar kai,tunda da aiki ne da tuni ya shaidawa baba,amma ko baban baisan da zuwanshi ba.
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
[23/02, 11:52] Beesama Zamani Wrt Grp: ✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
8⃣7⃣
*Bismillahir rahmanir rahim*
*SANARWA DA BABBAR MURYA*
*BA NUFIN MU CIN ZARAFIN WANI KO BATAWA WANI BA,SABODA GUDUN RUBUTA MUNANAN AYYUKA CIKIN LITTAFIN AYYUKANMU,WANDA SAI MUN TSAYA GABAN UBANGIJI MUNYI BAYANI RANAR GOBE QIYAMA,AMMA TURA TA KAI BANGO,AN FARA SHIGA SHINGENMU ANA MANA BARNA,BAYAN MUN KAME KANMU DAGA DUKKAN WANI ABU DA ZAI ZAMA SHIGA HURUMUN WANI BATANCI KO CIN ZARAFI A GAREMU*
*GAREKU MASU SATAR FASAHA ZANCE KO BARAYIN ZAUNE*
*Ina mai shaidawa duk wani mahaluki da yasan cewa yaci da gumi na,ya dauki wani littafi nawa da na zauna na bata lokacina na rubutashi da hannu na don al'ummar ma'aiki su amfana,MALLAKINA ya kaishi wane waje ya saida yana zuba kudin a aljihunsa cewa NI SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA BAN YAFE BA,BAN YAFE BA,BAN YAFE BA,KUMA INA ROQON ALLAH YAYI MIN SAKAYYA KAYANA DA AKA DAUKA ANA SAIDAWA*
*GAREKA KO GAREKI BARAUNIYA A OKADA,DUK WANDA YA SANSHI KO YA SANTA YA ISAR MASA/TA*
*ABADAN DAYA SATA KOTA SATA,AKA KAISHI OKADA ANA SAIDAWA AKAN KUDI NAIRA DARI BIYU,NACE ALLAH YA ISA BAN YAFE BA,INA ROQON ALLAH KUMA YA FITAR MIN HAQQI NA MATUQAR BANI NA ZALUNCESU BA SU SUKA ZALUNCENI,TUNDA BAN TABA DAUKAR HAQQIN WANI MALLAKIN WANI NA MAIDA SHI MALLAKINA BA,ALLAH YA BIMIN HAQQINA,INA FATAR ZAKU SADAR DA WANNAN SAQO ZUWA GARESU*
*SANNAN WANNAN LITTAFI DA NAKE RUBUTAWA DAMA SAURAN LITTATTAFAINA,MALLAKINA NE,NA YISHI NE KYAUTA BA NA SAIDAWA BA,A DUK SANDA NAKE DA BUQATAR SAIDAWA ZAN SIYAR DIN,AMMA BAN BAIWA KOWA IZINI YA SIYAR MIN BA,WANDA KUMA YAYI HAKAN NA BARSHI DA FITOWAR RANA DA FADUWARTA,NA BARSHI DA MAI SAMA,MUGA ALFANUN DA ZAI SAMU CIKIN KUDIN DA KA SAMU TA HANYAR SAIDA ABUN SATA*
*WALLAHI WALLAHI ALLAH MU GUJI CIN HAQQIN WANI,BILLAHILLAZAI LA ILAHA ILLA HUWA DUK WANDA KA GANSHI RAN QIYAMA YA QETARE TO BABU HAQQIN WANI A KANSHI,WANNAN ALQAWARI NE NA UBANGIJI,SAI YA FITARWA DA DUK WANI BAWA HAQQINSA KAN DAN UWANSA,KODA DABBA CE TA ZALUNCI 'YAR UWARTA DABBA*
*ALLAH KASA MU DACE*
_____________________________________
ta fahimci salon magana ce kawai ta qwatar kai,tunda da aiki ne da tuni ya shaidawa baba,amma ko baban baisan da zuwanshi ba,koma meye tana maraba kuma tana fatan alkhairi da samun wannan kyakkyawan canjin,sai ta saki murmushi
"Masha Allah" ta fada tana maida dubanta ga sumayya
"Me zaku ci,ko zaki shiga kitchen ki sama muku ko snacks ne,yau duka ma'aikatan na can baya suna aikace aikace suma"
"Am ok ummee" almustapha ya fadi,farinciki ya mamayetq,ta tabbata tunda ya fadi hakan hakanne,sai ta waiwaya ta dubi sumayya
"To kefa amira?"
"Nima ummee na......"
"Qarya take,ba abinda naga taci tunda muka taho" almustapha ya katseta yana tsareta da ido,murmushi ya subucewa ummee,salon da bata taba gani wajen almustaphan ba yau sai gashi da shi
"Maza shiga ki samu wani abu kici,halan shi kin sama masa wani abun yaci ke baki ci komai ha ko?" Cikin kunya tana murmushi ta miqe kanta a qasa tayi kitchen din,yayin da ya bita da kallo yana yabawa salon kunyarta,yanayin yadda take ganin girma da darajar mahaifansa,tunanin yadda cikin qan qanin lokaci kan ya gama shiryawa ta hada misi wani hadadden patatoe salad ya fado masa,ya jima baici hadin salad da ya masa dadi irin wannan na,murmushi ua dan qwace masa,yanayim takun ta na burgeshi,ya dauke kai sanda ta kai ga shigewa kitchen din,sai suka hada ido da ummee,shi yai qasa da kai kunya na lullubeshi,ita kuma ta dauke kai tana sakin murmushin tsantsar farinciki,waskewa yayi da cewa
"Ummee ya adam bai qaraso bane?"
"Ka fadi haka mana tunda wannan karon ka rigashi zuwa,ina zaton sai wajen laraba zai qaraso,amma dai ni'ima ya hadato da yaran sunyo gaba,dazun da safe suka sauka,shi da fahariyya sai ran laraban"kai ya gyada cikin gamsuwa
"Kunje kun gaida maamaan ne?"
"A'ah"
"To bari ta fito sai kuje ku gaisa,da alama itama batasan da zuwan naka ba,babanku kam baya gari,ya tafi jigawa ta'aziyyar wani abokinsu da ya rasu,amma gobe ma zaya dawo" ta fadi tana daga wayarta dake ringing wanda amira ce ke kiranta,bayan sun gaisa take shaida mata zuwansu sumayyan,ihu ta saki har almustapha dake zaune yana jiyota,hararar wayar yake kaman amiran ma wajen,magiya ta dinga kan ummee ta bata sumayyan ta kira wayanta a kashe,dai dai sanda sumayyan ke fitowa daga kitchen din,ummi ta miqa mata wayar,a ladabce ta amsa ta koma gefe tana fidda murmushi,addu'a kawai take kada amiran ta baro zance ta bata kunya,ai kuwa zuba ta hau yi
"Amma namecy kinci amanar qauna da baki gayan har kin iso abuja ba,halan soyayya ta fara zaqi har kin soma mancewa da kowa sai wannan miskilin mijin naki,ina fatan kina bada wuta wajen sukurkuta masa shi muga ta tsiya,tab ai wallahi jibi nima zan taho Allah,ina fata kin samo mana tsaraban baby,wallahi har so nake naga babynku,kyau tako ina,wazai dauko uwa ko uba?,wa yaga ya man ya baby" gaba daya kunya ta cika sumayyan,yadda almustapha kadai ya kafeta da ido tasan yanajin komai amiran ke fada,ta sanshi sarai da kaifin ji,yunqurin datse kiran take sai ya miqa mata hannu,a hankali ta tako ta miqa masa wayar,ya kara akunnensa sanda amiran ke cewa
"Wayyo soyayyya zamu sha kallo......"
"Gidanku mara kunya fitsararra,idan naga qafarki gidan nan jibi sai na karyata na zubar,idan kin musa kuma bismillah" ya datse kiran,daga bangaren amira sai ta kwabe fuska zata sanya kuka,saifullah dake zqune gefanta ya dunga tiqa dariya har da qwarewa da lemon da yake sh,haushi ya sanyata daukan filo ta dinga maka mishi shi kuwa yana fadin
"Maganin aku kuturu mai shegen zance kenan,tun dazun nake kwabarki kiyi a hankali may be suna tare amma kika qi ji,tunda kuwa ya man ya fadi haka ke da zuwa gida sai ana gobe daurin aure"kuka kuwa ta sanya taba buga qafa
"wallahi wallahi ban yarda ba,don kawai kaji ya almustapha ya fada ko?"sai ta saki filon ta wuce bedroom alamaun taji haushi ya miqe da sauri ya bita domin yayi lallashi.
Boye dariya ummin ta shiga yi tana basarwa,don itama taji wani abun,sauka yayi daga bangaren kira ya shiga wajen adana lambobi,da dai dai ya dinga bi har ya iso wajen lambar da ya tabbata tata ce saboda ga hotonta nan saman lambar,ya dauki wayar shi ya kwashe lambobin ya adana a tashi wayar,ganin yadda kunya ta rufe sumayyan yasa tace
"kuje ku gaida maamaa,daga nan ku wuce sashenku sai da safe ma hadu"
"To" ya fada yana sauke qafarshi wanda ya dora daya kan daya ya miqe ya isa gefan ummin ya ajjiye mata wayarta
"Sai da safe ummee" suka hada baki wajen fada sai da ya waiwayo ya dubeta,dauke kanta tayi ummen ta amsa
"Sai da safe,Allah ya bamu alkhairi".
Kusan bangaren anty maamaa wannan karon yafi jama'a,hakan baya rasa nasaba da kasancewar ita keda bikin wannan karon,auren yara biyu tak duka maza da Allah ya bata,baki ta kama itama
"almustapha?,tun yanzu?"murmushi kawai ya saki yana fatan kada ta sake cewa wani abu saboda 'yammatan dake falon,bai ko zauna ba hannunshi zube a aljihun wandonshi ya soma gaidata,ta amsa cikin farinciki itama,don ta tabbata lallai hasashen baban ya soma zama gaskiya,tunda ga mustpha ya waiwayi gida ana daurin auren qannenshi saura kwana shida,sumayya kam tuni tana wajen humaida,wadda sukayi farinciki ganin juna,ya waiwaya bayan sun gaisa,ganinta wajensu ya sanya ya basar ya juya ya fice,cikin sakewa suka gaisa da anty maman tana dan tsokanar sumayyan kafin ta miqe ta fice ta basu wuri,ta sake sosai cikinsu humaidan aka dinga hira,abinka da mata gwanayen gulma,kusan kowa kallon sumayyan yake,kowa da irin gulmar dake cinsa arai,yayin da dama daga cikinsu ke jin dama sune sumayyar,a qalla sai gashi sun kwashe wajen awa daya suna shan hirarsu,don humaida har kiran amira tayi ta saka handsfree aka dan taba da ita,hakan ya sake tsokalota taji kamar tayi tsuntsuwa ta taho.
Tun da ya shigo yaje duba agogo yana kasa kunne amma yaji shiru,har ya kammala shirin kwanciya cikin wasu hadaddun pyjamas masu shegen kyau da suka haska shi,yana son ya daure ya basar amma sai zuciyarsa ta gaza,a hankali ya sauko ya soma takawa ya sauka qasan benen,ya bude dakunan baccinta bai ga alamun ta shigo ba,ya koma sama ya bude dakin baccinta dake sama nan ma babu alamun an shiga,dakinshi ya koma ya zauna gefan gado yana son samin meke sanyashi damuwa haka da lamuranta?,laluba lambarta fake cikin wayrsa wadda yayi servinn dazu yayi sannan ya shiga bangaren aikawa da saqonni ya tura mata gajeran tex
"Come back", suna tsaka da hiransu saqon ya shigo,sai abun ya daure mata kai kasancewar bata da lambarsa,daga bisani ta ajjiye wayar tana zaton batan kai saqon yayi ba wayarta zai shigo ba,mintina goma suka shude shiru,ya sake lalubo lambar ya kira,bugu kusan uku sannan ta daga ta kara kunnenta,yana iya jiyo hayaniyar su ta cikin wayar,haka kawai tasha jinin jikinta duk da batasaj number din ba
"Assalamu alaikum" ta furta a nutse,har cikin zuciyarsa sallamar ta ratsashi,cikin zuciyarshi ya amsa a fili kuma yace
"Bance ki dawo gida ba?" Ta fahimci muryar sarai amma sai tace
"Waye ke magana?"
"Ok,baki gane ba kenan?"
"Eh" ta fada tana sani
"Well" ya ambata shima yana katse wayar,sai ta ajjiye wayar yana qoqarin saukowa daga saman gadon.
Anty maamaa ce ta sauko daga sama tana duban sumayya
"Lalala amiran umman khalipha?,me kike har yanzu baki wuce gida ba?,ya zaki baroshi shi kadai waya gaya miki ana wannan sakacin,tashi ki wuce tun bai biyo sawunki ba wallahi" ta fadi don tasan halin mustaphan sarai,murmushi ta saki yayim da su humaida suka sanya dariya,humaida tace
"Allah sarki mu da yake warin takalmi muke mu kwana muna hira ma ko anty"
"Yo wa ya damu da ku?", ta fada tana juyawa sama tare da yiwa sumayya sallama,dif dariyansu ta katse baki daya,kowa ya kama kanshi,hakan ya sanyata dagowa,sai ta ganshi tsaye cikin kayan bacci,takowa ya dinga yi a nutse har inda take sandare a atsaye,yasa hannu ya zare wayarta dake hannunta ya dauke cak,baki daya 'yammatan sukayi mutuwar zaune na wucin gadi har ita sumayyan,ko a jikinsa ya juya dauke da ita ya fice daga falon.
Kallon kallo aka soma yi tsakaninsu,humaida ce ta soma tuntsirewa da dariya,abun ya matuqar burgeta,kamar a fina finan india
" to wallahi tunda guy din nan ya soma haka mu rufawa kanmu a siri mu dinga kora masa matarsa da wuri,idan ba haka ba wataran sai munga abinda idanuwanmu ba zasu iya dauka ba"
"Wai shi dan air ba" inji wata daga cikinsu,wadda a zahirin gaskiya hassada take ji cikin zuciyarta,don itama taso ace ta zama daya daga cikin matanshi
"Ba wani dan air wallahi,har ga Allah abinda ya sanya nakesom auran irin mazan nan,nuna so babu limit ko a gaban waye wallahi,wani miskilin namijin bai iya nuna miki qauna ba,idanunshi basa gani balle suji kunyar kowa" dariya suka sanya suka ci gaba da tattaunawa kowa na fadar albarkacin bakinshi.
Bai direta ba sai da ya saita mata hanyar matattakala,ya harde hannunshi yana mata nuni da idanu kan ta hau,babu musu ta haura saman kunyar abinda ya mata cikin jama'a na kama ta har cikin dakinshi,qofa ya maida ya kulle ya waiwayo cikin shammata ya turata saman gadon,baki daya ya danneta,ya dora mata nauyinshi,fuskarsa kawai ya dago yana dubanta,idanunshi cikin nata suna musayar numfashi,sosai ta gane kuranta,numfashinta ya soma mata nauyi
"Qirjina ka daga ni"
"Eh ai so nake na nuna miki banbancin,don na lura kin soma rainani saboda kinga makwancina.....me kike gayawa amira take rawan qafan zuwa ta sameki?,sannan me kike gayawa wadan can shashashan suke babbaka dariya kaman hauka sabon kamu?" Narai narai tayi da idanuwa,yatsansa ya dora saman lebansa yana fadin
"Shshshshsh,banson wani kuka,idan kuwa kika sake kikayi yau tilldown zanyi sai an miki ruwan zafi"cikin taushin murya a shagwabe da son qwatar kanta tace
"Allah babu komai ka yarda dani"sosai ta masa kyau,shagabarta ta taba zuciyarsa qwarai,murmushi na son qwace masa amma ya dake,bai son ta gwada abinda su'ad taso dauka dabi'ar yi,wato kwarzantashi da yabonshi da fadan qwarewarshi a kan shimfidarsu gurin qawayenta,randa kunnensa ya ji masa Allah ya sanya ranar ta soma,mutum biyu ta gayawa,ranar taga tashin hankalin da bata taba gani ba,don cewa yayi tunda ta gaya musu to ta sa a ranta sai ya auresu babu fashi,har ciwo sai da yaso kamata,babu