Showing 207001 words to 210000 words out of 364327 words

Chapter 70 - KUNDIN KADDARATA COMPLETE HAUSA NOVEL

HUGUMA   

20 Aug 2024

40135

dan tsokaneta
"Abdallah kam anyi wuyar gani anyi sabon daddy" murmushi kawai ta danyi ta basar.

       Wani qayataccen event center suka kama,hmmm masu abu da abinsu,kada kaso kaga yadda gun ya qawatu yayi matuqar tsaru,ranar sumayya anyi abun gani,ita ta zauna mazaunin babbar qawar amarya,tayi komai yadda zata faranta ran amiran duk da a takure take matuqa,idanuwan maza bisa kanta sunyi yawa,kai har ma wasu daga cikin matan,sai da guri ya gama tumbatsa sannan su'adah ta iso,a nan tayi burgar data saba,tsakiyan abokan ango cikin dinkim riga da skert na wani shegen leshi mai azabar tsada wanda aka ci mutuncin tsadar tasa aka yi masa dinki na ganin dama,tsagar skert din har kusan gwiwarta,dinkin ya kamata dam,banda dankwalin da aka tsarawa dauri babu komai a kanta,don ko tuna sunan mayafi bata yi ba,liqi ta shiga yi da 'yan dubu dubu sabni kar wanda ita kanta bata san nawa ta barar ba,abin nema ya samu ta dauki idanuwan jama'a,ta kuma qona zukatan 'yan baqinciki wadanda bas son tarayyarta da mustapha,to su gani ya tsaya mata,sai data yi mai isarta sannan ta sauka daga step din ta koma mazauninta.


Sai sha daya na dare aka tashi kowa ya koma inda ya fito.

*******    *******    ******

        Tun qarfe goma na safe layin nasu ya tumbatsa ya dinke da jama'a kasancewar goma da rabi ne daurin auren,bacci ranar tayi sosai dakin anty dije,bata tashi farkawa ba sai qarfe tara da rabi na safe,tarin missed call ta taras duka na amira,da hanzari ta miqe ta fada toilet tayi wanka,a gurguje ta fito ta shirya cikim shaddar da sukayi anko wadda tayi masifar haduwa,kamar yadda dinkin doguwar rigar ya dace da jikinta,komai da tayi amfani da shi kalar zaren da akayi aikin shaddar da shi ne,ta fito fes mashaAllah,daidai sanda laila ta shigo,baki ta sake tana kallon sumayyan,ta qaraso dakin ta samu bakin gado ta zauna
"Wai dama don Allah anty sumayya haka kike da kyau" dariya yarinyar ta bata saboda bihaqqi ta fada
"Sai an tambayo" ta fadi hankalinta ka can gidan baba,saboda hayaniyar data dinga jiyowa na tashi ta tabbatar layin yayi tumbatsar da babu damar ta fita,valcony din saman benan anty dije ta bude ta fita ciki,layin ya shaqara da mutane ya cika masha Allah,kai ta dinga kadawa don tasan dole ta haqura har sai an ragu.


Kujeta ta ja ta zauna daga gefe yadda zata iya hango komai,ta bude wayarta ta soma lalubar lambar amira don ya bata uzurinta,hakanan taji yana yinta ya soma sauyawa kamar ba ita daya bace a gun,kamar fisgar mayen qarfe haka idanuwanta suka jata zuwa inda yake tsaye tsakiyan wasu zaratan samari kamarshi.









*mrs muhammad ce*👑

📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
[23/02, 11:51] Beesama Zamani Wrt Grp: ✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖


*~NA~*

*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*

*WATTPAD:HUGUMA*

*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)



7⃣2⃣


*Bismillahir rahmanir rahim*

*ALLAH YANA GAFARTAWA WANDA YASO YA KUMA AZABTAR DA WANDA YASO*

YA ALLAH KA GAFARTA MANA
___________________________________

*TAB,BIGI SAI BIGI,BABBAN GORO SAI MAGOGIN QARFE,IDAN KAJI WANE BA BANZA BA,INA MA'ABOTA KARATUN LITATTAFAN HAUSA,KAMA DAGA NA QUNGIYAR HASKE HARMA WANDA BA NA HASKE BA,SHIN KUNA DA BUQATAR JIN WANI SABON KUNDI WANDA YA TATTARE LABARAI NAU'IN DABAN DABAN WADANDA SUKA SHAFI AL'AMURA NA ZAHIRI DAKE FARUWA CIKIN RAYUWARMU TA YAU DA KULLUM?.......TO MAZA KU GARZAYA KU NEMI LITTAFIN KUNDIN HASKE,WANDA KE QUNSHE DA LABARAI DAKE DAUKE DA NAU'IN RAYUWA IRI DABAN DABAN,LABARAI NE WANDA KE DAUKE DA DIMBIN DARUSSA MASU RATSA ZUKATA,DUMBIN ILIMI MAI JAWO HANKALIN DAN ADAM ZUWA SAKE LURA DA GYARAN RAYUWARSHI,MAZA KA/KI GARZAYA KADA A BAKI LABARI,BA SHAKKA ZA'A CI DA RABONKI MATAUQAR KIKA BARI YA WUCEKI,AKWAI SHI A WATSAPP DA APP DIN WATTPAD BAKI DAYA*


*SADAUKARWAR WANNAN SHAFIN GA:*

*SADIYA ZABURA*
*UMMU RAMLAT*
*MAMAN SAYYID*

*DA MARUBUCIYA*

*AYSHA DAN SABO*

*RABBI YA BAR QAUNA*🤝🏽🤝🏽🤝🏽🤝🏽🤝🏽😍😍😍







       Kyawawan idanuwanshi wanda suka wadatu da gashin idanu kamar yadda girarsa take masu kama da na wanda ke jin bacci suke kan ta,shi daya ne tak sanye cikin qananun kaya sabanin dukka sauran wadanda suke tsaye tare,baki dayansu shadda ce jikinsu dinkin tazarce kaloli daban daban,kusan tare suka janye idanuwansa,gabanta ya shiga faduwa,kasa zaman wajen tayi,batasan ana iya gajin mutum ba,gashi ko mayafi babu a jikinta,sai ta miqe jikinta na rawa gabanta na faduwa ta bar wajen,ta tura qofar ta kulle ta dawo cikin bedroom din anty dijen.

      Gefan gado ta kwanta rub da ciki tana sauke numfashi,maganganun baabaa suka soma dawo mata,har yau ta kasa gane me yake nufi,tana da buqatar qarin bayani,tana buqatar taimako wajen wanu ko zata fahimci me yake nufi,amma ta taimaka masa wajen gyara rayuwarsa kamar yaya kenan,wanu mummunan abu yake mara kyau yakeso ta saka baki?,amma ita a wa?,bata da wannaj power din,ganin qwaqwalwarta na neman daurewa yasa ta kada kai tare da yin watsi da maganar,maimakon ci gaba da tunani sai ta sake daukan wayarta ta lalubi zainab ta kirata,din jiya suna wajen dinner taga misscall dinta baya kuma samu ta bita ba.

        Bayan sun gama gaisawa da mama ta musu Allah ya sanya alkhairi zainab ta karba,nan take gaya mata jiya aka kawo lefe sati uku kuma aka sanya,murmushu sumayya ta saki tana tsokanarta
"Kice mu fara shirin tahowa kano ko?"
"Wallahi yaya,kizo ayi tsare tsare masu kyau"
"Insha Allah,ina huce gajiyar wannan bikin zaki ganni,Allah ya nuna mana da rai da lafiya"
"Amin yaya,ina abdallah na"
"Uhmm,ni kaina bansan ina yake ba,yana gidan biki"
"Ki gaisheshi tunda ya manta da mu" dariya ta danyi
"Zaiji,ki gaidan halimaty,wayarta bata shiga"
"Zata ji" suka katse wayar.

       Tana sauke wayar ta jiyo muryar abdallah yana karadi daga qasa shi da sh hafiz,sauka tayi daga gadon ta sauko qasa,yayi masifar kyau cikin wata arniyar shadda ash wadda batasan inda ya samota ba,hulace kanshi zanna wanda sau faman zuba qyalli take,qafafunshi saye da takalmi sau ciki,abinka da uwa da da,yana ganinta ya tako da gudu ya daneta,murmushu tayi ta zube saman kujera yana faman zuba mata surutu da bata labari.

        Ganin sha daya tayi ga gidan babu kowa sai ita ya sanyata yin shahada ta yafa mayafinta ta fito,kamar zata nutse haka ta dinga ratsa mutane a darare tana wucewa har ta kai ga cikin gidan bayan ta kira humaida ta gaya mata inda suke,ko ina harabar gidan 'yan uwa da abokan arziqi ke kai kawo,kowa ka ganshi cikin kwalliya da walwala,daga gefe guda ta hango mahmoud da tarin abokansu ciki har da alqasim,suma sun ganta saboda haka ta qara sauri don kada su rusketa.

       Batayi aune ba sukayi karo kanta ya daki qirjinsa,tayi taga taga ta komo ta fada qirjinsa,zuciyarta kamar zata fito saboda tsoro,tayi yunqurin janyewa,ta samu nasara saidai hannunta na cikin nashi hannun yana duban qwayar idanuwanta,sai yanzu ya samu amsar inda ya samu qamshin da ya buwayeshi tun shekaran jiya,wanda har kuka su'adah tayi sabida jin qamshin,don ta tabbatar hadin humra ce ta mata ta musamman ba turaren namiji bane,gaba ta tusashu tana tambayarsa ina ya samu turaren,baki daya zuciyarta ta gama zayyana mata yana neman wata ne,idan banda haka ina zai samo turaren mace a hannunshi?baya ga haka ta lura wannan karon sam baya marmarinta,baya nemanta idan ba ita ta buqata ba,bayan a baya ta sani cewa duk sanda suka hadu har sai ta gaji ta hada kayanta ta gudu yake qyaleta,amma wannan karon sam ba haka bane,yana jinta yayi mata banza ya gama shirin baccinsa ya kwanta tare sa juya mata baya,don bashi da amsar bata,shi kansa yana jin qamshin cikin hancinsa amma baisan inda ya sameshi ba,baijin zai iya bata lokacinsa ya mata wannan bayanin tunda har tana zarginsa,to ta dauki duj hukuncin da take gani zata iya dauka,hakan ya sake hassala zuciyarta,itama ta shiga fushi da shi gadan gadan miqe ta fice ta sauya dakin kwana,bata san cewa ba shi ta yiwa ba kanta ta yiwa,tunda ba yau farau ba da yake kwana shi daya tamkar gauro,idan da sabo ai ya saba.

       So take ya sakar mata hannu ko don idanuwan mutane da ke kai kawo a wajen,uwa uba ga haramci na riqe mata hannu da yayi,tayi yunqurin zame hannun nata amma abu yaci tura yana tsaye qyam yana dubanta,babban goro sai magogin qarfe,ya kusa lullube tsahonta baki daya,dududun nata tsawon bata fi iya qirjinsa ba,ga wani kwarjini daya cika wajen,ganin masu wucewa sun soma ankara ya sanyata cewa
"Ka sakar min hannu" cikin izza da motsa labbansa
"Saikin gayan abinda ke baki tsoro,me ya koroki bayan kowa na kai kawo a nutse amma banda ke?" Daga fararen idanunta tayi ta watsa mishi su,duk da yadda qirjinta ke bugawa,lumshe idonsa yayi ya bude ya janye nashi idanun daga kallonta,bai taba ganin mace mai farin qwayar idanu ba kamar haka ya raya a ransa,tsaki yaja a fili sannan ya saki hannun nata
"Ki kula next time,ban son irin wannan shirmen" ya fada yana duban gefanta,ita ke shirmen ma?,abun ya bata haushi,sai ta banka masa harara ta gefan ido duk da yadda gabanta ke faduwa qasa qasa tace
"Kaima sai ka kula tunda kana da idanu ai ba ni kadai ke da idanuwa ba" batasan tayi kuskure ba saboda kaifin ji da Allah ya hore mishi,ko yaya magana take yana iya jiyota,yana daya daga cikin wadanda Allah ya yiwa baiwar ji,har wani lokaci ba'a iya gulmarsa matuqar yana cikin gidan,har yayi gaba ya juyo a mamakance yana dubanta,karo na farko kenan da wata 'ya ta taba maida masa magana,bakinta ta murguda duk don ta sake bashi haushi tayi gaba abinta,wani abu ya tsaya mishi a rai,ranshi ya baci,yau shi akewa rashin kunya?,abinda yafi tsana kenan a rayuwarsa tun lokacin quruciya,abinda ya fara hadashi kenan da su'adah tun tana qaramarsa,lallai zaiyi maganinta,wace ita da har take jin karanta ya kai tsaiko,babu shakka sai ya hukuntata.

      A bangaren anty maamaa ta tadda su,tana zaune tsakiyar yayunta anty farida da anty huda da matan yayyen ta ni'imah da fahariyya,sai qawayenta da cousins dinta irinsu eesha humaida ummu salma da sauransu,a hankali ta qaraso saboda lasalar da take ji cikin jikinta tana karbar saqon harara daga amira,duk da haka murmushi ne kan fuskarta,ta riga da ta sani itace mai laifi,sauran da suka san mekw faruwa dariya suka dunga yi sunsan za'a kwashi daramer,amma sai sumayya ta kashe mata gwiwa da fadin
"Ta zama ta saifullahi,ayya yarinya zata bar gida" ai kuwa sai ta soma qwalla,tana dariya ciki ciki ta qaraso ta zauna gefanta ra mata rada a kunne ma tsawon minti biyu,sau gani sukayi ta saki dariya tana share hawayen,huda ce taja tsaki
"Au qaryar banza,dama fa son aurenta take 'yar banza bansani bane,saifullahin da ake ji da shi kamar a lashe mishi mazaunai" dariya ta kamasu baki daya,dqi dai da dai dai sumayya ta bi ta gaida kowa,batasan matan yaya adam ba sai lokacin ni'imah da fahariyya,fahariyya ita ta fara tahowa ni'imah ta jira maigidan sai jiya suka taho tare da daddare,bata ga fahariyyan ba saboda 'yar jin kaice itama kamar yadda amira ke gaya mata,ni'imah din ce babu ruwanga,hakanan take haquri da halayyar fahariyya na goranta mata da take lokaci lokaci akan rashin haihuwa,saidai zaman nasu babu yabi ba fallasa,rashin mutuncin fahariyyar da sauqi sakamakon cewa adam din tsayayyen namiji ne,bai yarda a wulaqanta masa uwar gida ba,sam basa shiri da su'adah da fahariyya saboda kowacce na jin kanta da jin cewa ta isa saidai daya tabi daya,duk da a zahiri duk cikin yaran gidan babu wanda ke da dukiyat almustapha,wannan ya qara kishin su'ad cikin zuciyar fahariyya,itakam ni'imah 'yar babu ruwa na ce,ta kama mutuncin kanta,don iyayenta ba wasu bane rufin asirin Allah ke garesu,sai a yanzu da tayi dace da miji na qwarai suke samun sauyin rayuwa sanadiyyarsa,duk da haka dama tana da managartan halaye wadanda su suka fusgi adam zuwa gareta,duk da tarin yaran masu kudi dake sonshi a lokacin,ta kasance ta daban a gunsa har a yanzun duk da bata taba haihuwa da shu ba,sakamakon haquri biyayya da tsantsar iya zamantakewa da miji mai tafiyar da hankali.

        Da daidai suka miqe suka fice ya rage saga sumayyan sai anty ni'imah sai humaida,suma sun maqale ne saboda suna kwasar wasu sirrika da lacture da anty ni'iman ke bawa amira,wanda baga fara ba sai bayan da wadancan suka fita,ba amira ba hatta su sumayya sun qaru da ita sosai,a nan suka zauna suka ci gaba da hirarsu,ni'imah ba dai sauqin kai ba,kamar qannenta haka ta daukesu,aqalla zata girme musu da kusan shekaru goma,amma sam hakan bai wani nuna ba sosai sabida tsabar gayu.

      Qarfe bakwai na magariba aka tafi kai amarya,babu wani takura ko neman mota kasancewar kusan kowa ya mallaki motar hawanshi,wanda ya taho daga wani garin ne bai taho da abun hawanshi ba sukayi amfani da motocin gidan baabaa,ga kuma ta familyn saifullahi.

       Ba shakka wannan shi ake kira qwarya tabi qwarya,ba shakka amiran ta shiga gidan da yayi dai dai da ita,gidane na alfarma wanda ke tafiya da tunanin mai tunani,sanda aka fara tafiya amiran ta riqe sumayya gam kan sai ta jira anzo an sayi baki,sun riga da sun gama tsarawa babu batun siyan baki,ko akwai din ma ita batajin zata tsaya,saboda mutum biyu daga cikin abokan saifullahi da suka uzzurawa rayuwarta tun ranar kamu,ta musu qaryar a niger take,saboda haka bata son su hadu bare su takura ta,dabara tayi mata cewar bari taje tayi fitsari daga haka ta arto gida.

      Biki ya tashi lafiya,ummee da kanta ta yi ma sumayyan godiya tare da godiyar kayan humra data yi mata wanda su aka jerawa amiran ma,kunya ce ta kama sumayyan,duka duka me tayi,su basu duba tarin karamcinsu wanda ya kai ga cancantarsu kan yi musu komai.

       Tun a daren ta kashe wayarta kwata kwata,don ta tabbatar cewa gobe kamar da qasa sai amira ta nemeta,jikinta ya gaji tubus irin gajiyar da bata taba yin irinta ba,lallai biki ba wasa bane,tunda ta kwanta bata tashi ba sai da gari ya waye,ta makara sallar asuba,don sai shida da rabi ta yita,tana gamawa ta koma ta sake kwanciya,ba ita ta farka ba sai sha biyu saura na rana,yunwa ta sadakarta,a guje tayi kicin ta tadda anty dije na soya miya qamshinta ya cika gidan baki daya,ba magana ta mata nuni da kayan break dinta dake ajjiye gefe,tana kaiwa baki daya yiwa antyn sannu da aiki
"Ai ke zanwa sannu,yaran nan sunso tadaki badon ma hanasu ba,shi yasa da abbansu zai fita na hadasu da shi ya kaisu wajen inna(kakarshi)"
"Kai kina ji da ni anty na" ta fada tana jan kujera don ta ji dadin cin abincin sosai
"Ba dole ba,kece fa babbar diya" suka sanya dariya baki daya sannan suka ci gaba da hira suna tattauna wasu daga lamuran da suka faru yayin bikin,antyn na juye miyar cikin warmer tace
"Ai ke kam bakiga hutu ba,saura sati uku a shiga wani bikin"
"Wallahi anty shi yasa nakeso nayi kamar kwana uku haka ina bacci,don so nake next week na wuce kano" hararata antyn tayi
"Dama na sani ai,ke kam garin nan kamar yana mintsininki,gidan fa baki daya baya dadi wallahi idan kika tafi,hatta da abbansu ya dinga mitar kin dade,amma wani lokaci sai na rayawa a raina dole fa mu saba tunda wataran zaki aure,idan kika tafi kuma ya zamuyi" shiru sumayyan tayi taci gaba da kurbar tea,saboda anty dijen ta kawo zancan da bata qauna cikin hirar tasu,sai data gama sha ta sure cup din tana goge hannunta sannan tace
"Anty,wata tambaya ce da ni"
"Uhmmm,Allah yasa na sani" shiru ya danyi tana tsara yadda zata jefa mata tambayar kafin tace
"Wai idan wata ko wani yazo ya cewa budurwa ki taimaka ki gyara rayuwar wane,wai me hakan yake nufi?" Waiwayowa tayi ta kalleta har sai da gaban sumayya ya fadi,Allah yasa ba wani mummunan abu bane,kamar antyn ta tambayeta wa ya fadawa wani hakan sai kuma ta fasa,taci gaba da aikinta tana bata amsa
"Maganar na da ma'ana bangare biyu,nq farko idan har aka fadi haka ga wani ko wata makusanciya ta mutum ana nufin ta dinga bashi shawara da hanashi aikata wasu abubuwa,ko kuma wani abu na son faruwa da shi ana son ka taimaka kada ya fada cikin wannan abun,sannan ma'anar na iya daukan AURE ko SOYAYYA,abun nufi.......shi wanda ya gaya miki maganar yana ganin kamar kina da wasu qualities da wani namiji ke buqata,wanda wannan qualities din zau taimaka masa wajen gyaruwa ko ingantuwar rayuwarsa,babu kuma hanyar da zaki gyara ko ki inganta rayuwar tasa sai ta hanyar AURENSA ko yin SOYAYYA da shi,to sai a baka maganar a dunqule" tunda ta dauko maganar gaban sumayyan ke faduwa
"Da gaske baba na nufin kenan ta auri almustapha?,abinda baabaa ke son fadi mata kenan" kai ta shiga girgizawa cikin zuciyarta ta soma furta
"La haula wala quwwata illa billah,Allah ka sani ina ganin qima da darajar wannan bawa naka,ya Allah ka fidda masa wannan tunanin daga zuciyarsa a kaina,ka jefa masa tunanin wata,Allah kada ka bashi iko ya tambayi abinda bazan iya masa ba"
"Ke sumayya meye haka?" Inji anty dije ganin yadda take kada kai tana mus mus da baki,murmushin yaqe na musamman ta qaqalo sannan tace
"Ba komai,kawai ina mamakin yadda muka kasa fassarar maganar,wani ne ya gayawa wata" ta fada tana miqewa tsaye sannan ta fice daga kitchen din,da kallo anty dije ta bita,cikin zuciyarta tana addu'a,Allah ubangiji ya sanya sumayyan tayi gamo da miji ne dan gaske,wanda zata huce takaicinta,babu shakka zata so za kuma tayi burin sumayyan tayi auren da zata huta ta sanadiyyarta,juyawa tayi taci gaba da aikinta tana addu'a cikin ranta.

        A sanyaye ta zauna bakin gado maganar na sake y mata yawo,indai haka ne ba shakka dole ta qauracewa haduwar ta da baabaa,kai ya zame mata jazaman tafiya kano,kuma bata jin zata dawo nan kusa idan ta tafi din,zata yita qirqiro dalilai ne wadanda zasu zaunar da ita a can.

       A daddafe ta haqura ta kai ranar alhamis kamar yadda ta gayawa anty dije,sannan ta shirya tafiya,wanda ya rage sauran kwanaki goma sha hudu bikin,anty


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login