Showing 321001 words to 324000 words out of 364327 words
dan cikinta,d'an kuma wanda take iqirarin tana so,lallai dole ta sanya ido da takatsantsan da eeshan,don ba zata taba lamunta yaran da tun kafin ta haifesu su dinga shan wuya ba haka kawai ba tare da laifinsu ba,biyo bayanta ummin tayi,sai data sake tabbatarwa komai lafiya sannan hankalinta ya kwanta,saukowa qasa tayi,ta tara ma'aikatan dake kula da kitchen baki daya ta tsawatar musu,sannan taja kunnensu da kada ta kuma gani sun bar sumayyan ta shiga kitchen sannan ta sallamesu kowa ya koma muhallinsa bayan sun gyara gurin.
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖
*~NA~*
*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*
*WATTPAD:HUGUMA*
*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)
9⃣9⃣
*Bismillahir rahmanir rahim*
*Allah S W T yana cewa*
*duk wanda ya aikata daidai da qwayar zarra na alkhairi(komai qanqantarsa) zai gani(cikin littafin ayyukansa,zai ganshi a rubuce kuma za'a masa hisabi da hukunci a kansa),hakanan duk wanda ya aikata dai dai da qwayar zarra na sharri zai ganshi.
__________________________________________
Tun daga lokacin sumayyan ta zubawa eesha ido cikin nutsuwa,tana kula da takatsantsan da duj wanu taku nata,a bangaren eesha kuwa ko daya bata sauya qudurinta ba,ko da yaushe tunaninta daya na yadda zata illatar da sumayyan ne.
****** ****** *******
Qarfe goma da rabi ranan ta sauko bayan farkawarta daga bacci wanda kusan almustapha ne ya tasheta,sai data gama biye masa sannan ta shiga tayi wanka ta shirya ta sauko don ta karya,bata da damuwa tasan cewa komai na shirye,tun daga randa wancan abun ya faru bash sake barinta shiga kitchen ba.
Tare suka sauko da sajida,ummi na sashen anty maamaa,sajida ta wuce dining don ta karya,ita kuma kiran halima da ya shigo wayarta ya sanya ta wuce saman kujerun falon ta zauna tana amsawa,qarar sajida data jiyo shi ya sanyata sakin wayar ta miqe,bata jin nauyin jikinta haka ta nufi sajida da tayi zaman 'yan bori saman step na dining area,wajen ta isa tana dagata gami da tambayarta
"Faduwa nayi anty" ta bata amsa tana shirin sakin kuka saboda qafarta ta bugu sosai,idanunta sumayya ta kai wajen sai taga ruwa ne ya zube wajen
"Ya akayi kika zubda ruwa haka sajida?"
"Bani bace nima haka naga wajen,kuma ban kula ba har sai da na fadi" wani tunani ne ya darsu ran sumayya,ta sanya hannun ta cikin ruwa sai taji yana santsi da qanshin klien,to waye ya zubda ruwa haka?,tasan cewa babu yadda za'ayi ma'aikatan su zubda ruwan su tafi ba tare da sun gyara ba,ummi bata nan sajida ba ita ta zubar ba
"Eesha" zuciyar sumayya ta raya mata,kai ta girgiza,batason ta zargeta bayan bata gani da idanunta ba,riqe sajidan tayi don dawo da ita saman kujera,tana juyowa suka hada idanu da eeeshan,sai ta juya ta shige dakinta,mamaki ya kama sumayyan,wai me eeshan ke nufi,take ranta ya baci,ta zaunar da sajida saman kujerar ta kama qafarta tana mammatsawa,gefe guda ke mata ciwo,sai ta isa bakin dispenser ta tari ruwan zafi ta dawo kusa da sajidan ta gasa mata qafar sosai,cikin ikon Allah wajen ya saki,ta shafa mata man zafi a wajen sannan taje da kanta ta goge wajen sannan ta hada mata abin break din taci ta kwanta.
Tana saman kujera zaune kanta a qasa,ranta a tsananin bace yake,don me zata dinga neman cutar da ita?,tana tunanin dai dai gaggawar unguwar zoma ta bari a haihu ko?,ta bari su hada miji tukunna,meye na hanzarin son cutar da ita tun yanzun,saqar data dinga yi kenan cikin zuciyarta,qara qofar dakin eesha tayi,itace ta bude ta fito,tana tafe dai dai ta hura hanci,idanunta da suka kada saboda bacin rai ta zuba mata
"Aisha..." Ta kira sunanta cikin kakkausar murya wadda ta sanyawa eeshan tsayawa ta kuma juyo tana dubanta
"Jan kunne nakeso nayi miki na qarshe....duk abinda zakiyi kiyi qoqari ya tsaya iya ni,kada ki bari sarkarcinki da haukanki ya sake taba wani cikin gidan nan,yanzun da kin karya musu yarinya kuma kice me?,haka rannan kika watso ruwan zafi saura kadan a fuskar sajida,kina gidan kakanninta kina cin arziqinsu kina neman salwantar musu da jikoki?"maganar sumayyan ta qarshe ta sosa mata rai,ita zata yima gori bayan ita ya cancanci ta yiwa gori
"idan kuma banji jan kunnen naki ba me zaki iya diyar malamai masu ci da buzu da tawada?"murmushi ta sake mata sannan ta bata amsa cikin nutsuwa
"alhamdulillah da na kasance diyar malamai magada annabawa,zancan rashin jin gargadina kuwa....koni zan iya miki hukunci.....amma da yake ni din mai uwace a gindin murhu,kunnen mutum daya maganar zata je kiga yadda dunuyarki zata gigita" ta fahimci sarai tana son hadata da almustapha ne ko shi ko baba,to har gwara ma baban akan shi din,kuma ta sani sarai qarshen lamarin bazai mata da dadi ba
"Duk abinda zakiyi baki isa ki hanani shiga gidan almustapha ba wallahi,baare ma ya sameshi bare kuma na gida" murmushi ta kuma yi
"Kan me zan hanaki dama?,nima fa wata ta taras,sannan kuma ba kanku na soma zama da abokan zama ba,abu guda kawai nakeso daga gareki.....koda zaki auri almustapha to ki kiyayi taba lafiyar jama'ar da basu ji basu gani ba.....ki taqaita haukanki....ki adana shashashanki har zuwa sanda zaki shiga gidan nashi"tana yunqurin maidawa ummi tayi sallama,hakan ya sanyata dole yin shiru,bata ji ke suke fada ba taga dai sajida kwance
"a'ah lafiya kuwa?" Ta tambayi sajidan tana dubanta
"Ruwa ne ya zube sai na fadi" ta bata amsa,gefe ummin ta samu ta zawa
"garin yaya ruwa ya zube a wajen?" Ta tambaya cikin mamaki,wannan karon sumayya ce ta karbi zancan
"Wallahi ummi,sashen dai ba kowa,ni da ita kuma tare muka sauko sai ihunta kawai naji" waiwayawa ummin tayi tana duban eesha
"Aysha ya akayi ruwa ya zube wajen?"
"Nima ummi ban sani ba"
"Bake na bari wajen ba kina karyawa?" Sai ta langabar da kai
"Tea ne ummi,ina so ma goge kuma na mance naje na kwanta"
"Amma ya kamata ki dinga kulawa tunda kinsan yadda wajen nan ke da santsi,ko su lami kika saka zash goge,yanzu da amira ce ta taka wajen Allah ne kadai yasan me zai faru,ki kula sabida gaba"
"To" ta fada tana zumbura baki ta koma daki,ranta cike fal da baqincimi,ita wacce iriyar mara sa'a ce,kuma wai ummin har take goyon bayan wata bare a kanta,lallai kam ba zata qyake wannan abu ba zatayi mai gaba daya ne kawai komai ta fanjama fanjam,ruwa ummi ta buqata ta gasawa sajida wajen,sajidan tace ai anty ta gasa mata,hakan yayiwa ummin dadi,daya daga cikin abinda yasa har kullum take sumayyan ke sake shiga ranta kenan sanin ya kamata,ba qaramin jin dadin zama take da ita ba,ba shakka da zaiyiwu riqe sumayyan zatayi wajenta har ta haihu,amma tasan hakan ba maiyiwu wa bane,ita kanta tasan alkunya almustapha kawai yake mata,wanda dukkan alamu sun nuna ya fara gajiyawa,don ya soma yi mata qananun qorafi,ko haka kawai ba gaira ba dalili sai ya dinga tashinta cikin dare yana sata kaiwa sumayya waya.
***** ******** ******
Kimanin takwas ne na dare yau ta kwanta da wuri,so take tayi bacci sosai,jin kanta take kamar wadda ta shekara batayi bacci ba saboda yau tayi tashin wuri,don haka yau tun magariba ta kashe wayarta don ta huta sosai,har ta kwanta qishirwa ta tasheta,ta miqe ta zura hijabinta ta sauko qasa,cikin sandata bude fridge ta dauki ruwa saboda duk saman babu ruwa mai sanyi,ummi ta hana ta sha shi yasa ake ajjiye mata mara sanyi,ita kuma qaunarshi take,idan bata sha ba har wani abu take ji ya tokare mata qirji.
Tana tsaka da bude robar taga fitowar eesha ta haura sama,da alama wajen ummi zata,kamar tace mata ummin na sashen baba sai kuma ta fasa tunda ba shirginta take shiga ba,ta kammala shan ruwan ta ta maida robar ta rufe ta kama matattakalar benen ta soma haurawa saman,tana tsakiya eeshan ta fara saukowa,bata dubeta taci gaba da hawa abinta,tana step din qarshe eeshan ta iso inda take,wata wawuyar bangaza da bata zata ba bare tsammata eeshan tayi mata,wanda hakan ya sanya sumayyan yin taga taga baki daya tayi baya,ta gama saddaqarwa ta gama yawo,saboda step.ne ya kusa ashirin wanda ba shakka idan har ta samu nasarar komawa da baya sai ta gangara ta kan kowanne,cikim azama tare da kiran sunan Allah taji kamar an turata gaba,singalin qafarta ya daki qasa ya bafa wata qara,ta sanya hannayenta ta dafe qasa sanda take faduwa,wanda banda hakan da saman cikinta zata fada,suma hannayen qarar suka bayar ta zube ta gefen hannunta na dama daidai sanda taji muryar ummi cikin qaraji tana fadin
"Hasbunallahu wani'imal wakil,innalillahi wa inna ilaihi raji'un aisha!!" Ta qarashe fadi tana haurowa saman cikin wata iriyar sassarfa da gaggawa,idanu eesha ta soma fiddawa gabanta na wata matsananciyar faduwa,tasan tata ta qare,ya akayi har ummi ta iso wajen bata lura ba?.
Tuni ummi ta isa inda sumayya ke yashe,azaba da radadin da hannunta da qafarta daga buge kadai sun isheta,ambaton sunan Allah akwai take tana jin yadda qashin qafarta ke zugi da tsuko,a rude ummin ke tambayarta da qyar ta bata amsar qafafunta,ta matsa qafar sai ta sanya qara sabida azaba,cikin matsanancin bacin rai ummi ta waiwaya ta dubi eesha
"Ashe baki da hankali eesha?"
"Wallahi ummi....." Ta soma fada cikin rawar jikibda rawar murya,tsawa ta daka mata wadda ta sanya hantar cikinta kadawa tana gaya mata ta bace da wajen,sai da taga saukarta sannan ta maida hankalinta ga sumayya taba mata sannu,tausayinta na kamata,taimaka mata tayi sai data jinginata da kujera sannan ta dauki waya ta kira baba da anty maamaa.
Kusan lokaci daya suka shigo,salati anty maamaa ta dinga yi,shi kanshi baban shiru yayi ranshi na sosuwa,ba bata lokaci ya kira driver yasa ya fito da mota suka sanya sumayyan ciki
"Inaga ba asibiti ya kamata aje ba,wajen masu gyara za'aje a duba mata qafan da hannun,tunda Allah yasa bata fadi kan cikin ba" inji ummi,hakan ya sanya baba ya kira mutumin dake musu irin wannan aikin,basu da nisa sosai shi yasa bai bata wani lokaci ba ya iso.
Sai daya duddubata sannan ya tabbatar musu qafarta gocewar qashi ce,hannun kuma targade ne,zaiyi mata gyara,dui wanda ke wajen sai daya tausaya mata,tasha wuya sosai wajen gyaran,haka ta dinga hada gumi taba kiran sunan Allah kaman zata suma,murqususu take ga ciki a gaba daya fara tasawa,kafin a gama ta hada gumi sharkaf,ya gama ya baiwa ummi maganin da za'a ringa shafa mata da kuma yadda za'a kula da wajen,yace duk bayan kwana bibbiyu zaizo ya dinga dubawa,godiya baba yayi mishi sannan ya sallameshi.
Kusan kasa runtsawa sukayi baki daya,sai daga bisani baba ya fara tafiya,anty maamaa kam bata iya tafiya ba ita kanta sai wajen biyu na dare,ummi kuwa kwanan zaune tayi tare da sumayyan,sajida ma da qyar tayi bacci,duk tausayin sumayyan ya cikata,eesha kuwa tunda ta shige ba'a sake jin motsinta ba,ita so tayi cikin ya zube idan yaso ayi mata hukunci baki daya,ran ummin ya kai maqura wajen baci,tausayin sumayya kawai ya isheta,ta riga ta gama yanke hukunci a gobe aysha zata bar gidan,kome mamanta zata fada saidai ta fada,don ba zata yarda tana jibtana gani a bata amana ba kuma ta kasa riqewa,me zata cewa almustapha idan wani abu ya samu cikinsa?
A dakin ummin ta kwana,nan ummi ta kawo mata ruwa da roba ta daura alwala saboda yadda qafar tayi mata tsami,a hankali ta waiwayo tana gaida ummin bayan ta idar da sallar,amsawa tayi tana tambayarta jiki ta amsa mata alhmdlh,sannu ta sake mata tare da bata baki kan abinda eeshan tayi,ita kunya ce ma ta kamata,sai kace ummin ce ta aikata?.
Qarfe biyun rana ummi ta isa dakin eeshan ta taddata kwance,zumbur ta miqe tana gaidata,a tsautsaye ta amsa tana ajjiye mata kudi
"Ki tashi maza ki shirya ki wuce gida,koda wasa kada kice zaki sake dawowa gidan nan a yanzu,tunda ba yau ashe kika soma qoqarin aikata mata hakan ba,idan banda tsabaar rashin mutunci eesha bata ci darajata ba a wajenki?,ko duka bata ci darajar wannan ba ai taci darajar dan tayin dake cikinta ko?,to ki tashi ki shirya ki wuce gida" kuja eesha ta saki,abinda take bege wato so yake yayi mata nisa,garin neman gira zata rasa idanu
"Yanzu ummi sabida ita zaki raba zumuncin dake tsakaninmu?" Cikin mamaki ummin ta waiwayo tana dubanta
"Van raba ba,amma a yanzu dai na raba har sanda zata bar gidan nan,na riga na gama magana da mamanki" ta juya tana ficewa,abun takaicin ma sam bata ga nadama tattare da ita ba,don ko qafar benen bata taka da niyyar zuwa dubata kan abinda tayi mata ba.
Wunin ranar yini tayi tana tofa fatiha a wajen,haka ya kawo mata sauqi sosai kan radadin dake damunta.
****** ***** *******
Ranar da abin ya faru baki daya bai samu zama sosai ba,ayyuka sunyi musu yawa can company,sau uku yana kira yaji a kashe.
A gajiye ya dawo,a falo ya sami su'ad din,tana kwance dai dai saman kujera,sanye da gajeran wando da qaramar vest iya ciki,ko ina baja baja da kwalayen data gama ciye ciye,yayin da bacci mai nauyi yayi awon gaba da ita,tsallaketa yayi ya nufi bedroom dinshi kai tsaye ya rage kayan jikinsa,duk abinda yake tunanunta na mqale a ranshi,yau daya tak da baiji muryarta ba jinsa yake kaman maraya,yayi tsammanin zai iya share mata kaman yadda ta shareshi amma sai yake ji abun ba mai yiwuwa bane a wajenshi,towel ya dauka ya wuce bathroom yayi wanka.
Ko mai bai iya shafawa ba bare ya ya sanya kaya ya janyo wayarshi ya soma lalubar wayarta,a kashe aka sake ce masa take,sai yaji hankalinsa bai kwanta,lambar ummi ya soma laluba cikin sa'a ta shiga,fitowar ummin daga dakin kenan taga shigowar kiran
"Ummi an yini lpy?"
"Lpy lau almustapha ya aiki?"
"Alhamdulillah" sai kuma yayi shiru,halin nashi ya motsa,itakam da zaiyu shirun da yafi mata,tasan wal'alla sumayyan yake nema,ita kuma batasan zancan yaje kunnenshi,tafiso matarshi ta warke saidai yazo ya tadda labari kaman ma ba'a yi ba
"Ummi.....sumayya" ya fada kaman mai tsoron fadin
"Uhmmmm,wani abu ne?"
"Tun jiya bamuyi magana ba,ko zan samu jinta?" Kaman ta hanashi saidai ba yadda zata hanashi magana da matarshi
"Kashe zan kai mata"
"Ummi batta a haka zan jira" dariya ma yaso bata har sai data ce
"Almustapha?,kaman wanda network din zai gudu?" Kunya ta kamashi amma sai ya dake yayi shiru yana sauraron tafiyar ummin.
Tana zaune ta gama shirin baccinta tana karanta wani qaramin littafin labarai na larbci,qafarta na saman matashi mai laushi,hannunta daya na ajjiye saman cinyarta,wayar ummi ta miqa mata tana cewa
"Almustapha" littafin ta ajjiye ta karba gabanta na faduwa ta kara kunnenta sanda ummin ke juyawa ta fice,shiru yayi kawai yana saurarenta tamkar baya kan layin yana hadiye wani abu,fitar numfashinta kawai ya soma samar masa da nutsuwa,sallama tayi masa sai da ya bada tazarar wasu sakannni sannan ya amsa
"Why sumayya why?,wato idan ban nemeki ba ba zaki neme ni ba?"
"Ba haka bane.....wayarce bansan inda ta fada ba"
"Kaman yaya?" Ya tambayeta,da sauri ta gyara zancanta
"Amm...ina nufin ta dauna daukan chargy ne" tsaki ya ja sannan yace
"Kamanni ace wayar matata ta har takai matsayin da don kanta zata daina daukan chargy?,ki cire layukanki ki bar amfani da ita,gobe da safe za'a kawo miki wasu,daya ni kadai zan dinga kiranki da ita always ta zama akunne kusa da ke,dayan kuma ki kira duk wanda kika ga dama"
"Na gode Allah ya saka da alkhairi ya qara arziqi"
"Amin.....nifa gaskiya na fara gajiya,haquri na ya kusa qarewa fa....a qa'ida ai cikinki ya shiga wata uku...am a doctor nasan yadda zan kula da mata ta" gabanta ya fadi,yau bisa dukkan alamu rigima yake ji tunda taji muryanshi ta fuskanci haka,tayi qas da murya
"Habba mana.....duka saura sati nawa lokacin da suka ce ya cika,ka qara haquri mana please kaji?" Shiru kawai yayi yana sauraren muryarta yana nazari
"Me ya sameki?" Taji ya furta kai tsaye,sai ta hau fiddo da idanu tana kalle kalle,ta daga wayar ta duba voice call ne ba vedio call ba bare tace yana ganinta
"Ni?...ba bau komai me ka gani"
"Akwai wani sauyi tattare da muryarki,kuma jikina ya bani haka"murmushi tayi duk don ta dauke hankalinsa
"wrong doctor,baka canka dai dai ba,am fine,ina shirin yin bacci ma ummi ta shigo"
"Ban yarda ba,but....tunda kince haka ne is ok,ki kunna wayarki kafin a kawo wata"
"An gama yallabai" murmushi yayi,yanajin kaman tana lallabashi ne kawai ya sauka daga kan layin,sai kawai ua datse kiran yana jin wayar kawai bata yi masa ba,jikinsa bai bashi ba,sam ma ba irin wannan hirar yakeso suyi ba,hankalinsa baki daya yayo nijeria.
Ajiyar zuciya ta saki da taga ya datae layin,da alama halin ne yau ya motsa,dole ta tashi sajida ta sanyata ta dauko wayar ta jona a chargy sannan ta kunnata kafin ta kwanta.
****** ****** *******
Washegari misalin sha daya na safiyar ranan yana tsaye gaban mudubi yana shiryawa,kominshi a nutse a tsare,ya gama komai tsaf yana taje sumarshi ya janyi wayoyinshi dake gefe,tun jiya da ita ya kwana cikin ranshi,yana jin mawuyacine idan baiyi rashin ta ido ba yaje kawai ya daukota,yana jin kaman sun shekara goma ne basu ga juna ba,number baba ya soma don ya gaidashi kaman kowacce safiya,idanunshi suka sauka kan takardar dake gefanshi,ya saka hannu ya dauko ya bude ta,ranshi ya baci sosai ba wai don kudin da ya kashe kawai kan takardar ba,sai na yanda su'ad tayi burus da maganarshi.
Yana tsaka da duban takardar ta fito daga wanka tana tsane jikinta da towel
"Yanzu wai har ka shirya zaka fita,nifa gaskiya na gaki da wuni a gida