Showing 186001 words to 189000 words out of 364327 words

Chapter 63 - KUNDIN KADDARATA COMPLETE HAUSA NOVEL

HUGUMA   

20 Aug 2024

40131

miqewa kamar wanda ya sha abun maye ya lalubi hanya ya fice.

     Ya jima zaune gefan gadonshi aqalla awa guda yana yamutsa hannayensa cikin kwantacciyar sumarshi mai santsi da laushi,gumi ko ina yana keto masa,miqewa yayi ya soma zare kayanshi yana jefarwa cikin dakin,sai da ya rage saga shi sai boxer sannan ya fada bandaki,ruwan sanyi ya sakarwa kansa tsakiyar shower,ya jima tsaye sanyinbruwan na ratsashi tare da qoqarim control din kansa,ya sake barnatar da awa guda cur a haka har sai da tunaninsa ya dawo yadda ya kamata,qwaqwalwarsa ta fara yi masa bita,ya tabbatarwa kansa bai yi kalaman da suka dace ba ga mahaifinsa,baabaa ne,masoyinsa,wanda qaunar da yake masa ta daara ta dukkan wani daa ko jika dake cikin zuriyarshi,dakin gadon ya dawo ya sake lalubar wasu kayan ya sanya,wannan karon jallabiyya ce,ya gabatar da sallar la'asar,zama yayi kawai yana karanta yadda wannan QADDARAR ta fadowa rayuwarshi a lokacin da bai zata ba,yana nan a haka bai ankara ba yaji kiran sallar magariba,a nan gun itama ya yita a haka isha'i ta ruske shi,sai a sannan ya samu qwarin gwiwar miqewa ya sake daura alwala ya sanya hular tashi ka fiya naci ya nufi masallaci.

       Sahunsu daya da baabaa,har aka idar bai motsa ba sai da ya ga baabaan ya gama addu'o'inshi ya miqe zai fita sannan ya mara masa baya,yana gaba yana binshi a baya,baban ya san da haka amma yayi banza da shi bai ko nuna ya ganshi ba,sai da zai bude qofar gidan yayi sauri ya bude mishi yaci gaba da binshi har sanda ya isa falonshi sannan ya waiwayo yana sake tamke fuska duk da yasan dama hakan zata faru,yasan halin mustaphan zai sake waiwayowa a duk sanda nutsuwarshi ta dawo jikinsa
"Lafiya kake bina,zan shiga na kwanta ne idan akwai bashin da kake bina ban kammala biyanka ba sai ka gayan ko?" Kai ya sadda yana jin nauyi da kunyar maganar da baabaan ya fada,qarasawa yayi gabanshi sannan ya zube kan gwiwarsa
"Kayi min afuwa baabaa kayi haquri kan baata makan da nayi,nayi kuskure wanda bana fatan sake yinsa,na amshi dukkan hukuncin daka yanke me kake buqata yanzu daga gareni" dawowa yayi ya samu waje ya zauna sannan yayi masa nuni da ya dawo kusa da shi ya zauna,sosai baabaan ya dinga kwatanta masa manufofi da hujjojin da yake jin sun isa su sanyashi qara aure,daga bisani ya rufe
"Ka gwada zama da ita mustapha na cika maka baki tare da kurin samunta fiye da yadda kake zato ko tsammani,nasan jinin sule ba zai taba kasa gadon halinshi ha,mustapha,ka riqemin sumayya da mutunci da amana,idan ka wulqantata ka dauka ni ka yiwa,haka idan ka bata daraja,bazan iya maka afuwa ba aduk sanda na sameka da lafin wulqantata ba bisa haqqi ba"
"Na yi maka alqawari insha Allahu"
"Allah ubangiji ya albarkaceka,yq cika makq burikanka,ya kyautata rayuwarku kai da ita baki daya,kiran da nayi maka kenan zuwa nijeria,yaushe zaka dauki matarka?,sannan a ina kake son ajjyeta?"
"Duk yadda kace baba haka za'ayi" murmushi ya saki yana dukan kafadarsa
"Kaine fa mijin kuma kai ke aurenta bani ba da zaka turon zabin"
"Ka isa damu ne baki daya baba"
"Idan ta nine ko yau kaje ka dauko matarka,sannan ka wuce da ita dubai,don nima ina son naga daana ya fara dandanar zaqin aure" duk da rudin da yake ciki maganar baban ta qarshe sai data sanyashi jin nauyi
"Zanyi yadda kace,amma amin afuwa zuwa gobe"
"Ba lallai bane ai,kana iya barinta abuja idan kaso,amma sai bayan kun gama fahimtar juna da ita kun fara sabawa,fatana ka riqeta da mutunci"
"Insha Allah baaba" addu'a yayi masa mai kyau da tsaho,wanda tilas mustapha ya dinga lallaba kansa da zuciyarsa ya zauna sukayi hira da malam din na wasu mintuna sannan ya tashi ya wuce.

       Kamar zai zauce cikin dakin shi daya haka ya dinga ji,kiran hamza ya shigo wayarshi,wata bahaguwar harara ya ballawa wayar,ganu yake hamzan ne da shegen bakinsa ya masa wannan fatan,to amma ai ba fatan hamza bane tunda baifi awanni da yi masa shi ba,anya kuwa hamza baisan da wannan maganar ba ya munafunceshi?,yana kallon kiran har ta ya gaji da kiran nasa ya haqura,yana tsagaitawa lambar su'ad ta danno kai,wanda shi sam yama mance da ita,ya kuma mance rabon da suyi waya,hannu ya sanya cikin mutuwar jiki ya daga kiran ya kara akunnensa,tun kafin yace wani abu sheshsheqar kukanta ta cika kunnuwansa wanda hakan ya hadu da tashin hankalin da yake ciki take suka saukar masa da ciwon kai,sai ya runtse idanu yana saurarenta
"Almustapha,ni zaka ci amana?,ni zaka yaudara almustapha,dama zakq iya kqllon wata mace macen ma 'yar afrika bayan ni?,almustapha kana jina kayimin banza da kai nake musty!" Ta fada cikin qaara da qaraji,tasan sarai yana jinta tafi kowa sanin halinshi na rashin son hayaniya da kuka,shirunsa ya sake tunzurata,mamanta dake gefe ta rada mata abinda zata yi,itama a ganinta hakanne ya dace tunda da irin wannan taci nasarar aurenshi
"Wallahi almustapha sai na kashe kaina,sai nasha poison don bazan iya hada ka da wata can ba,wallahi sai na kashe kaina....." Ga mamakinta tun kafin ta kashe wayar shi ya kashe,bama kashewa kadai ba sai da yaja mata wani mugun tsaki sannan ya kasge wayar baki daya ya cillar,miqewa yayi cikin tangadi ya sauya kayan bacci ya koma gado ya duqunqune cikin bargo,yayin da qwaqwalwarsa ta kasa aikin komai a tsaye take cak.

   ******   ******   *******

      A shirye ya fito cikin baqaqe sidik three pieces slim fit suit,ba qaramin kyau suka yi masa sun haskashi matuqa,saidai shi kadai yasan izayar da yasha daren jiya,tilas ya dauki sun glases wada ya dace da shigarsa ya sanya,tamkar don ado ya sanyashi ba don kare idanunshi da suka sauya launi ba saboda rashin wadataccen bacci yayi masa kyau sosai shima,ya yanke shawarar gwara yaje asibitinsa ko wasu daga cikin marasa lafiyan da zai iya dubawa ya duba ko hakan zai rage masa zafi da radadin da yake ji.

     bai samu baabaa ba saboda ya fice wajan aminin nashi malam kan maganar yadda zai gabatarwa da malam dukkan gidajen gonanshi wanda yakeao a yanzu su dawo hannunshi ya karbi dukiyarsa,yaga kamar malam din yana bagarar da zancan yaqi tsayawa su tattaun,yau yake so ayita ta qare,saboda haka anty maamaa maan kawai ya gaisar ya wuce wajen ummee,tana kwance ta fito ya gaidata ta amsa tana dubanshi,basai an gaya mata ba tasan da walakin goro a miya,ta gabatar masa da break fast,bai iya cin komai ba sai coffe da yayi qoqarin sha don kada ya daga hankalinta,yana sha tana gefansa a hankali tace da shi
"Dukkanin mai biyayya zaici ribarta a gaba,bijirewa iyaye koda kan gaskiyarka ne bashi da wani alfanu,zaiyi wuya idan baka ci karo da tashin hankali ba a gaba sanadiyyar wannan bijirewar,almustapha,na roqeka ka riqe musu yarinya da mutunci,ka fiddani kunya kada ka watsan qasa a ido,yanzu ne lokacin da zaka nuna irin tarbiyyar daka samu daga gareni" jikinsa duk sai yayi sanyi,shi wai iyayensa da suka isa da shi ke roqo?,akan me?,duka akanta?,akan yarinya qwara daya tal,cup din ya dire yana fadin
"In sha Allah" cikin sassanyar murya sannan ya fice yana dauke da brief case,tuni drivanshi ya gama shirya komai,maimakon baya da yake shiga wannan karon gaban motar ya shiga,baice komai ba don shima ya lura akwai abinda ke faruwa da ubangidan nashi ya shiga ya tada motar masu tsaron qofa suka bude masu wakekem get din suka fice.

       Daga kadan kadan ciwon marar ke sake yawaita mata,wanda hakan ya sanya maama ta takurata kan lallai yau sai taje taga likita,itakam baki daya bajin dadin rayuwar ma take ba,amma tilas ta shirya zuwa don cika umarninsu da samun kwanciyar hankalinsu,qarfe tara ta gama shiryawa bayan sun gama waya da anty dije ta bata adresa din wani asibi,ta gaya mata komai kyauta ake saidai akwai tsantsar kulawa tamkar asibitin da ka fidda kudinka ka biya,ba kyautar ce zata kaita ba,kulawar data fada shi yasa zata,don bata da matsalar kudi,don baabaa ya ajjiye mata su tamkar baisan zafin su ba,hatta da abinda zata ji bai yarje taci na gidan ba,sabida yace yanzun ba dolensu bace.

        Sai data shiga ta gaida baabaan a kunyace sannan sukayi sallama da malam kan zata asibitin da yake baaban yace izinin fitarta ya damqawa malam din kafin qarasowa mijinta,dakatar da ita baaba yayi ya fidda wayaraa ya kira daya daga cikin direbobin dake dakon fitowarsa ya bashi umarnin kaita ganin likita,cikin girmamawa ya amsa,shiru tayi cikin lafiyayyar motar wadda idan ba gargada ta kai gargada ba ba lallai ka fahimci ana tafiya ba,ire iren motocin da suke mallakin familyn professor mukhtar,motar da ada ko a mafarki bata darsa shiga irinta ba,ajiyar zuciya ta saki sannan ta fidda wayarta ta duba kiran dake shigowa amira ce,murmushi ta saki duk ciwon marar dake neman sake tsananta mata,amsa wayar tayi ta kara akunnenta.

Masu karatu muje zuwa,wanne asibiti sumayya zata????.







*mrs muhammad ce*👑

📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
[23/02, 11:51] Beesama Zamani Wrt Grp: ✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖


*~NA~*

*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*

*WATTPAD:HUGUMA*

*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)

6⃣7⃣

*Bismillahir rahmanir rahim*

Allah madaukaki yana cewa


*duk wanda ya sallamawa Allah dukkan lamuransa alhali yana mai kyautatawa haqiqa yayi ruqo da igiya qaqqarfa wanda bata tsinkewa(yankewa/rabewa)*

_____________________________________




        Wuni nafisa tayi ta kasa sukuni da tausayin sumayya,a haka auwal ya dawo ya taddata,baki daya wani qaunarta na sake shigarta,haqiqa bata yi zaben tumun dare na aminiyar qwarai ba.

         Washegari da kanta taje gidan anty dije dauke da ledar mayuka da turarukan data siya matan,dariya sumayyan ta dinga tana kallon tarkacen kayan,ko ba'a fada mata ba tasan cewa sunfi qarfin mai rangwamen gata irinta,saboda zuwa yanzu kanta ya soma budewa,tana iya gane abu mai tsada,balle ta san nafisan sarai,komai nata designer ne,kuma komai nata a set dinsa take amfani da shi
"Wai kina nufin ni kike so na dinga amfani da wannan kayan?"
"Qwarai kuwa da wace?" Kai ta kada tana dariya
"So nake naga kin sauya sis,so nake naga kin fara sabuwar rayuwa" kai taci gaba da kadawa tana dubanta,kafin tace wani abu anty dije ta shigo dakin,kayan ta dinga dauka tana dubawa tana dariya
"Allah yasa a baki hadin kai"
"Idan ma taqi ina kallon fatarta zan gane,don sun tabbatar min suna da kyau,suna gyara fararen mata" itama ta fadi tana dariyan,godiya anty dije ta taya sumayya,sun jima suna hira kafin nafisan ta koma gida don dora abincin dare,don auwal baison take away idan ba lalura ba ta kama.

        Anty dije ke jinjina tsadar kayan
"Bansan ya zata kaya ba idan kayan suka karbeki ba,suna da kyau amma akwai tsada" cewar anty dijen.


Kiran wayar daya shigo wayar sumayya ita ta katse hirar da sukeyi din,fuskar ta washe baki bude take fadin
"Amiran baabaa ce anty"
"Kice ina gaidata" inji anty dije tana miqewa don ficewa daga dakin ta fara jiyo hayaniyar minal da khalipha da alama rigima suke shi da ita
"Autan baabaa(haka take kiranta idan taso tsokanarta)"
"Mutanen uk,wai nikam yaushe zaku dawo,nifa na gaji wlh daga gida sai makaranta,ni daya kamar mayya,idan bakuyi wasa ba fa zaku ganni wlh na biyo sahu" dariya sumayya ta dinga yi ganij dududu watansu nawa ma da tahowa
"Kamar yaune fa zaki ga mun dawo din,yi haquri takwara" dariya sukayi baki daya sannan suka soma taba hira,amiran na bata labarin abubuwan da suka faru bayan tafiyarsu
"Amiran umman khalipha,baabaa fa ya karbi kudin aurena har da sa rana watanni shida masu zuwa dai dai sanda zan kammala degree dina" ta fada cikin nuna farinciki,cikn zumudi sumayyan tace
"Kai haba dai takwara"
"Wallahi amira,amma nikam tsoron yin auren nan nakeji takwara,duk da saifullahi na matuqar sona da qaunata,hakanan na amince da tarbiyya da halayyarsa" gefe daya na zuciyar sumayya itama jimamin da take mata kenan,saidai ba lallai abinda ya samu dan uwanka kaima ya sameka ba,kowa da tashi kalar qaddarar,bare amiran ita ba mai mata zata aura ba,ita daya ce a gunsa
"Meye wani abun tsoro?misali su ummee da sukayi auren su wani abu kika ga ya samesu?" Kai ta kada kamar tana kusa da ita
"Um um,kawai banson rabuwa ne da gida,ina son family na"
"Ba shakka familynki abunda zaka yi marmari da begensu ne idan ka barsu,duk wanda ya kalli yadda kuke son juna ba zaiyi mamakin haka ba" sumayya ta zantawa ranta,amma afili sai ta bagarar da zancan da nuna rashun muhimmancinsa
"Duk mace 'yar wani gidan ce,ko su su ummeen ce miki akayi gidanku ne gidansu,suna nasu familyn fa suka baro ko?" Sai amiran ta qyalqyale da dariya
"Kinji umme tace ah to,ashe taji me kika fadi,kinsan abinda anty maamaa ta gama gayan kenan dazu" itama dariyan tayi,ta shiga tsokanar amiran
"Kawai kice mu fara shirin baki,ina ga ba zamu wuce wata guda da dawowa ba zamu shiga hidima,ummm,bari na gayawa anty dije mu fara taru"
"Ahto,don kune amarori,shi yasa na dage saidai asanya wata shidan,daa qasa da haka za'a saka,nasan kafin sannan kun dawo"ci gaba da tsokanarta sumayya tayi a haka suka rabu cikin barkwanci.


Bayan ta aje wayar ta samu anty dije na sauyawa minal kaya da alamu bata wadancan tayi don ba'a jima da yi mata wanka ba
" nikam saura qiris na sauya qawa,wannan qawa tawa qazamiya ce"sumayya tayu maganar tana duban minal tare da yamutse fuska
"Yadai fi wallahi,duk gidan nan babu mai bata kaya kamar nata"inji anty dije,fuska ta kyabe tana shirin sakin kuka
" na daina anty,wayyo Allah na"ta fada tana bubbuga qafafunta zata hau bori
"To shikenan,ya isa,ai ke qawata ce ta amana,babu mai rabamu,uwata ce fa ta kaina" sai ta soma dariya tana tsallen murna sumayya na dubabta tana murmushi,duk yaron data gani tuna mata yake da abdallahnta,dauke kanta tayi ta maida ga anty dije
"Anty an sanya bikin amira fa,wata shida mai zuwa" sakin maballin da take ballewa minal tayi dama ta kusa gamawa ta juyo tana duban sumayya
"Tabdijan,kice akwai gangami kenan,bikin auta guda?,bikin amira ni 'yasu?" Antyn ta fada cikin jinjina lamarin,kai sumayya ta gyafa tana nade qafafunta saman gado tana murmushi
"Jar uba,kice abuja zata motsa,familyn baabaa prof za'ayi bikin da aka jima ba'ayi kamarsa ba,to ai ina ga da na su mahmoud za'a hada tunda suma wata bakwai ne inaga yayi saura cikin ranar auren da aka sanya musu ko,Allah ya nuna mana,sai mu fara shiri tun yanzu,sumayya kuna da biki" inji anty tana murmushu gami da jinjina kai
"Wallahi anty haka tace,ni kam mai zan iya cikin hidimar,ni da ban taba bikin qawa ba?"
"Aikuwa dole ki ware ayi komai da ke,yadda amira ta daukeki kada kuce zaki watsa mata qasa a ido,nasan halayyarki sarai" dariya sumayya tayi ganin yadda antyn ta camfata tana kwantar da kanta saman filo
"Allah ya bamu iko to anty" kan ta gama rufe bakinta kira ya shigo wayarta,lambar alqasim ne,tana mamaki da har yau bai rabu da ita ba,bayan ta zayyana masa ita din bazawara ce har da yaro,sai ta latse wayar ta kasheta baki daya tana jan qaramin tsaki ta gyara kwanciyarta abunta,ita yanzun babu mai daga mata hankali,ko lukman idan ya kira sai taga damar dagawa,darajar yaranshi dake sonta kawai take dubawa,badur rahman je kadai ke da wannan qinar na daga kiransa a duk yayin da ya kira din.

        Cikin qanqanin lokaci da fara amfaninta da mayukan da sabulan taga banbanci,ita a karan kanta taga sauyi,wani laushi da santsi fatarta ke sake yi tamkar wadda ke zuwa gyaran jiki,baki daya qamshin jikinta ya sauya zuwa wani qamshi na musamman ma daban wanda ya kama kayanta sabida turaren da take amfani da shi set na man da sabulun,cikin watannin da basu gaza biyu ba sumayya ta sake komawa wata ta daban,komai nata ya sauya,sau tari laila na tononta tana cewa
"Wlh anty sumayya kin koma 'yar gayu" hakan ya yiwa nafisa dadi qwarai a ranta,bisa dukkan alamu zata cimma qudurinta cikin sauqi kan sumayyan,tana son sumayyan ta zama wani sashe na familynsu,dukkanin halayyarta sun mata babu na yarwa.

*******     *******    ********

         Yau da gobe kayan Allah,sannu a hankali kwanaki ke mirginawa suna wawasar kwanukanmu a duniya,da kuma kwanakin dukkan wani abu da muka sanya masa lokaci,zuwa yanzu su sumayyan na da watanni takwas cikin qasar ta uk,ba qaramin karba qasar ta yiwa sumayyan ba,bugu da qari kuma ga nafisa daga gefe data kafe kai da fata zata sauya sumayyan malam din zuwa wata sumayyan ta daban,sumayyan uk,qudirinta kuwa ya karbu,a yanzu idan kaga sumayyan zaka sha mamaki,komai nata ya sauya,wani irin kyau da da can yake boye a yanzu ya soma bayyana kansa,hutu jin dadi da kwanciyar hankali suma na bada tasu gudun mawar,hatta da anty dije kan kalleta mafi yawancin lokuta,dadi take ji cikin ranta da ta sanadiyyarta sumayyan ta soma samun canjin rayuwa,ashe da can damuwa rashin kwanciyar hanakali da tension ita ta tasamma kassara sumayyan da gurgunta tunaninta,a yanzun kai baka ce sumayya bace wadda ta taba aure,'yar shekara ashirin da biyu har da yaro ba,sai kayi zaton tana cikin shekararta ta sha shida ne,tun da can Allah ya bata sanyin murya nutsuwa da iya magana,sai abun ya sake zame mata ado,zakayi zaton daga wani babban gida ta fito.

       Gefe daya karatun ta ya kankama haiqan,turanci ba damuwarta bane a yanzu bare hausa,mai gaba dayan larabci dama ya jima da zama kan harshenta tun tana qanqanuwarta,tana daya daga cikin zaqaquran ajinsu a yanzu,zaka yi mamakin yadda harshenta ya karye,tana karbar karatunta da kyau,tuni wata daya baya ta kammala makarantar koyon girki da mu'amalar yau da kullum,ta fita da cetificate mai kyau,a yanzu kusan anty dije ta zama 'yar kallo ta fannin kitchen,kowacce rana da kalar abincin qasar da sumayyan zata girka,uncle farouq da taya bera bari shike basu kudi suje suyi siyayyan kayan da za'a buqata a ranar tunda shi bai sansu ba,laila ce 'yar rakiya,kai na rawa zata bita suje,zuwa yanzu ta sake tana iya zuwa gurare wadanda ke kusa da su ba nisa can ba,idan kuma suka so yin nisan nafisa ce jagora,zata debesu guri guri da yake ita din tamkar 'yar gari ce a garin,ranar haka zasu wuni a waje,sau tari sumayya na


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login