Showing 306001 words to 309000 words out of 364327 words

Chapter 103 - KUNDIN KADDARATA COMPLETE HAUSA NOVEL

HUGUMA   

20 Aug 2024

40076

tun kayan safe ne jikinki"
"Ai naci abincin da amira......"
"Amira?.....amira ita ta tsaidaki kenan ko?,ita tazo?" Ya fada cikin sigar tambaya da jin zafi,shiru tayi bata amsa ba,hakan ya sanyashi cikin hanzari ya fara saukowa daga kan step din zuwa qasa yana fadin
"Na baki mintina goma ki tabbatar kin sake wanka...ki canza kayanki....ki dauki abincinki kici kisha magani..." Ya qarashe maganar cikin huci yana kewayeta ya fice.

         Dariya su'ad ta saki wadda ta riski zancanshi na qarshe
"Sai haihuwa manya.....kinga kadan daga illolinta ko?,har kin fara qazanta kenan.....baki sani ba,bama zama da qazami,hakan yana nufin kin fara saitawa kanki hanya"ta fadi tana saukowa daga sama tsuke cikin riga da dogon trouser qoqarin daidaita kanta tayi kafin ta qiriqiro murmushi
" wani ko zai shekara baici ba wa ya damu da shi?,ke dai kiyi ta kanki,wadda ba'a damu da wuninta cikin gida ko waje ba,koda watar qasar ce kuwa ta shekara can,duka daya wajen wanda ya ajjeta"ta juya ta shige ta bar su'ad abin na mata zafi a rai,da ita take,tana yaba mata magana ne kan zamanta america almustapha na dubai,ranta ya baci qwarai,ta tsaya nan saman matakalar bene tana ciza yatsa.

        Duk data rama hakan bai hana zuciyarta suya ba,komai zai mata ya kasance su biyu,bata son ace har gaban su'ad yana yi,haka dabi'arta take ko a gidajenta na baya,sai ta fashe da kuka maimakon ta shiga bandaki yin wanka sai ta fada saman gado tana ci gaba da rusa kuka.

       Bangaren ummi ya wuce direct zai saukewa amira,taimakon da Allah yayi mata ko layin motarsu bata gama ficewa ba ya shigo neman nata
"Sun tafi yanzun nan,lafiya?" Ummi ta tambaya tana karantarshi,fushi ne taf cike a zuciyarshi da fuskarshi,batasan me ya taboshi haka ba,tunda ita bata dauki maganan hanasu tafiyan ta kai haka ba
"Ba komai...." Ya fada yana juyawa wannan karon a sanyaye ya fice,sai ta bishi da kallo kawai ta girgiza kai tana ci gaba da yin abinda take.


        Yana shiga su'ad ta taroshi,har saman dining ya zauna tana karairaya fari da karkade karkade,babban abin takaicin sai da yace
"Bani abinci" yana lumshe ido saboda yunwa da fushi,yau duka saboda bacin rai baici komai ba,zuba masa tayi ta tura gabanshi tana debo masa labaran da sam basu shafeshi ba tana masa,idan yayi loma daya sai ya jima baiyi ta biyu ba,ga surutunta da ya soma hawa masa ka,sam labarin da take bashin sake caja mishi kai yake,labarin abokanta karatunta maza da mata,duka bata lura da hakan ba bare ta sarara,rabin hankalinsa baki daya ya karkata bangaren sumayya,yana so yaji daga gareta,haka kawai ya kasa nutsuwa,baya so kuma ya shiga haqqin su'ad ya bar ta wajen hakan bai dace ba.

        Wayarta dake daki ta soma kira tana sanar mata da sunan wanda ya kirata,qawarta ce zulee,wadda idan suka soma waya tana bata labarin bayan dawowarta nijeria har sai a qalla sun kashe kusan awa,da hanzari ta miqe tace mishi tana zuwa,kai kawai ya kada yana ci gaba da tura abincin,qoqari yake ya ture tunaninta daga zuciyarshi amma ya kasa,daga qarahe dai ya tabbatar bazai iya din ba,ture plate din gabanshi yayi wanda ya sanya abincin zubewa ya miqe,kai tsaye ya durfafi dakin.

        A kwance ya cimmata kamar dazun tana fidda hawaye,taji motsin shigowarsa amma bata motsa ba,qare mata kallo yayi sannan ya sauya akalarsa zuwa bandaki,ruwan wanka ya hada mata sannan ya dawo dakin gadon ya tsaye a kanta cikin dakiya
"Tashi ki wuce kije kiyi wanka,wannan ya zama last da zan kanki kina kuka,idan ba haka ba ranki zaiyi mummunan baci" a kasalance ta miqe tana rangaji tare da qwalla ta shige bandakin,locker dinta ya jawo ya fidda magungunanta ya ajjiye,ya shiga kitchen dinta ya fiddo plate ya juye gasashshen naman daya siyo mata da shinkafa 'yar kadan a gefe guda.

       Tana yafe da qaton towel ta fito,a sanyaye ta qaraso bakin gadon ta zauna,tura mata dan table din daya saka abincin da magani yayi a kai ya juya a hankali ya fice,yayin data bishi da kallo qwalla na taruwa a idanunta.

       Cikin dare ya kasa bacci,ji yake kamar yaje ya roqeta ta bishi amma wani sashe na zuciyarshi na hanashi,a hankali ya sauka daga saman gadon,ya zura slippers dinsa ya fice bayan ya dauki wayarshi,qofar ya tura a hankali,dakin lullube yake da duhu,ya ci gaba da takawa har ciki bayan ya kunna fitilar wayarshi,har lokacin itama bacci bai dauketa ba,wani iri take ji cikin jiki da zuciyarta,tana jin shigowarshi tayi hanzari rufr idanunta tare da qara yin luf tamkar mai yin bacci,ragowar hawayen dake maqale a fuskarta ya tona asirin baccin qarya take,ya dauki wajen minti biyar yana duban kyakkyaar fuskarshi,fuskar dake sanyaya mishi rai,fuskar da duk duniya ayanzun bayan ta umminsa yana jin yafi qaunarta,don me zata guje mishi a sanda yake tsaka da tsananin buqatarta ita da abinda yake cikinta,kada dai ace har yau bata sonshi?,har yau bai cimma nasarar zama wani sashe na rayuwarta ba?,sai ya juya a hankali zuwa inda ya ajjiye mata abincin,yasa hannunshi ya bude,ba abinda ta taba aciki,ya duba magungunan ta balla ta sha duka,hankalinshi yaji ya tashi ranshi ya dugunzuma,sai ya kunna wutar dakin baki daya
"Wakeup" ya fada a taqaice,shiru tayi ita adole bacci take
"Ki tashi nace miki!", ya fada a dan tsawace,cikin hanzari ta miqe,daukan abincin yayi ya isa gabanta ya zauna suna fuskantar juna,cokali ya sanya mata ya mata alama da ido kan ta dauka taci,hannunta har rawa yake saboda yunwa,hakan ya sanya ya amshe cokalin ya soma bata a tausashe duk da fukarshi a dinke take,a hankali ta soma karba,tana ci tana satan kallonshi,saidai ko kadan yaqi ya kalleta,
"Abu abdallah"ta kirashi tana kallonshi,yana son sunan qwarai amma wannan karon sai yaqi dubanta,hakan ya karya mata zuciya ta kuma sakin kuka harda 'yar shashsheqa,sai ya ajjiye cokalin yana hade yatsunshi waje daya tare da zuba mata ido,kukanta na ratsa zuciyarshi tamkar ana yankar tsokar zuciyarshi,tsahon minti biyar sannan ya motsa bakinsa
"yanzu fisabilillahi ni me nayi miki?me ke damunki?" Ya fada murya can qasa a tausashe,wanda hakan ke nuna raunin dake cikin zuciyarshi
"Kain....ne" ta fada cikin sheshsheqa,ci gaba yayi da dubanta kafin yace
"Saboda Allah a dakeni a hanani kuka?,saboda ni ban da bakin kukan?,kinsan zafin da nakeji a qirjina?,ina tunanin har yau baki gama yarda da wacece ke cikin rayuwata ba shi yasa kike son aikata min haka,amma babu komai....Allah ne ya jarabceni kuma ina fatan ya yayemin,tunda baida amfani sanya mutum cikin zuciya,da can da ban sanya ba kinga rayuwata lafiya lau..." Bata ji dadin furucinsa ba,sai ta sake sakin kuka
"Kayi haquri don Allah"
"Zan haqura ne kadai idan kika shaidawa ummi zaki bini,ke kadai zaki fada mata ta yarda" kai ta girgiza,ba zata iya watsawa ummin qasa a ido ba,tace mata meye?,kafadanshi ya daga sannan ya miqa mata ruwa,tare da tsareta da ido,tilas ta sha ya kauda kayan ya ja mata bargo zuwa saman cinyanta ya gyara mata filo,bai sake sauraran komai ba ya kashe qwan ya ja mata qofar ya fice.


Washegari yaje kaima baba qara,saidai duka bakinsu daya da ummi,hakan ya sake jagula lissafinshi,haka ya fice jikinsa ba qwari,baki daya sai yaqi zaman gidan,ya wuni waje,yayin data wuni begen ganinshi,amma bata ga gilmawarsa ba,wuni tayi bata leqa ko ina ba tana daki akwance abinta.


Randa ta amshi girki ya rage saura kwana biyu su tafi abida ta haihu,su'ad anata rawar kai tare da shirin tafiya,jifa jifa idan sun hadu a falo tana yadawa sumayya habaicin zasu tafi banda ita,ita tana tsammamin uban tafiyar ne yace ba zata je ba,sabida tana laulayi,ko kallonta batayi bare tasan tana yi,ita ayanzun fushin almustaphan yafi komai daga mata hankali,kaf ta laluba walwalarta ta rasa,ji take kamar taje ta cewa ummin zata bishi,saidai hakan ba mai yiwuwa bane,kawai kunya mai tsanani tattare da hakan.


Ana ya gobe zasu tafi suka je yima abida barka,ta samu santalelen danta namiji tubarkallah da shi,babyn ya burge su su duka,sai taji kwadayin son ta haihu ya sake kamata,ta shafi cikinta ta cikin mayafi tana ddu'a cikin ranta,tana son taga ta tara yara da yawa,wanda ta fuskanci ra'ayin almustaphan ma kenan,su'ad kam dama bai mata tayin zuwa ba,don ko yayi mata dama bata zuwa,don ba shirin arziqi tsakaninta da abida,ta raina ajawalin abida yayin da ita kuma abidan bata daukan raini sam,bata roqa komai daga gareka ba don haka kada ka raina mutincinta,kowa ya tsaya matsayinshi,ya dauki sumayyan bayan sun biya wani katafaren shago sun mata siyayyan kayan barka masu yawa kyau tsada da kuma quality,har ita abidan sai da ya saya mata kayan fitan suna masu kyau bawai don hamza ya gaza ko bai da shi ba,kawai ya wuce komai a wajensa,ya dora musu kudin dinki dubu dari a saman kayan,tun jiya take dubanshi,duk abinda yake kawai gashinan ne babu karsashi sam tattare da shi,tana jin hamza na kwasarsa kan me ya sanyashi laushi amma yayi masa shiru bai ce masa uffan ba,shi ya tuqasu hakan ya sanya su biyu kenan suka fita,a parking space ya tsaida motar ya kasheta,sai ta kasa fita tana dubanshi kawai,bai dubeta ba ya dage gilasan motar,ya kwantar da kujerar ya miqar da bayanshi a kai,hakan ya nuna bai da niyyar fita kenan,ta jima tana dubanshi kafin tace
"Kayi haquri don Allah" ya jima shiru kafin ya bude idanunsa da suka kada
"Da kikayi me?"
"Na rashin tafiyarmu tare" ta fada tana murza yatsunta
"Ba abun damuwa bane ai tunda bake kadai bace" maganar ta soketa,ranta ya baci,kishi ya soma cinta
"Haka ne" ta fada tana dora hannunta kan mabudin motar ta bude ta fice,ta gefan ido ya bita da kallo,ya rasa yadda zaiyi controlling kanshi,bai taba damuwa da wani abu haka ba,sonta ba qaramin mamaya ya yiwa zuciyarsa ba,yana son ya daure kan rashin tafiyar tasu tare ko don abinda ke jikinta amma ya kasa,tun yanzun kewarta ke damunshi,nan yaci gaba da kwanciya,baison ya shiga ya taddata cikin rashin walwala ko kuka,hakan na tabashi,bashi ya shiga ciki ba sai sha daya na dare.


A falon qasa ya tadda su'ad sanye da kayan bacci,tsaye bakin t.v tana shan ruwa cikin gora,dubanshi tayi tana sakin murmushi,wani dadi ke ratsata a kwanakin nan,ta fuskanci kamar akwai wata a qasa tsakanin sumayyan da almustapha,bugu da qari kuma ga tafiyar da zasuyi daga ita sai shi
"Welcome" ta fada tana murmushi
"Yauwa....baki bacci ba?" Fari tayi da idanu tana cewa
"Wlh ban kammala shirina bane"dubanta yayi cikin mamaki,don bai taba ganinta cikin zumudi haka ba irin wannan lokacin,don ko tafiya ta kamasu tare wano lokaci idan tana wata sabgar saidai su raba flight ita ta biyoshi
"Ya kamata kam ki gama da wuri,don tafiyar safe ce"
"Ba damuwa ai" ta sake fadi tana faari
"Sai da safe" ya fada yana ci gaba da takawa,binsa tayi da kallo kafin tace
"Ok goodnight" ba haka taso ba,so tayi ta bata masa lokaci a nan,har sumayya ta gaji da jira taga bai shigo da wuri ba,koma tazo ta samesu tare.


Sanda ya shiga tana gaban mudubi sanye itama da kayan bacci tana gyara gashinta,kaya ne da bata taba sanyasu ba cikin kayanta,sun bala'in karbar fatarta,abinka da mai yaron ciki,ga wani kyau na musamman data ajiye,kanshi ya dauke ranshi na suya idan ya tuno gobe warhaka basa tare?,har ta kammala shirinta ta kwanta bai gama nashi ba,bacci ya soma rinjayar idanunta,cikin baccin taji ya janyota cikin jikinsa ya rungumeta tsam,shiru tayi ba tare data yi qwaqwqwaran motsi ba,saqonni ya fara aika mata kafin daga bisani su shiga babbar headquater.


Sosai ya moreta tamkar wani mai biyan bashi,sam bata isarshi ko yaji ya gaji da ita,kamar ana sabunta masa ita ne,tana kwance jikinsa baki daya gabbanta sun mutu,amai ya dinga taso mata,ga yunwa da take ji,bata ankara ba ta soma sheqashi,ya miqe da hanzari ya riqeta gam,sai data amayar da duk abinda taci,tana jikinshi bai damu da yadda ta bata shi ba,sai daya gyara mata jikinta sannan ya gyara gadon ya sauya zanin gado ta koma can,yace ta zauna ta huta kafin ta sake kwanciya
"Abinci" ta furta a hankali,da kanshi ya shiga kitchen karon farko ya dumama mata a na'ura sannan ya kawo mata,yana zaune opposite dinta yana kallon yadda take cin abincin hannunshi rungume a qirji,zallar tausayinta ke ratsashi,bai taba zaton haka mata ke dawainiya da shan wahala da ciki ba sai yanzu,a haka har wasu ke iya yadda ayi musu cikin shege?,su haifan yaro su iya yarwa?,ko su bayar?,ko su kashe shi da kansu?,sai ya tuna gidajen marayunshi da irin yawan yaran da ya qunsa,
"A irin wannan halin kikeso na tafi na barki ke daya?" Ya samu kanshi da furtawa a sanyaye ba tare da yasan furucin ya fita ba,dubanshi tayi itama cikin sanyi tace don kewarshi ta fara bugunta tun jiya
"Haka ummi suka tsara,nasan saboda qaruwarmu sukayi hakan,kuma na tabbata ummi zata kula da ni fiye da yadda zaka yimin,dukkanmu ta fimu sanim zafin haihuwa" ko yaushe kalaman girmama iyaye daga bakinta sune gaba dan komai,idanunsa ya lumshe yana jin kamar yace ya fasa tafiyar,ji yake kamar zasu rabu ne ba zasu kuma ganin juna ba,da sauri ya kori wannan mummunan tunanin daga ranshi tare da yin ta'awizi.


*saura naji an zage mustapha tsaf,lol😂😂kada kuyi qorafi,duk dadin zamanku wataran dole a samu sabawa juna*








*mrs muhammad ce*👑

📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖


*~NA~*

*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*

*WATTPAD:HUGUMA*

*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)



9⃣7⃣
*Bismillahir rahmanir rahim*

*Allah madaukakin sarki yana cewa*

*haqiqa Allah ma'abocin falala ne abisa mutane,saidai,yawancin mutane basa gode masa*
______________________________________




        Wani dare suka gabatar wanda kusan rabinshi basu samu bacci ba,sai da suka idar da sallar asuba wanda shi yayi limanci sannan wani bacci mai nauyi ya dauketa,dubanta ya dinga yi saman abun sallahn,tausayinta yake ji,daren jiya kawai amma sai yaga ta fada baki daya,kanshi ya dauke a hankali yana ci gaba da karanta azkar dinshi.

         Bugun qofan aka soma yi a kai a kai,wanda hakan yayi sanadin farkawar sumayya,a hankali ya miqe yana mamakin waye wannan,bude qofan yayi,su'ad ce tsaye cikin kayan bacci tana jifarshi da murmushi
"Lafiya?" Ya tambayeta cikin mamaki,fuskarta dauke da murmushi tace
"Cewa nayi ko zaka zo muje ka shirya" waiwayawa yayi ya dubi agogon dake manne bangon dakin,baki daya qarfe bakwai da minti hamsin da hudu na safe,sai ya maida kanshi wajenta
"Halan baki ji qarfe nawa nace miki zamu tafi ba ko?,sha biyun rana shine har zan fito ma shirya yanzun?" Kasaqe tayi,tayi nufin janyeshi ne,yadda sumayyan ba zata sake ganinshi ba,wataqila ma sai bayan sun dawo
"Shikenan" ta fada gwiwa a sage tana juyawa,ya maida qofar ya rufe sannan ya tako zuwa cikin dakin,tana zaune tana murza yatsunta a inda ta tashin,da alama ba isarta baccin yayi ba bugun shi ya tasheta
"Ina kwana" ta gaidashi kanta a qasa
"Lafiya lau,ya jiki" ya tambayeta yana komawa inda ya tashi ya sake zama
"Alhamdulillah" ta maida masa tana miqewa,toilet ta nufa ya bita da kallo har ta shige.



*Bayan awa hudu*



Kwance take lamo cikin dakin dake bangaren ummi wanda ta ware mata,tun bayan awanni hudu da tafiyarsu babu abinda ta iya tsinanawa sai juyi da take daga farkon gadon zuwa qarshenshi,ba wani loko ko saqo dake jikinta wanda kewarsa sonshi da qaunarshi basu bi sun illata mata ba,hango sallamarsu take da kuma sallamarsu tsakanin shi da ita,hawaye ya gangaro mata ta sanya hannu ta sharce,har ya tafi tana iya hango damuwa qarara kan fuskarshi,furucinsa na qarshe sanda ya sanyata cikin jikinshi suna sauraron bugun zuciyar junansu
"Ki taimakeni ki bini.....ki cewa ummi zaki" a sanyaye ta girgiza kai duk da tana kwance qirjinshi
"Bazan iya ba.......kunya nakeji....kayi haquri" bai sake cewa uffan ba face zareta da yayi daga jikinshi,ya fiddo kudi da kuma daya daga cikin ATM dinshi ya ajjiye gefanta,ya tsugunna gabanta a hankali ya yaye rigar jikinta zuwa saman cikinta,ya dora tattausan lebbansa ya sumbaceta sannan ya miqe,duka wannan abun da yakr yaqi yarda ya dubeta kamar yadda take nacin duban qwayar idanunshi,a hankali cikin takinshi ya juya har ya fice daga dakin idanunta na kanshi.


Ba irin sallamar da takeso suyi ba kenam,saboda haka tunda ya fita take faman kiran layinshi saidai ba'a daga ba,bata daina kira ba har sai da aka tabbatar mata wayar a kashe take,abinda ya sake karyar mata da zuciya kenan har yanzu yake fidda hawaye,zuciya da gangar jikinta baki daya a quntace suke,wunin ranar baki daya a quntace tayi shi,duk da yadda ummi ke nan da nan da ita,duk abunda take buqata dama wanda bata buqata ta tanadar mata shi.


Bata sake tabbatar da cewa lallai almustapha ya zama wani sashe na rayuwarta ba sai da dare yayi,baki daya bacci ya gudu a idanunta,fafur yaqi zuwa,dole ta shiga bandaki ta daura alwala ta yi sallolinta yadda zata iya,duk juyin da zata yi sai ta dibga hangoshi gefanta sanda yake bata kulawa,cikin jikinta take jin tamkar ta rasa wanu babban sashi daga jikinta.


Washegari kallo daya ummi tayi mata ta fuskanci batayi bacci ba,wannan dalili ya sanya ta sanyata gaba sai data tabbatar ta samu isashshen bacci,ta sani fushin mijinta ke damunta,saidai baki dayansu kuwa suyi haquri,don ba zata taba bari wani abu mara dadi ya faru ga sumayya ba,idan da ace su'ad din mai aiki da tunaninta ne babu abinda zai sanyata rabasu,zata barau suyi tafiyarsu tare,amma a irin wannan qadamin da ake ba zata lamunci tafiyarsu wata uwa duniya ba a sanda sumayyan ke da buqatar taimako,a yammacin ranar iyalan adam suma suka shirya komawa lagos wajen mijinsu,sumayya na zaune falon ummi tana kallon wani comedy,babu abinda ya dauke mata na daga kewarshi da take,saidai ya dan dauke hankalinta,anty ni'imah ce ta shigo cikin shirinta,sanye take da doguwar riga ta atamfa da yalwataccen mayafi,bayanta hibba ce da hibban,sai nasrin da


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login