Showing 255001 words to 258000 words out of 364327 words

Chapter 86 - KUNDIN KADDARATA COMPLETE HAUSA NOVEL

HUGUMA   

20 Aug 2024

40107

kiran ya dubesu yana kai wata lomar bakinsa
"To kunji girkin amaryar musty ne" take kowa ya soma yaba girkin,lomar da yayi ta tsaye masa a wuya,sau kawai ya dauki ruwa ya kora ya miqe tana duban hamza fuska a dinke
"Tashi ka kiramin ita mu wuce" dubansa yayi yana qoqarin hadiye abinci
"A'ah man,bamu tattauna komai bafa,dududu ko awa bamuyi ba agidan nan"
"Zaka kira min ita ko sai na shiga dakin da kaina" dariya suke qasa qasa,lamin ne ya dake ya soma masa bayani ba wani abu suke nufi da matarshi ba tsokanarshi kawai suke,hannu ya saka ya daki teburin
"Ce muku nayi wannan ne ya bani haushi,shut up da Allah"yau sunga bala'i sai suka sanya masa ido,miqewa hamza yayi ya isa kafadarshi ya dafa shi ya soma masa magana wanda basa jin me yake ceww,ajiyar numfashi yayi ya juya ya dubesu,sau ya saki qaramin murmushi
"kunci bashi wlh zakusan kunyi da musty,amma kiramin ita mu wuce din kawai na riga da na tashi,after eight zamu hadu a masauki ba case"dariya suka saki baki daya,cikin minti biyi sumayyan ta fito
"amarya ki gaida gida"suka ce mata ta amsa da to tabi bayanshi.

      Tuqinsa yake a hankali saidai har yau abinda ke tokare a zuciyarshi bai baje ba,sau biyu yana satar kallonta,har yanzu mode din damuwa yake iya gani kan fuskarta,ya lura da wayarshu dake ta haske a jakarta amma baice komai ba kamar yadda bata ce masa ba,a zaman kuramen suka isa gida.

       A waje yayi magariba da isha'i,sanda ya dawo da zummar yin wanka sai ya sameta nannade saman doguwar kujera,ko t.vn ma da ya kunna kafin ya fita a kashe take,hakanan yaji ya fasa fita,wayoyinsa biyun da suke gunsa ya kashe ya shiga yayi wanka ya dawo ya sanya pyjamas masu taushi farare qal bayan ya wadata jikinsa da turarensa kamar ko yaushe,tana kwancen bata motsa ba,jikinta duka na arufe sai kanta dake a waje,qwayayen dakin ya kashe ya kunna na bacci duk da a sannan dududu qarfe tara na dare,gadonsa ya haye yaja lallausan bargonsa ya rufa iya qirjinsa bayan ya zauna sosai saman gadon yana karanto addu'o'i,sai yaje yayi bacci da wuri tun kafin abinda ya sha ya soma taso masa.

       Wayar dake saman kanta ta soma haske,hannu ta sanya ta duba,miscal ne da qarin saqonni,tsaki ta ja kamar ta maidata ba tare data gaya masa ba sai taga hakan bai dace ba,mai kiran zatayi tsammanin ya ganu ne bai kula ba,kuma ko banza matarshi ce,motsa bakinta tayi murya can qasa a tausashe kamar maijin bacci tace
"ana kiranka akwai kima sms"
"Tun yaushe?"
"Rana"
"Waye?" Dan jim tayi sannan tace
"Su'ad na gani" shiru yayi yana ci gaba da addu'arsa har sai daya kammala sannan yace
"Me saqon yace?" Kai ta girgiza tana daga kwancen
"Ban duba ba"
"Me yasa?"
"Ba saqona bane,ba kuma hurumina bane" amsar tayi masa,wannan itace cikakkiyar amana
"Ok,karantomin naji" shiru tayi don bata da muradin karantawar har ranta,sai da ya sake maimaitawa,janyo wayar tayi ta bude,a hankali ta isa ma'ajiyar saqonni wanda tunda wayar ke gurinta ko gefan bata je ba,ta dannan saqon daya fara shigowa da fari ta soma karanta masa,idanu ya lumshe muryarta da tayi low tayi sanyi na ratsashi,har ta qare kusan bai fahimci me ta karanta din ba,sai da yaji shiru alamun ta gama karanta saqonnin sannan ya farga,gyara zamanshi yayi tare da bude idanuwanshi
"Banjin me kike karantawar,dawo nan kusa" ya fada yana mata nuni da gefansa,duk da babu wadatar haske amma tana iya ganinsa,ba tare da tunanin komai ba ta miqe tsaye,ta nufoshi tana maida mayafinta daya zame daga kan tulin gashinta dake daure cikin ribbom,a hankali ta zauna daga gefan gadon da tazara mai yawa tsakaninsu qafafunta na zube a qasa ta jingina da fuskar gadon sannan ta sake bude saqon da nufin maimaita masa.








*mrs muhammad ce*👑

📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
[23/02, 11:52] Beesama Zamani Wrt Grp: ✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖


*~NA~*

*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*

*WATTPAD:HUGUMA*

*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)



8⃣3⃣

*Bismillahir rahmanir rahim*

___________________________________

      Idanunsa lumshe murya can qasa ya mata nuni da filon dake daura da shi
"Nan zaki dawo" daga kai tayi ta dubeshi,ganin idanunsa a rufe yake ya sanyata matsowa ta sake rage muryarta ganin tana kusa sosai da shi babu buqatar daga murya,don har tana iya sheqan daddadan qamshin turarensa
"A daga wayata,nasan cewa kana kusa,kana shirin wulaqantani ne kawai,kafi kowa sanin zuwa yanzu zan iya rasa kudi hannuna,naji kuma ka share baka da alamun sauke nauyin dake kanka" cikin harshen turanci ta turo wannan saqon,salon yadda take karanta saqon da tataccen engilishinta ya matuqar burgeshi,ta karya harshe sosai tamkar yarenta,sautin muryarta ya dinga ratsashi ya hanashi sukuni,jin tayi shiru yasa yace
"Uhmmm,ci gaba" ba tare da ya bude idanunshi ba,sake bude dayan tayi wanda shi kuma da hausa ne
"Kana wacce qasa?,ina son nazo na sameka mu warware sabanin dake a tsakaninmu,kafi kowa sanin bazan iya jurewa rashinka ba......"
"Is ok" ya fada yana amshe wayar daga hannunta,don bashi da lokacin saurarar shirmen su'ad din,ya lura ta maidashi wani qaramin yaro,ya tabbata buqatarta ce ta taso,mai hali baya fasa halinsa,ba zata taba canzawa ba,a hankali ta soma motsawa da niyyar sauka daga gadon,caraf taji an ruqo hannunta,da sauri ta waiwayo,still har yanzu idanunsa na rufe
"Ina zaki?"
"Kwanciya zanje nayi bacci nake ji"
"Ni kuma bana jin bacci so ya za'a yi dani?" Ya qarashe fada bayan ya ware manyan idanuwansa fes a kanta wadanda suka sauya launi,sunkui da kai tayi saboda wani abu da taji yana fisgarta,hannunta ya saki yace
"Dawo ki zauna" bata musa ba cikin mutuwar jiki ta sake dawowa gurbin data matsa,saidai wannan karon baki daya a takure take,saboda waiwayowa da yayi yana fuskantarta gami da zubo mata ido,baisan me zaya ce mata ba,baisan ta ya zai fuskanceta ba,bai taba tsammani akwai wata rana da d'iya mace zata yi masa kwarjini ba,shi kadai yasan me yake ji cikin jikinsa,meke zagawa jini da jijiyarsa,tabbas yana buqatar dauki,ya godewa Allah daya kasance akwai halalinsa a kusa,da ya tabbatar yau babu abinda zai hana ya yanki ticket zuwa america,zuwa yanzu nauyin da yake ji ya fara guduwa,ya soma daina fahimtar kunya nauyi izza da isa dake tattare da shi,zuciyarsa ta fara kaiwa maqura,ajiyar zuciya ya sauke
"Bani labari.." Ya fada yana dubanta,a wannan karon yadda mamaki ya kasheta shi ya hanata motsi bare ta dago kai
"Bani da labari" ta yanke masa hanzari tun kafin taji me yake shirin fada,shiru ya ratsa tsakaninsu,yayin yaci gaba da qare mata kallo ta cikin lullubinta wanda mayafin ba wani kauri gareshi ba,numfashi ya fitar da qarfi sannan yace
"Shekaran jiya kin yimin tayin samun 'ya'ya ko?" Ya fada yana duban sumarta wanda mayafin ya zame ba tare data sani ba,sai a sannan ta dago ta dubeshi tana mamakin me ya maido wannan maganar,kanta ta maida qasa tana murza tafin hannunta
"Ta wuce ai,tunda baka da matar da zata haifa maka din"
"Idan kuma ya kasance kece matar fa?" Gabanta ya fadi tsoro ya kamata
"Idan kuma bazan iya ba fa?"wani salon murmushi mai fidda qaramin sauti ya fitar yana matsowa dab da ita
"qarya ne,wanda kika taba haifa fa a baya?"wannan karon ma sai data dubeshi,ya akayi yasan ita ta haifi abdallahn?duk da ya gansu a tare amma ta tabbata baisan itace mamarshi ba,duba da tsawan daya taba yi mata sanda ta mareshi,tsareta yayi da idanuwanshi yana karantarta,tuni tsoro ya mamayeta,idanuwanshin kadai sun karantar da ita me yake nufi,to amma da wacce siga yake son kasancewa da ita,mutumin da bai gama aminta da cewa matarsa bace ma?,mutumin da bai taba cewa yana sonta ko yana qinta ba,ita kam wai a haka rayuwarta zata kasance,ta zama rabon mutum uku kenan nan duniya?,zuciyarta ta karye tana jin wannan karon ba zata iya ba har sai ta tabbatar da matsayi ta,da azama ta sake motsawa da niyyar sauka,saidai ina halittar ba daya bane,cikin zafin nama ya danne rigar baccin tata ta gefe daya ya aza duk nauyinsa,tilas ta durqushe,jikinta ya fara rawa idanunta suka tara qwalla
"ka yima Allah ka barni matuqar kasan ba zaka iya ci gaba da zama da ni ba har qarshen rayuwarmu,kada ka shiga rayuwata daga baya ka fice ka barta" ta fada kuka na qwace mata,baki daya jikinsa sai ya mutu amma hakan bai kashe kaifin abinda yake ji cikin zuciya da gangar jikinsa ba,tabbas ya sani ta taba aure amma baisan me ya rabata da gidajenta ba,abu daya kawai ya sani ya kuma yarda da shi,baban bazai taba zaba masa macen da bata kamaci rayuwarsa ba,tafin hannunshi ya sanya tsakiyar nata yana murzawa a hankali idanuwanshi a kanta,ya tabbatar koma mene wani miki ne dake zuciyarta me yiwuwa take amayar da shi ta hanyar hawaye,a hankali yaci gaba da mutstsuka tafin hannunsu dake hade waje guda,wani abu na yawo cikin jikinsa,sannu a hankali kukan nata ya soma tsagaitawa,har cikin jininta take jin mutstsutsukawar da yakewa tafin hannunta,cikin sanyi ta daga kanta sai ta tsinci idanuwanshi na kanta,kai ya girgiza mata alamun a'ah,sai ta maida sabuwar qwallar dake shirin zubowa,hannayensa ya bude mata baki daya alamun ta taho,haka nan wani shauqi ke jansa zuwa gareta,kai ta kawar gefe alamar ba zata iya ba,birkitota yayi baki daya tayi masauki saman faffadan qirjinsa,jikinsa ya hadu da nata,lallausan fatarta ta sake bashi gudun mawa wajen samun himmar aiwatar da abinda da kaikawo cikin jiki da zuciyarsa,tamkar wanda ake kadawa gangi haka ya dinga tsuma,cikin zafi zafi yaje aika mata da saqonni masu nauyi,wanda har suka nauyaya cikin qirji da zuciyarta,tsoro ya kamata,tunda take bata taba tsintar kanta cikin duniyar daya jefa ta ba,saqonni ne masu rikita qwaqwalwa da kashe gangar jiki,data rasa abunyi sai kawai ta sake masa kuka,sam baya son abinda zai kawo cikas ga abinda ya nufata,yayi nisan da bai tsammanin kira zai dawo da shi,bai buqatar kukanta a wannan lokaci,sai ya hade bakunansu waje guda tare da sake jefata a wata duniya mai nisan gaske wadda bata taba tsammatar akwaita ba.

      Tana kwance saman faffadan qirjinsa duk da kusan shudewar awanni biyu suna a haka amma hakan bai dameshi ba,shauqi ke shawagi dashi cikin sabuwar duniya kamar tsuntsun daya samu sararin sama,abunda bai taba faruwa ba tsakaninsa da su'ad ba,hasalima Allah Allah yake ya tashi ya tsaftace jikinsa,saidai wannan karon jinsa yake wani daban,ya kasa rabata da jikinsa,ya kasa tashi,hakanan ya kasa lallashinta kukan da take fitarwa,saboda yana da yaqinin idan ya lallasheta din akwai wani lallashin a gaba,saboda baijin zai iya barinta aziyara daya,anya daidai kunnensa ya jiyo masa sanda baban ke fadin bazawara ce da yaro guda daya tsaga jikinta ya fito?,har yau ya kasa tantance ainihin duniyar da yake,duk yadda yaso sake koyi da sunna wajen yin alwala amma ya gaza samun wannan qwarin gwiwar,burinsa kawai shine ya koma duniyar da ya fito,kuka ta sake saki sanda ya sake maidata jikinsa,tana tunanin rayuwarta kawai yau yake nema,maganin kukan ya sakeyi karo na biyu sanda ya rufe bakinta gaba daya da nashi.

  ******    *******    ********

      Ya jima zaune saman abun sallar da suka idar da sallar asuba yana dubanta,yayin da take takure waje daya itama kan abun sallar tana zub da qwalla,tasbihi kawai takewa ubangijinta tare da godiya a gareshi,tasan shi kadai ke yadda yaso da rayuwar bawa,sosai kukan nata ke sukarshi,ya rasa ta yadda zai lallasheta,yana jin tamkar bai kyauta mata bane,don me ya gaza haquri ya shiga gonarta ba tare da amincewarta ba,sai ya jingina da gadon yana qarasa azkar dinshi,ya kammala ya shafa,har yanzu bata sauya zani ba,wani mugun firgita tayi sanda taji ya sureta gaba daya,karon farko data yarda suka hada idanuwa tun daren jiya bayan faruwar abun,baki daya idanuwanta suyi luhu luhu sunyi ja,hawaye ne cike da idanun,ya fuskanci me take nufi,tana tsoron ko wani abun zai sake,shi kansa yayi makin yadda taji jiki haka,yadda ya saba tafiyar da su'ad haka yayi mata,dauke kanshi yayi yana ci gaba da takawa har kan gadon,gyara filo yayi ya kwantar da ita
"Ba abinda zan sake miki,bacci kawai nakeso kiyi" ya fada yana ja mata bargo zuwa kafadunta,luf tayi tana sharar qwalla gami da fitar da ajiyar zuciya
"I hate crying" taji ya fada
"Idan baki daina ba kuma zan miki abinda bakyaso" har ga Allah tsoronsa take ji,bata marmarin sake gamuwarsu,sai ta rage jan hancin da take,kashe qwan dakin yayi tana jinsa ya bude qofar ya fice ba tare da tasan inda zashi ba,a hankali idanuwanta suka fara nauyi,bacci mai dadi ya sureta wanda batayi tsammanin zuwanshi nan kusa ba.

         Minti talatin ya dawo a sanda yake zaton tayi bacci,sai ya janyo kujerar soso ya dawo da ita gabanta bayan ya kunna qwan dakin,qaramin qur'ani ya dauka cikin ma'ajiyarsa ya bude ya dora da tilawarsa daga inda ya tsaya cikin zuciyarsa yake yi,saidai lokaci lokaci yakan daga kai ya dubeta,fuskarta ta sake wani haske,kamar yadda kan hancinta da saman idanuwanta suka yi ja sabida kukan data sha,hakanan tausayinta ya dinga ratsashi,baisan tausayin na meye ba,ya dinga tuna wasu abubuwa da ya gani game da ita tun daga sanda igiyar aurensa ta hau kanta zuwa yau,yasan dai koma me yayi halalinshi ya karba,amma baisan me yasa yake jin wani bawai ba,ganin bai fahimatar karatun sai kawai ya rufe qur'anin yaci gaba da kallonta,har yanzu akwai lema kan zara zaran gashin idanuwanta,dan qaramin bakinta wanda kalarshi take pink ya kalla,sai ya lumshe ido yana jin wani sabon shauqi na taso masa,ba shakka tilas su bar hotel din nan su koma gidansa kowa ya kama dakinsa,idan ba haka bai baijin zai iya jure ci gaba da zamansu a muhalli daya ba tare da faruwar wani abu ba,bazai iya kallon giftawarta ta gabanshi ba tare da yaji komai ba,murmushi ya kufce masa sanda ya tuhumi kansa yaushe ka koma haka almustapha?,bai mancewa yakan jima baiji wani abu akan su'ad ba,wani lokaci har sai ta nemeshi sannan zaiyi ashe akwai feeling tattare da shi,har qorafi take masa bai zuwa wajenta saidai idan ita ta matsu ta biyoshi,hannunsa ya sanya qasan gadon ya ciro wayarshi wadda tun jiya ta fada,yama manta da su hakanan baibi ta kansu ba sai yanzu,kunnasu yayi baki daya har ta hannunta wanda ta soma karanta mishi saqo,murmushi ya sake saki sanda ya tuno yadda take karanta saqon a tsare cikin muryarta mai dadin amo,yadda kowanne harafi take furtashi cikin qwarewa,baisan yaushe yakai gareta ba,murmushi ne kwance saman fuskarshi yana zancan zucinsa shi kadai,saqonnin su hamza lamin musaddiq ne suka dinga shishshigowa a jajjere,dan qaramin tsaki ya ja,baki daya ya mance da cewa ya musu alqawarin zasu hadu a masaukinsu jiya da daddaren,baibi ta kan saqonnin nasu ba ya soma lalaubar lambar kamfanin da suka yi mishi aikin ginin gidansa,ba bata lokaci suka daga ya basu umarnin qarasa dukkan sauran abinda ya rage cikin gidan tare da basu kalolin furniture din yake so a zuba dakinsa da daya dakin
"Sir sauran dakin fa?" Waiwayawa yayi ya dubeta,baison wanne kala tafi so ba,dauke kanshi ya sakeyi
"A sanua orange da fari" ya amsa musu,bai ajjiye wayar ba sai da ya musu transfer na dukka kudin da ya rage.

      Yana shirin ajjiye wayar kiran baba ya shigo,a ladabce ya daga kiran yana gaida baban,yayin da yake amsawa shima tare da tambayarsa harkokinsa,ya tabbatar masa komai lpy
"Masha Allah,ina fatan komai yana tafiya dai dai ko?"
"Komai lafiya baba"
"To madalla,kadai kula da amana,Allah yayi maka albarka ya sake hada kanku"
"Amin ya Allah,Allah ya qara girma,ya jiqan mahaifa ya saka da alkhairi" ya samu kanshi da kwararowa baban addu'o'in
"Amin ya Allah,ga umminka ita keson magana da kai" ya fada yana miqawa ummeee wayar,cikin girmamawa ya gaidata ta amsa tana fadin
"Ina amirata?" Sake dubanta yayi,tana baccinta cikin nutsuwa,karon farko daya taba ganin wani mutum wanda bacci ya yiwa kyau irin haka
"Nace ina amira?" Ummen ta sake maimaitawa jin shiru bai amsa ba,sam ya mance tan kan layi
"Tana bacci ne ummee"
"Ba rana ta soma fitowa ba nan?,Ina fatan dai lafiyarta qalau ko?" Kunya ta kamashi,yana ganin kamar ummeen zata fahimci wani abu,cikin qoqarinsa nason boye komai yace
"Lafiyarta qalau,kawai batai isashshen bacci bane jiyan....." Da hanzari ya katse maganar da yake sanda ya soma fahimto zaiyi baran barama
"To madalla,ka gaisheta idan ta tashin,anty maamaa tana gaidaku"
"Zataji insha Allah" ya fada yana datse layim cikin hanzaei,idanuwa ya fitar waje yana furzar da iska daga bakinsa.

       Daya wayarce ta soma ringing,da sauri ya amsa kiran yana duban sumayya dake kwance,haka kawai baya son ta tashi,hamza ne tashi yayi ya koma saman doguwar kujera ya miqe a can sannan yace
"Lafiya malam da zaka damu mutane da kira da sassafe haka?" Dariya hamza ya bushe da ita
"Wai ko ba musty na kira bane?"
"Ban sani ba dan iska,da bakasan waka kira ba?"
"Dole na fadi haka,amazingly na kiraka kana na tasheka da sassafe,naga kai din baka da lokacin kira,any time ur available" yasan tabbas magana ya gaya mishi don hakan yake,su din ne har basu so a fiddasu daga gida da daddare ko a sasu tashin wuri,hakanan yau yake jin kansa shima as magidanci ,yake jin kansa wani na daban,ashe haka suke ji idan aka kirasu da sassafe haka,shi daya ne baya damuwa saboda baisan ana jin haka ba idan aka kira mai iyali da wurwuri ko idan dare ya fara turawa ba
"Naga alama ka fara rainani wallahi hamza,ni kake gayawa am available always?"
"To qarya nayi,idan banda rainin wayo jiya saika shanyamu muna ta jiranka har sha daya na dare na baro abida ita daya a gida?"
"Sannu tattabara sarkin aure,to nima fitarce bazan iya ba na bar....." Idanunshi ya dauke ya dora a kanta yana ware mata kallo,sai ya rasa sunan da zaya kirata da shi,dariyan da hamza ya qyace da ita ta sanyashu runtse ido,hayaniyar har tsakiyar kansa
"Hey,ar u mad,a kunnena kake wannan gadar?"
"Aci amarci lpy my maan,sai ka fito" ya fada yana datse kiran,maimakon yaji haushi yadda suka saba yi da hamzan sai murmushi ya subuce masa,ya sauke wayar daga kunnensa yana kwanciya rigingine yana kallon saman dakin,hannunshi kan sumarshi yana shafata a hankali,jinsa yake fresh tamkar wani sabon mutum,wani farinciki ke ratsashi
"Iyalina,matata,mata ta na bar ta


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login