Showing 237001 words to 240000 words out of 363280 words

Chapter 80 - DUNIYATA BOOK 2 COMPLETE

HUGUMA   

11 Nov 2025

1391

ya sauya akalar tunaninta na taci gaba da riqon laila.

Zuwa yanzun lailan ya fara zame mata kaya,don ba wani abu da zata iya aiwatarwa na qashin kanta saita tambayi maamah din. Daidai da cin abinci wannan sai data fatattaketa,tace kada ta qara tambayarta don zataci abinci,taci ko kada taci wannan ya rage nata.

Ko yanzun da akayi mata knocking sai data ja tsaki,tasan bazai wuce laila din ba,don cikin masu aikinta ba wanda ya isa ya qaraso nan wajen sai idan ita ta nemi ganinka.

"Waye?". Ta tambaya cikin 'yar qaramar fusata.

" Laila ce".lailan ta fada jiki da muryarta dukka suna rawa. Har ta bude baki zata koreta,sai kuma taji kaman akwai raunana a muryarta don haka tace

"Meye kuma?,kinsan banason damu ko?".

"Kiyi haquri.....wani abu ne ya faru nazo nuna miki,nima yanzu naga an sakashi a page din jaridar breakers".

"Shigo" Ta bata dama kai tsaye tanason jin me tazo dashi.

Sanda ta shigo jikinta yana rawa ta miqa mata wayar hannunta. Hannu ta sanya ta karba cikin yamutsa fuska sai kuma ta waro idanunta dukka waje.

"AN KAIWA SHARARREN MATASHIN ATTAJIRIN NAN FARMAKI A FILIN TASHI DA SAUKAR JIRAGEN SAMA HARI WATO MUHAMMAD FU'AD JADDA.....HARMA ANA KYAUTATA ZATON BACEWARSA.....YANZU HAKA BA'ASAN INDA YAKE BA". Sake qarewa rubutun kallo tayi da kyau,ta maimaita rubutun ta sake maimaitawa sai kuma murmushi ya subuce mata duk da zulumin daya cika wani sashe na zuciyarta.

"Lokacin tarwatsewarki ameenatu yayi.......tabbas wannan itace dama ta ta farko a kanki kafin na isa ga dama ta biyu na qarasa murqusheki.....na kuma jefa rayuwarki data ahalinki cikin halin ni 'yasu" Tayi maganar a sararin tana jin dadin samun wata gwagwgwabar dama da ta sameta ta sassauqar hanya.

Idanunta ta zube akan laila dake kallonta kawai.

"Kina da hanyar da zaki hadamin 'yan press?,ina da buqatar gabatar da taron 'yan jarida.......ya kamata na fara gwadawa ameenatu nawa salon da kuma ainihin kalata" Kai laila ta girgiza.

"Bansan yadda zamu kirasu ba.....amma ina da qawa da take aiki gidan radio.....zan shaida mata sai suzo din".

"Hakan yayi.....gobe da sassafe nake buqatar su hallara a harabar gidan nan,bayan gida radio dinsu ina buqatar ta qara da gayyatar wasu kafafen yad'a labaran dama na jaridun......zan biyata akan wannan aikin gayyatar" Maamah tayi maganar tana lalubar number musaddiq,can qasan ranta baqincikin yadda musaddiq ya kasa kiranta a matsayinta na mahaifiyarsu ya shaida mata abinda ya farun sai a rariya ta gani.



*_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_*
08187255862

5?? 5?? 5?
? 5?? 5?? 5?? 5?? 5??
_Zafafabiyar_

6B6O6O6K 62

g,D? D? ?

5?K?5?


https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX



120


Dab da zata tsinke ya daga,kafin yakai ga gaidata ta amshe

"Duk tsiya tuwo dai sunansa tuwo.....kuma.basai kayi hakan ba zaka tabbatar min ni ba komin komai bace a wajenku.....abu ya samu dan uwanka musaddiq saidai naji labari a wani wajen?,yanzun kuna ina?". Tafin hannunsa ya sanya ya riqe goshinsa saboda yadda kansa yake sarawa......ta dage ita kuma still saita qara masa wani ciwon.

"Muna asibiti" Ya amsa mata a taqaice.

"An ganshi ne?" Ta tambaya yana fargabar bayyanarsa kafin ta qullawa ameenatu jakar tsabar data shirya qulla mata.

"Adda sabreen ce....."

"Tayi bari?" Ta qarasa masa da abinda zuciyarta ke fatan ya kasance. Sai daya janye wayar a kunnensa yana dubanta kafin ya maida cike da mamaki.

"Wanne asibiti ne?" Ta tambayeshi tana kauda waccan tambayar ganin bai bata amsa ba.

"Noor hospital" Iya abinda dama takeson ji kenan,tana kuma da buqatar zuwa idan barinne sabreen din tayi ta karbi barin da hannunta ta taho dashi nan ta bawa karnukansu su cinye su shanyen jinin,ta kuma aikawa sabreen din video din ta yadda zai zame mata wani mummunan ciwon.

Sharp sharp ta shirya,ta kuma kira driver ya fidda mota suka wuce noor hospital kai tsaye.

Masifa ta dinga yiwa driver din,tana ganin kaman baya sauri.....kamar ba zai isa akan lokaci ba. Cikin qasa da minti arba'in sai gashi cikin noor hospital saboda uban gudun data sanyashi ya dinga zubawa.

"Scanning din da mukayi mata ya kasa bamu ainihin abinda mukeson gani.....saidai mun samu nasarar ganin two embryos,hakan yana alamta akwai d'a biyu cikin mararta.....iya abinda muka gani kenan,mararta akwai nauyi da aiki fiye da marar me dauke da yaro guda daya....so that dole ta dinga kiyaye wasu abubuwan.....bacin ranta.....aiki me wahala da nauyi da duk abinda zai sanya mata stress.......babies din suna lafiya......amma idan ba'a basu kulawar data dace ba.....komai zai iya faruwa" Bayanin likitan kenan da dukkaninsa ya sauka a kunnen maamah data shigo dakin da qarfinta,saidai ta samu annin da dr mubeena tana mata bayani a parlor din dakin da sabreen din take.

"Za'a kiyaye in sha Allah Dr...." Anni ta fada jikinta yana sanyaya,tana sake girmama hukuncin ubangiji da girman qudurarsa da zatinsa.

"Allah kaine Allah,baka da abokin tarayya Allah.....yadda ka samar da wadannan halittu naka a mahaifar mahaifiyarsu cikin wani salo da hikima irin naka.....Allah ka fidda mahaifinsu ka kiyayeshi daga dukkan hadari" Anni tayi adduar da take har zuciyarta ba tare da tasan da wanzuwar maamah a wajen ba.

Duk da taso tazo ta samu gudan jinin yaron a leda amma saita samu akasin haka.....daga tunanin yaro daya ya koma biyu....bugu da qari ma kuma ana bata tabbacin raunanniyar lafiyar da suke da ita.....to amma har yanzu tana da sauran abinda ya rage wanda zata girgixa duniyar anni.....a yanzu zata gudanar da plan A......plan B din kuma ta ajewa kwanakin da suke zuwa a gaba.

"Zaki gama munafuncinki tsaf.....da duk wata munafukar addu'arki ki gayamin inda kika kaimin d'ana.....ni dama nasan za'azo wajen.....ko ba dade ko bajima dole sai kinyi yunqurin salwantarmin da yaro saboda ki handame abinda ya mallaka......to wallahi baki isa ba......ni mariya nice uwar FU'AD,bazan kuma qyaleki ba idan yarona ya salwanta". Cak anni ta dakata daga buda qofar ainihin dakin da sabreen ke ciki,waiwayowa tayi a nutse cike da mamaki tana duban maamah din

"Mariya?,kinsan abinda bakinki yake fada kuwa?". Wani kallo maamah ta watsawa anni,cike da alfahari da samun tabbaci akan qudurinta.

"Na sani mana ameena.....kina tunanin ba'a hayyacina nake ba?.....UWAR RIQON MUHAMMAD JADDA TAYI KIDNAPPING DINSA SABODA NEMAN KUDIN FANSA......A HALIN YANZU BA WANDA YASAN INDA TA BOYESHI....ya kikaga taken wannan labarin a gidajen rediyoyin Nigeria africa dama duniya gaba daya?" Har tsakiyar kanta anni taji wani abu ya tsarga mata

"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un"

"Dama ki riqe abarki zuwa gobe.....don kuwa goben warhaka bana tunanin kina cikin masu cikakken 'yanci kamar haka". Ta qarasa fada tana takawa hankali kwance tana wucewa dakin da sabreen din take.

Duk wata jijiya ta kanta ta gama tashi saman goshinta,ba abinda qirjinta yakeyi sai bugawa da wani irin matsanancin fushi. Kowacce kalma data fita daga bakin maamah a kunnen sabreen ta sauka wadda ke zaune ta jingina da fuskar gadon tana kokawa da kanta ta samu tasha tea din ko babu yawa.

Zubawa maamah ido tayi sanda take shigowa dakin,qasan ranta cike da damuwar yadda ta samu sabreen din zaune sosai.....ba wani alamu na fitar hayyaci ko jigata a tattare da ita.

Kallon kallo sukewa junansu,yayin da kallon da sabreen ke ajiye mata ya kasance wani qazamtacce kuma wulaqantaccen kallo da bata taba ganin irinsa ba a kanta. Hakan bai sage mata gwiwa ba,taci gaba da takowa har ta qaraso dab da gadonta sannan ta janye dubanta daga kanta ta maidashi kan ledar ruwan da aka gama qara mata.

"Inda zan baki shawara ki dauka......da zaifimiki kyau salin alin ki kwanta a zare miki cikin nan cikin girma da mutunci......"

".......idan ba haka ba zaki sanya a kwantar dani a kasheni sannan ki qwaqule abinda yake marata?" Lafuzzan suka fita da wani irin fushi da yaja hankalin maamah din zuwa gareta.

Wani zazzafan kallo take sauke mata tana kuma ajiye mug din hannunta.

"Eh ina nufin abinda na fada din......kina zaton don kin aikata hakan zai bani mamaki?" Ta jefa mata tambayar tana dage dukka girarta sama,sai kuma ta girgiza kanta.

"Ko kadan bazanyi mamaki ba......matar data zabi duniyarta akan lahirarta?,.....matar data zabi salwantar yaranta ta tsira da qazantar duniya wato kudi!......ke nake zargi......ke nake zargi da harbin FU'AD!......ke nake zargi da batarmin da MIJINA UBAN 'YA'YANA......" Ta qarasa maganar tana dora hannunta saman mararta,wasu zafafan hawaye suna taruwar mata.

Sosai maganar ta zowa maamah a bazata,amma bata dauketa da wani muhimmanci me yawa ba tunda tana ganin sabreen din bata da wani power hujja ko damar da zata iya aiwatar da komai a kanta.

Girarta ta dage duka tana yiwa sabreen duban mamaki,wani qaramin murmushin rainin wayo yana fita akan fuskarta

"Ko?......sannu tattabara uwar aure.... Sannu me miji,to idan nidince fa?,sai yaya?". Idanu sabreen ta zuba mata kafin wani kwantaccen murmushi ya sauka saman fuskarta,abinda ya soma sanyawa maamah dawowa hayyacinta. Ba jiya ko yau ba,ta sani murmushin sabreen din bashi da dadi

"Kina daukan abun da sauqi ne har haka ko?.....haihuwar muhammad da kikayi hakan bazai qareki da komai ba a sanda kike qoqarin rabani dashi......haihuwarsa bazai qareki da komai ba a sanda kike qoqarin tabamin shi....lafiyarsa hankalinsa ko dukiyarsa........ko waye yayi gigin tabamin DUNIYATA sai inda qarfina ya qare........ciki kuwa harda ke......ke mahaifiyarsa wadda tayi rainonsa na shekara sha hudu kawai......fu'ad DUNIYATA ne.....duniyar da ko mutuwa nayi za'a binne ni a tsakiyarta".

Wani gigitaccen yanayi maamah ta shiga,idanunta bibbiyu duka a warwaje take kallon sabreen din. Kalaman yarinyar na yau sun girmi hankalinta,saidai duk da haka zuciyarta tana tuna mata ita din MARIYA CE FA.....giwa kuma kota fadi tafi qarfin wawa.

"Kinyi kuskuren fara son abinda nice silar zuwansa duniya......"

"Amma ina me farincikin bake kika halicceshi ba ko?" Ta maida mata idanunta tsaye a kanta.

"Ba wani doguwar sa'insa bane tsakanina dake kodon albarkacin wannan dake kwance a marata...." Ta fada tana nuna cikinta da yatsa.

"Sassauqan umarni ne na ki fiddomin mijina ko ina ya shiga.......awa ashirin da hudu kacal kike dashi.....sannan......taron 'yan jarida karki fasa.......hakan shi zai sauqaqewa muhammad sanin asalin launin kalar mahaifiyarsa" Ta qarashe maganar tana daga mata wayar hannunta.

"Maimakon zazzafan labarin uwar riqo me kidnapping dan riqonta.....wataqila sai labarin ya canza akala zuwa labarin BAQAR UWA" Ta qarasa fada da wani mugun confidence daya nuna har cikin idanunta.

Wani gigitaccen kallo maamah ke yiwa sabreen din,wannan wacce irin BAQAR JARABA ta hadu da ita?,sam sam ta mance da batun video da yake cikin wayar,lallai kuwa da ta nemi hanyar da zata salwantar dashi,saidai a yanzun ba salwantar da video din kawai take nema ba......tana neman sassauqar hanyar da zata shafe babin sabreen......ta kuma shafe labarin rayuwarta gaba daya daga duniya.

Ko sau daya itama bata daga qafa daga kallon maamah din ba,a wannan karon tanajin takai maqura.......itama takai qarshe,kuma ko meye zai faru saidai ya faru. Ko kadan bata yi mata kallon bil'adama cikakkiya a yanzun. Tanajin ta shirya tunkarar kowanne yaqi,ta shirya tunkarar kowanne qalubale akan muhammad fu'ad dinta......tana jin ta shirya ta sadaukar da komai a kansa koda hakan yana nufin salwantar numfashinta.

Tsaiwar maamah a wajen yayi mata,don tana jin akwai sauran maganganu daya kamata ta gaya mata,idanunta suna lumshewa da wani irin bacin rai,mararta tana murda mata da wani irin ciwo ta kalli maamah

"Ina kyautata zaton har yanzu bakisan asalin wace sabreen ba......amma lokaci ya kusanto da zata shaida miki ainihin kalarta.......har yanzu baki tunzura sabreen ta nuna miki wace ita ba......to amma yanzu anzo wannan gabar.....duk inda za'a juya duk inda zakiyi ki tsaya tsakaninki da ita,huda nadra haneefa anni farouq musaddiq da saddiq.......uban gayya DUNIYATA fu'ad......wadannan din ahalina ne.....jinina ne,iyaye kawunnai kuma kakannin abinda yake yake cikina ne,uwa uba me gayya DUNIYATA jadda.......taba daya daga cikinsu?" Saita girgiza kanta tana sake tsareta da idanu.

"Bazai taba zame miki abu me sauqi ba.....jeki gwada idan zaki iya.....zabi ya rage naki.....nima wayewar garin goben nake jira.....ki tara 'yan jarida.....idan kinso kiqi nemomin mijina kiga yadda DUNIYARKI zata tarwatse a karo daya" Takai qarshen maganar rashin tsoronta qarara yana bayyana.

"Idan kin fita ki rufen qofan" Sabreen da amai ke tasowa ta fadi tana zamowa a nutse daga saman gadon ta doshi bandaki da 'yar sassarfa gudun kada ta zube aman a wajen.

Dif tayi tana sauraren sautin yunqurin aman da takeyi daga bandaki.....wasu irin taurari suna zagaya kwanyarta tun daga gaba zuwa baya

"Wacce irin lalacewa ce ta sameki MARIYA?" Ta tuhumi kanta da kanta tana jin wani zazzafan gumi yana karyo mata.


*_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_*
08187255862

5?? 5?? 5?
? 5?? 5?? 5?? 5?? 5??
_Zafafabiyar_

6B6O6O6K 62

g,D? D? ?

5?K?5?

https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX



121


Daga nan inda take tana iya jin kakarin aman sabreen da take kwarashi da wani irin wahala da kuma galabaita. Aman tana yinsa ne da dukka zuciyarta da wani irin karyewa da sarewa,wani irin rauni ne yake cikata a duk sanda ta tuna
"Ba fu'ad a gefanta.....qarfinta.....rayuwarta......kuma duniyarta gaba daya,hasalima ba wanda yasan yana ina......yana raye ko ya mutu,me gobensu zata haifar musu su duka?".

A maimakon tausayi dake sauka zuciyar kowacce 'ya mace a sanda taga 'yar uwarta mace cikin hali na ciwon laulayi saboda sanin ciwonsa da tsananin da yake dashi......a bangaren maamah fitar aman sabreen sai takejin kamar wani sauti ne na barazana a gareta......kamar wani sauti ne dake gaya mata dukkan komai naki ya kusa zuwa qarshe.....asirinki zai tarwatse muddin haduwa da tabbatuwar alaqa yaci gaba da wanzuwa tsakanin sabreen da fu'ad.

"Ya zanyi na cire cikinnan?,ya zanyi na rabata dashi?" Abinda zuciyarta ta dinga gaya mata kenan da wani irin qunci da tsananin takura.

Yunqurin aman shi ya sanya anni qarasowa cikin dakin da wani irin mutuwar jiki da sarewa,zallar mamaki da kuma tsananin tsoron hali da kuma dabi'ar maamah din.

Da baya da baya ta dinga tafiya har takai bakin qofar dakin,idanun maaman akan anni,haka idanun anni din itama akan maamah,saita juya tana fuskantar qofa ta murdata ta fice.

Asalin gigicewa takeji gaba daya har cikin kwanyarta,me yasa duk wani motsi da zatayi sai yarinyar ta zame mata cikas?.....me yasa take zamewa rayuwarta da duk wani motsinta matsala ne?,yaya akayi ta gayyato matsala cikin rayuwarta?. Idan ta duba ta sasanni da dama sai taga takunta na baya yafi kyau......takunta na baya yafi fita akan wanda take fafatawa bayan shigowar sabreen rayuwarta. Batasan me ya dauki hankalinta ba tun a wancan lokacin da har tabar yarinyar da video din bata salwantar dashi ba,ko a sannan tana ganin bata da wani power.....ba kuma abinda zata iyayi?,ko wannan shine sila?.

Cikin tausasawa da tausayawa anni ke riqe da ita,tun tana iya fitar da dan abinda ta samu kurba har ya zamana ba komai cikin aman sai yawu kawai,abinda ya qara adadin galabaitarta kenan,don tanata yunqurin aman kuma babu wani sauran abinda yayi saura a cikinta. Wani hawaye na taru idanun anni sanda take kwance ana qara mata ruwa gudun kada galabaitar ya taba lafiyar yaran da suke cikinta,tausayin sabreen din yana ratsa anni sosai. Ta sani ba abu bane me sauqi wajen mace ta shiga irin wannan yanayin.....ko ita a baya data taba rasa abba,bawai rashi na mutuwa ba,aah saidai rashi na rabuwar aure na dan lokaci,ita kadai tasan me taji,ita kadai tasan ya taji.....ita kadai tasan abinda ta fuskanta,to ballantana wannan,wani yanayi ne da babu tabbas ko sahihancin zance akanshi.....wani yanayi ne da ba wanda yake da tsayayyen abun fada akai. Gefe daya lalurar ciki.....ga qananun shekaru,ga kuma uwa uba me kankat wato MARAICI.

Ta wani bangaren kuma abinda ke daga mata hankali shine.....irin maganganun da taji ana musaya tsakanin maamah da sabreen,wanne irin makami yarinyar ke dashi har haka da ya girgiza mariya farat daya?.

Batasan adadin lokutan data share a zaune gaban sabreen ba,tana riqe da carbinta wanda har yatsunta sun fara zafi saboda riqonsa. Dare yayi nisa sosai,ita kadai ce kawai,don ta hana kowa zama tare da sabreen din sai ita,gani takeyi babu wanda zai iya kula da ita irin yadda takeso,gani takeyi dole ita kadai ce zata iya bata wannan kulawar.

Yadda taga rana haka taga dare,sau daya tak sabreen ta farka tsahon daren zuwa safiya,ta bada tea dan kadan,bacci ya sake kwasheta ta koma.

Sai anni take ganin baccin yafi zama alkhairi akan ta zauna idanun ta biyu tana kuka,ko ??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????don saboda lafiyar yaran da take dauke dasu.

*_WASHEGARI_*



Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login