Showing 204001 words to 207000 words out of 363280 words

Chapter 69 - DUNIYATA BOOK 2 COMPLETE

HUGUMA   

11 Nov 2025

1433

Allah bazai wofantar da addu'ar da aka dauki tsahon lokaci ana qwanqwasa qofarsa saboda ita ba.

Duk wasu kaya nata tunda sukazo wajen tayi bankwana dasu,daga kayan safiya zuwa na dare duka tana shigarta ne a bisa zabinsa. Tun tana dojewa har ta fara ragewa,don idanma tace zata musa shi zai tubeta ya kuma sanya matan. Yayi amfani sosai da damarsa......yayi amfani da tsoronta da gurin ya mata wani irin sabo da kwana a jikinsa,ya sanya wata shaquwa me qarfi a zuciyarta da wannan. Ranar farko da hakan ta fara kasancewa.....
Tayi wani irin bacci da idan zata iya tunawa irin baccin qarshe da tayi saman cinyar ummenta ranar da asthma dinta ya tashi. But bacci cikin jikinsa yana da wasu qa'idoji da ta kasa kiyayesu har yanzu. Wani sabon abune kwanciya hakanan ba tare data rabawa jikinta komai ba....shi kuma kullum sai ya maimaita mata bayan ya maidata yadda yake

"That's my rules". Daga qarshe wayo yake mats,wayon da yake sanyawa washegari ta tashi da matsananciyar kunyarsa da bata iya hada idanu dashi.

Duk yadda taso ta gano yadda yake iya cimmata ya firgitata ya fiddata daga saitinta ta kaucewa wannan abun amma ta gagara......wani lokaci har jira takeyi yayi wani motsi don tayi masa tawaye.....to amma da an iso gurin sai ya sanyata ta manta wacece a ina kuma take?,sai bayan qura ta lafa ta isheshi da kukan banza da qorafi. Wani lokaci ya biye mata ya lalace wajen rarrashi.....wani lokaci kuma yaja hancinta

"Har yanzu baki fara koyan maida martani ba......am dreaming about it,saikin gama kwashe alkhairan kuma ayitamin kukan abunga...." Gulma tason yakeson cewa,fadi ne kawai bazaiyi ba.

"Sabrrrr" Ya kirata jikinsa yana sake macewa. Wani irin Palazzo ne a jikinta da wata 'yar top data zauna mata sosai a jikinta,ta kuma bayyana masa albarkatun qirjinta yadda yakeso. Kanta yasha hair pins wanda shi ya zauna ya shiryata,ya kuma gyara mata kan yadda yakeson gani.

Yasha wahala sosai wajen nesanta kanshi da mata,ya kame kansa,ya runtse ganinsa ya kuma kiyaye al'aurarsa.....wannan ya sanya yaci alwashin ko meye dake burgeshi game da mace sai yayi qara'insa a jikin matarsa......sai ya kalla yadda ranshi keso. Yana ankare da ita a takure taka,yasan zaayi hakan,don shima ko sau daya bai bari idanunsa sun huta da kallonta ba.

Duk sanda yaga dari darinta akan sakin jiki ga d'a namijin da ya kasance mijinta sai yaji wani qunan rai da bacin rai ga wadanda suka dinga sadakar mutuncinta,suka kuma dangantata da sunan KARUWA.

"Zo kiji" Ya fada a galabaice yana miqa mata hannunsa sanda tazo gilmashi. Baima bata lokacin tunani ba ya sanya hannunsa ya jawota saman cinyarsa yadda ya saba mata. Sam bata masa nauyi wajen dauka ko jawowa,kaman wata leda yake daukanta.

Matseta yayi a jikinsa yana rungumeta sosai,ya kuma dauko system din ya aza saman cinyarta yana saka password dinsa.

"Massages nakeson dubawa amma gaba daya kin hanani sukuni.....sai rarrabamin hankali kike,gwara ki zauna mu duba tare,wataqila nafi samun nutsuwar dubawar"

"Me nayi kuma?" Ta tambaya a shagwabe. Hancinta yaja yana kashe mata idanu

"Aah hajiyata....komai mafa kinyi.....satar da kikayi a gangar jikin muhammad fu'ad.....zuciyarsa dinnan ta tafi kenan,bana jin zata dawo masa har abada" Ya fada yana sakinta gami da fara buda saqon farko wanda ya sakashi sakin murmushi ganin saqonnin farouq a jejjere a jejjere. Na qarshen ya fara budawa wanda bai wuce mintuna talatin da turowa ba.

_"You're rocking the boat,you're fanning the flames.......dude.....ka shiga hankalinka ka dawo gida.....yaqi zai barke tsakanin ummominka.....am serious dude"_ shine saqon qarshe daya gani mintuna talatin baya. Dan murmushi ya saki yana tabe baki,yasan abinda farouq zai masa qarya.....ya kuma san wanda bazai masa qarya ba,wannan state??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????ment din nashi yasan real ne ba wasa yake masa ba,sai ya danna replies ya soma bashi amsa

_"Step back BB.....leave them.....nasan anni ba zata biye abun yayi worst ba.....ina nan ina neman hadin kan DUNIYATA.....zamu hadu a airport ranar Tuesday to makka in sha Allah"_ yana tura masa ya koma duba ragowar saqonni masu muhimmanci yana ragewa,saidai kusan bayan kowanne minti daya sai ya tura kansa cikin rigar ta. Tureshi tayi har sau biyu,ana ukun yayi warning nata

"Idan kika sake ban yafe ba" Idanunta dukka ta fidda idanunta waje tana dubansa a mamakance,rai ya hada

"Yes....aikin karanta walau alattanur ko wajen rumaisa?" Qasa tayi da kanta tana tunawa da hadisin,ya kuma aza mata wata irin kunyarsa sosai. Yadda yaga tayi ya masa dadi.......da gaske karatun yana kama zuciyarta har haka,tsaf fa zai iya komawa wajen malam ci gaba da daukan karatuttukan da zasu sanyashi sake sanyata ta sake zama sassanya.....buqatar maje haji sallah. Yadda tayin ya bashi daman dauke hannuwansa daga can system din ya maida inda yafi muradi da wani tattausan yanayi yana sake shigewa jikinta.

"So kike na zama dan is......" Batasan ta saka tafin hannunta saman bakinsa ba.....batasan sadda hakan ta kasance ba sai data tsinciki narkakkun idanunsa cikin nata,hakan sai ya zama kaman wani lasisi ta bashi kenan daya sakashi yunqurawa dauke da ita,daidai sanda saqon farouq da mamakin fu'ad din ya kasheshi ya shigo system din,ta baya ya saka qafa ya tureta ba tare daya damu da idan ta fadi zata iya fashewa ba

"Just leave me have this moment,don't dampen the mood" Yayi maganan kaman wanda yasha giya ya maku,saidai duk da hakan abun mamakin shine,sanda ya mata masauki saman tattausan gadon da harshensa dake hardewa yace da ita.

"Let me relish this moment,and then I'll tell you more about fu'ad. Ya kamata kisan waye fu'ad......am ready to make you DUNIYATA da gasken gaske.......inason kisan komai nawa da gaske......".




*_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_*
08187255862
5?? 5?? 5?
? 5?? 5?? 5?? 5?? 5??
_Zafafabiyar_

6B6O6O6K 62

g,D? D? ?

5?K?5?

105


_Barkanmu da dawowa,fatan munyi sallah lpy,ubangiji ya maimaita mana cikin lafiya aminci da kwanciyar hankali_




Batasan me yake tsarga mata ba duk sanda ya kirata ta DUNIYATA ba,wani irin feeling takeji yana motsa zuciyarta,wanda tun tana qaryatawa har ta soma yarda tana jin wani abu a ran nata duk sanda ya ambaci sunan. Yafi mata dadi ya kirata DUNIYATA akan ya kirata my world.

Susutacciya ya maidata yadda ta fahimci ya soma maidata a wadannan kwanakin,lallai so yake sai ya matso komai a kansa dake cikin zuciyarta. Ta sani tabbas muddin zaici gaba da wannan salon......muddin zaici gaba da tafiyar da ita da wannan tsumammen yanayin to ba shakka zata gaza boye duk wani abu dake zuciyartata kuwa.......yana kuma dab da maidata mahaukaciya da gasken gaske,zata rasa duk wannan dauriyar tata da basarwa da takeyi.

D'aya bayan daya ya dinga zare hair pins din da dama shi ya zauna ya jera mata su,duk daya idan ya zare yana ware gashinta me tsaho baqi da santsi,wanda zuwa yanzun hair mist dinsu shi da ita ya zama guda daya,kaman yadda mayataccen mouth fresh dinsu ya zama products daya. Kusan komai nata cikin kwanakinnan ya canza mata zuwa kalar wanda yakeso,qamshinta,creams lip gloss da komai ma......komai kuma me tsada ne fiye da tunaninta,ranar data duba kudin perfume din daya sauya mata zaune kawai tayi tana binsa da kallo ba tare da yasan ma me ake ba. Su huda na wata duniyar duk da tayi imanin suna cikin kulawa......amma ita tana nan tana rayuwar da take ganin tafi qarfin matsayinta?.

Sai daya zare mata duk pins din,sannan ya kutsa yatsunsa cikin sumarta yana barbazata yadda yakeso,ta fahimci tana daya daga cikin abubuwan da suke matuqar burgeshi ga diya mace. Kaman yasan abinda yake saqawa muryarsa me kama data mashaya ta sauka a kunnenta

"I love it duniyata......kina da komai da nakeso..... Please ki sake bani dama na gina miki wasu dabi'u.......na dade ina kame kaina daga kallon Haram da kuma zina.......i only want my pure halal.......please ki qarasa mallakamin kanki da rayuwarki gaba daya I want the best from you,i want the best relationship with you" Ya qarashe maganar yana mata wata kyakkyawar runguma kafin ya fara maidata birkitacciya yana cireta daga ainihin tunani nutsuwa da saitinta. Batasan wanne abu daban yake buqata daga gareta ba.....batasan wanne best yake nema ba bayan duka fitar da ita daga tsarinta da yakeyi. Yana sakata jin wani irin nauyi da kunya da bata taba tsintar kanta a ciki ba.

Ko yanxun da qura ta lafa tana gaban madubi yana tsaye a bayanta yana bata dan kunnenta tana maidawa daya bayan daya,ya kafeta da idanu murmushi na fita daga kan fuskarsa qasa qasa. Idan yana kallon fuskarta a irin wannan yanayin sai komai ya dinga dawo masa. Idonsa ya lumshe yana jin zuciyarsa kaman zai fashe don tsananin cika da qaunarta da sukayi,yadda yakeji a duk sanda suka kasance da juna.....yasha imagination abun idan tana participating itama,yana kwadayin yaga wannan lokacin.

Taku uku ya qara ya hade tazarar dake tsakaninsu,ya dora fuskarsa saman kafadarta yana dubansu a tare shi da ita ta fuskar madubin.

"Idan Allah ya bamu 'ya'ya......wanne irin kyau xasuyi my world?". Wani kunya ya saukar mata,tayi qasa da kanta qaramin murmushi yana subuce mata. Shima murmushin ya saki,a duk sanda kunya haka ta bayyana saman fuskarta tana mata wani irin kebantaccen kyau na musamman.

"DUNIYATA.......Why aren't you responding?" Idanu ta daga alamun tambaya ba tare data yarda ta kalli tsakiyar idonsa ba. Ya fahimci haka,sai yasa yatsunsa yayi gefe da gashinta yana cusa bakinsa ta kunnenta abinda ya sanya tsigar jikinta tashi.

"On bed dear......" Ta fahimci inda ya dosa,don haka bata bari ya qarasa bama ta soma neman inda zata boye fuskarta. Ire iren rashin kunyarsa suna sakata jin wani irin nauyi ba kadan ba.

"Ko sai randa aka yanke shawarar ana sona ko ba'a sona?" Ya sassauta muryarsa yana fadi qasa qasa gami da riqe hannayenta da kyau qaramin murmushi yana subuce masa.

"I hope wannan ranan zata zo soon.......na matsu,ko akwai wani abu da ake buqatar nayi da za'a gayan I LOVE YOU MUHAMMAD FU'AD JADDA?....." Ya tambayeta da gasken gaske,har qasan zuciyarsa yana sha'awan jin ta fadi hakan. Kai ta girgiza tana basarwa,neman tserewa takeyi ya kuma fuskanceta,don haka ya sunkuceta kawai yana nufan stairs din da sukayi dakin qasa.

Idanu ta fitar waje,har ha Allah tsoron dakin qasan nan takeyi,yatsa ya saka ya lakuce mata hanci yana girgiza kai.

"Relax.....you're safe my world.....bazan taba yin wasa da DUNIYATA ba fa". Kasa ce masa komai tayi sai idanu data lumshe tana shaqar daddadan qamshinsa daya cika mata hanci,ta kwantar da kanta a qirjinsa tana jin bugun zuciyarsa. Batasan me yasa ko yaushe bugun zuciyarsa daban yake ba,wani bugu ne me sauri sauri wanda tasan qa'idan bugun baikai haka sauri ba. Idanunta saman dakin duke kallo,yadda ruwa yake gudu saman kansu tare da kifaye kala kala ba tare da ko damshin ruwa ko qwaya daya ya tabasu ba,ta dauke idanu tana tasbihi ga ubangijinta.

Saman lafiyayyen gadon dakin ya ajiyeta,ya dawo gabanta ya tsugunna yana zagaye hannuwansa da qugunta.

"Muhammad fuad jadda.......d'an alhj Muhammad ne,haifaffen bafulatanin mambila......,ta gefan mahaifiya kuma...." Sai ya danyi shuru yana hadiyar numfashi.

"Mariya da akafi sani da maamah itace mahaifiyata.....bafulatanar mayo belwa ganye local government" Hannuwanta ya riqe a tausashe cikin nasa zuciyarsa na karyewa.

"Lokaci na farko da zan bude bakina na fasawa wani dan adam daban rayuwata.....waye ni?....me naji me na fuskanta?.....sabrrrrrr.....abbana......abbana yana cikin jerin sahun mutumin da nafiso nafi qauna kaf cikin rayuwata.......saidai mun rasashi a sanda mukafi qaunarsa......mun rasashi a sanda mukafi buqatarsa......mun rasashi saboda wa'adinsa ya cika.....amma da taimakon maamah". Kai ta daga tana dubansa,tana ji yana tayar mata da wani mikin ciwo dake zuciyarta.

Kai ya gyada mata idanunsa suna sauya launi.

"Ta shayar dashi guba......ta dura masa miyagun maganganu da suka qarasa illata gangar jikinsa da zuciyarsa,suka Haifa masa da ciwon zuciya......kalmomin bakin maamah su suka jefa abba na a matsanancin ciwo......ciwon da haquri ya gadar dashi dashi,ya kuma ci gaba da tara masa guba na maganganun da suka zama silar fashewar zuciyarsa daga qarshe. Tun a gaban idanunsa muje ganin qasqanci da wulaqanci,ba wanda yake samun tausasawa ko kulawa daga gareta,daga shi mijinta harmu 'ya'yanta......bazan boye miki komai ba......bamusan dadin uwa ba,bamusan wani abu da ake kira dadi tsakanin mahaifiya da 'ya'yanta ba,mun rayu tamkar irin rayuwar da bawa zaiyi a hannun ubangidansa,walwala 'yanci da farinciki dukka yayi mana qaura,mun rayu tamkar agololi kuma 'ya'yan riqo......abbanmu kuma ya zama tamkar wani yaro gida bame gida ba......ba abinda tafi bawa mutunci da kima sama da KUDI sama da tayi KUDI sama da abbanmu dole ya zama me KUDI ya nemo KUDIn da zatayi kalar rayuwar da takeso,yayi lafiya ko kada yayi......ya rayu ko kada ya rayu,muyi lafiya tarbiyya ilimi mu tsaftatu mu qoshi duk basa cikin lissafinta,abinda ya dameta shine KUDI.....sabrrrrr..... Mun rayu cikin qasqantacciyar rayuwar da al'umma suka gaza janmu a jiki a garin da bamu da kowa,kowa yana ganin tunda wadda tayi silar zuwanmu duniya ta gaza tallafawa da tausayawa rayuwarmu,lallai mudin akwai wani abun aibu ne a tattare damu. Taji a rant ba zata iya rayuwa damu ba,ba zata iya zama damu bs,ta watsar damu da abba dake buqatarta saboda matsanancin ciwon zuciya dake sake kwantar dashi....duk inda abba bai qwallafa rai a soyayyarta ba,tayi nesa dashi shi yafi alkhairi,kunnuwansa xasu daina kwana su wayi gari da jin munanan kalmominta a kansa wanda hakan shizai bashi lafiya da wuri.....saidai kuma sonta ya zame masa jarrabin rayuwa,ya kasa haqura da nesanta kanta damu da tayi,ya sake zame masa silar hauhawar ciwonsa. Nayi kwasar kashi......nayi aikin bola da hannuwana duk don na kula da musaddiq da abbana......nayi sharar kasuwa nayi ta kwata har bansan iyakarsu ba kawai don na samo abinda xan kula da abbana da musaddiq.......munci abincin bola saboda gudun yunwa kada ta halakamu.......na kwana da GAWAr abbana.......na kwana da gawar mahaifiyar abbana JADDA saman cinyata dukkansu ba tare da nasan mutuwa sukayi ba ko bacci?,naci gaba da gadin gawarsu ba tare da nasan ya akewa gawa ba?,a shekarun da duka duka baifi a koreka daga bakin gawa ba idan kana da gata don kada kaga abinda shekarunka basukai ba. Jadda tazo mana da wani irin gata da muka dinga tunanin wahalarmj ta yanke......ta saida duk komai nata don tazo ta kula damu......ta bamu wani jin dadi wanda ko maamah da tayi silar zuwanmu duniyata tsahon shekarun da mukayi tare da ita bata taba bamu irinsa ba. Saidai sanda muke tsaka d wannan tunanin ashe ragowar kwanakinta na rayuwa yazo qararwa tare damu ajalinta yazo mata a kusa.....ta sake kwanciya ta barmu a wani irin yanayi. Daga sannan muka sake gane meye ma'anar rayuwa?,muna ta tunanin maamah zataji labarin komai......zataji tausayinmu ta dawo garemu amma inaaa......wanda yayi nisa bayajin kira........wata kalma da maqocinmu ya fada a kanta sanda ya dawo daga kudu yace mana ya ganta a can.......taqi barin raina da zuciyata.......har yanzu da ita nake kallonta.......bansan ranar da zata bar zuciyata ba.........maamah dinnan dai da daga qarshe naji duk duniya ba wani abu da nake qyamatar ya kusanci inda muke......itace silar mutuwar abba......ke daya kikasan wannan a duniya......na kamata har sau uku tana ciyar dashi da abubuwan da likita ya hanashi ci saboda suna tunzira ciwonsa.......suna kuma iya sanyawa komai ya faru dashi ciki harda rasa rayuwanshi......a dukk ukun nan dana kamata tayi alqawarin ba zata qara ba.....mantawa takeyi ne......na fahimci abinda ya sanyata take aikata haka ta hirarta da qawarta da har yanxun nake tunanin kamar matar nan harira da suke tare ne......so take ta kashe auren,so take abbanmu ya saketa shi kuma yaqi......tace tana buqatar tayi arziqo,tana buqatar freedom amma yaqi sallamarta....wannan shine dalilinta......shine kuma silar tunzurar ciwonsa har ya kaishi ga kushewarsa......ba ita ta kasheshi ba kenan sabrrrrr?" Yayi mata tambayar da wani irin yanayi daya tsorata sabreen qwarai da gaske.......yanayin da yake tabbatar mata wani abu ne guda daya da yake masa ciwo har yau har gobe a zuciyarsa......salon tambayar data tabbatar ya jima yana so ya yiwa wani dan adam ita......amma rashin jin kowa a matsayin na kusa da zuciyarsa sosai ya sanya ya gaza furtawa kowa,yadda yayi tambayar kaman hankalinsa na neman gushewa daga jikinsa sai ta kama kafadarsa da kyau tana riqewa kuka yana shirin qwace mata......tana jin ashe suna da yawa irinsu wadanda suka rayu cikin wulaqantacciyar rayuwa?......amma dashi dake da sauran uwa a raye........dasu da ba ko daya ga dangi masu tsananin jifa da zumunci waye yafi rashin sa'a.

"Sabrrrr" Ya rigata sakeyin magana duk da tana buqatar magana dashi.

"Idan kika gwada yimin abinda maamah ta yiwa abbana......nima mutuwa zanyi kaman abba.......saboda na fahimci zuciyata irin tashi ce......bamu iya soyayyar qarya ba,bamu iya soyayya da wasa ba,bamu iya yiwa masoyi qaramin riqo ba.......a halittarmu yake.......wannan ya sanya na tsani soyayya na kuma tsani kowacce 'ya Mace......anni ce mace qwaya daya data fara samun qauna irin ta uwa daga gareni bayan faruwar komai......amma hatta da amna bata samu komai daga gareni ba sai sanda naga tana shirin mutuwa ta barmu........bazan jure ba sabrrrrr idan kikace zaki gujeni......bazan iya dauka ba idan kika ce zaki barni sabrrrrr,da gaske nake nima mutuwa zanyi" Ya qarasa fada muryarsa da dukkanin jikinsa suna wani irin rawa,tabbacin ya tabo mikin da baida kamarsa a rayuwarsa.

Gaba daya sai ta rude,ta rasa yadda zatayi dashi,ga wani irin ciwo daya tayar mata wanda baida magani illa itama tabar hawayen idanunta su sauka ko xata rage abinda takeji tsakanin qirjinta zuwa zuciyarta.


*_DUNIYATA


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login