Showing 327001 words to 330000 words out of 363280 words

Chapter 110 - DUNIYATA BOOK 2 COMPLETE

HUGUMA   

11 Nov 2025

1451

duka ukun,kafin kuma a hankali su kece da kuka.
162



Hannun fu'ad ta riqe da kyau tana ji kaman ana matsa zuciyarta sanda sautin kukan nasu ya isa ga kunnuwanta. Jikinta duka ya dauki rawa,ta daga idanu tana kallon fu'ad. Qin kallonta yayi,kuma kaman ta fahimci yana sane yaqi kallon nata,sai kawai ta sadda kanta qasa tana sake jin yadda zuciyarta ke tsananin bugawa.

Cika mata kunne sosai kukan nasu yayi.

"Ya isa....kuyi shuru" Ta fadi tana jin ciwon yadda furucinta baya fita a sanda ta yishi,saidai kuma ga mamakinta sai almustapha ya fara rage sautin kukansa,a hankali dukkaninsu suka rage kukan kafin kuma suyi shuru. Mamaki taji ya kamata,ta sake xuba musu idanu wanda kaman sunsan da hakan sai hamza ya soma bude idanunsa. Tarwai qwayar idanunsa,kai ba zakace jariri bane dan sati biyu kacal,tana waiwayawa ga sauran suma duk idanunsu sun bude,kuma ita suke kallo.

Batasan me yasa ba ta samu qaramin murmushi ya subuce daga fuskarta,ta samu kanta da yunqurin miqa hannunta ta kamo hannun koda d'ayane a cikinsu.

Cikin wani irin ba zata da mamaki sai ga hannunta ya motsa,ta maida dubanta ga hannun,ta sake gwada dagashi xuwa gaba,ga tarin mamakinta sai hannunnata ya isa ga almustapha ta riqe yatsunsa hannun nata yana wani irin kakkarwa.

Wani abu da batasan meye ba ya soma ratsa zuciyarta,hawayen da batasan daga ina suke ba suka tsinke mata.

Wacce irin baiwa ko hukuncin Allah ne tattare da yaran?,abinda ta dinga maimaitawa kanta da nacewa da tambaya kenan idanunta akan fuskokinsu dukka su ukun. Sun zame mata waraka daga wani bangaren ciwon ta kenan?. Tambayar da tana ajiyeta fu'ad ya murza qofar ya shigo a hankali shidaya,don gaba daya sabreen ta gaza miqewa bare tayi jarumtar biyoshi,kawai zuciyarta tana gaya mata shikenan,shurunsu wani abun ne maras kyau ya samesu.

Hannun nata yabi da kallo yana mamaki shima wanda har yanxu yana cikin yatsun almustapha,ya qarasa gabanta ya tsugunna yana duban hannun yana kuma duban yaran.

"Hannunki ya motsa yau?" Ya tambayeta,saita gyada kai a hankali hawaye yana silmiyo mata daga idanunta. Qasa yayi da kansa yana tasbihi ga Allah,sun jima a haka sannan ya fiddo wayarsa.

"Ubangiji ya tabbatar da lafiya" Ya fadi a taqaice yana kiran sabreen zuciyarsa ta nauyaya da girman zatin Allah.

Tana kallo suna ficewa da yaran a dakin,sai ta samu kanta da gaza dauke idanunta a kansu har suka kammala ficewa. Tafi qarfin awanni uku bacci bai dauketa ba,tana jin kamar dakin nata ya koma kango bayan fitar tasu,kamar ba wani abu daya rage a dakin sai ita kadai.

Abun mamakin shine,kwana tayi tana mafarkin yaran,cikin mafarkanta na daren gaba daya sune kewaye da ita,harda wanda suke magana da ita,saidai ta kasa bambance me suke fadi.

Ajiyar zuciya kawai ta dinga saukewa sabreen din tana tariyo abinda fu'ad ya gaya mata na yadda ya shiga ya samu maamah din.

"Ya Allah.....ka jefa matsananciyar soyayyarsu a zuciyarta ninkin ba ninkin yadda ta tsani mahaifiyarsu" Ta samu kanta da wannan addu'ar.


*_NAMING CEREMONY_*


Katafaren kuma qawataccen guri ne na alfarma,aka aka shirya sannan aka tsarashi musamman saboda gabatar da radin sunan. Komai na gurin kusan fari ne,farin ma irin qal dinnan me daukan hankali da kuma daukan idanu. Tun daga farkon shiga gurin har zuwa ciki wasu irin manyan hotunan ne na jiraran design daban daban suke welcoming naka.

Kana shiga gurin zakasan guri ne bana wasa ba.....guri ne da akayi barin dukiya,irin barin da zai gaya maka ba'asan zafin kudin ba,don an nemesu a sanda ya dace an kuma tarasu.

Komai a tsare yake,don guri na musamman aka tanada saboda ajjiye yaran. Kowa xai qarasa ya gansu,me buqatar basu gift ko wani abu makamancin hakan amna da huda suna kusa,don sune iyayen yaran gaba daya.

Cikin tsari aka soma gudanar da taron,sabreena maman yaran wadda ta koma hajiya sabreen,tayi wani irin razanannen kyau cikin wani dan banzan lace da aka warewa milliyoyin kudi aka bada order saqashi a india. Ba iya lace din jikinta kawai ba......hatta da lace da atamfofi da manyan luxury warmers da aka raba a gurin duka container guda akayi musu.

Tun kana lissafa adadin kayan ciye ciye da shaye shaye da aka tanada a wajen zaka gaji ne kawai,don kuwa tsarin serve yourself kawai akayi,debi da kanka,kaje ka zaba ka zuba koka aika a debo maka,ko ka kira daya daga cikin ma'aikatan dake wajen ka bashi order din abinda kake da buqatar ci.

Guri na musamman aka tanadarwa jama'ar DUNIYATA,don a idanun sabreen mutane ne masu kima mutunci da daraja,wadanda suka taimaka qwarai wajen bawa dangantaka dama soyayyarsu gudunmawa.

A gurinne fannah ta gabatar da kyautar da BB ya yiwa takwaranshi,wato kyautar sabon company dinsa na sarrafa auduga da fiddashi qasashen waje.....daukan nauyin duka wani abu da ya shafi rayuwarsa,tun daga karatu lafiya sutura da sauransu,yace kawai abbanshi ya zuba masa idanu,don shi aka haifawa umar din. Bama umar duka ba.....dukkanninsu yana jinsu a zuciyarsa,saidai yace bazaiyi qarya ba umar din na dabanne a wajensa.

Abba baiyi qasa a gwiwa ba shima ya aiko da nashi saqon ta hannun amna,estate guda ne me dauke da gidaje dari ya mallakawa nasa takwaran. Ihu aka dinga yi a wajen,saboda yadda abun ya qawatar da mahalatta taron,wato dai gasa ce ta gasken gaske tsakanin kowa da takwaranshi. A sannan fu'ad din yana daga can gidan hutawarsa,yana kallon yadda taron yake gudana kamar a gabanshi,ta hanyar cameras da ya saka aka zuba sosai a wajen,aka kuma miqa ragamar monitoring dinsu a hannun qwararrun security dinsa. Saidai duk da haka yaji yana sha'awar zama,yayita kallon duniyarsa da yanzun ta rarrabu da wasu hadakar qananun duniyoyin har guda uku.

Murmushi ya saki yana gyada kai,shi za'a yiwa wariyar launin fata kenan a ware masa abbansa?,kawai sai ya dauki waya ya kira musaddiq da nashi saqon.

Sanda musaddiq ke sanar da bada kyautar JADDA WINGS ga almustapha kusan kowa sai da yaji shock,kafin daga bisani gurin ya kaure da tafi.

"Sannan nima ina gabatar da tawa qaramar kyautar motar" Ya fadi yana fiddo maqullin motar daga aljihunsa ya dagashi sama ya kuma isa gaban abban nashi almustapha ya ajiye. Motace me bala'in tsada new model,wadda har yanzun ko cikin masu kudi ba kowa bane ya samu nasarar mallakarta ba. Tabbas abban abba ne,kusan yafi kowa a cikinsu tashi da gwaggwabar kyauta.

Kafin abar gurin fu'ad ya sanya qaramar musabaqa ga yara masu haddan qur'ani a wajen,daga shekara goma sha biyu zuwa qasa,koda izu uku ke gareka kuwa. An gwabza musabaqa me kyau,abinda ya sake janye hankalin sabreen taji a duniya bata da burin daya wuce yaran nata su zama mahaddatan alqur'ani.

Sai da aka kammala komai sannan anni itama ta gabatar da nata kyautan. Motoci ne masu kyan gaske guda uku iri daya sak,dukkaninsu farare qal,amna kuwa wani babban box ne da ba wanda yasan ainihin meye a ciki. Fannah ma ba'a barta a baya ba,itama da nata gift din,haka dai kusan duk wanda yazo wajen da nasa alkhairin da zai gabatar,

Muhammad fu'ad jadda ba qashin yarwa bane,komai arziqinka komai kuma babunka ba zaka taba cewa baka amfana dashi da komai ba,wannan ya saya ma yaranshi dama matarsa wata irin soyayya da qauna.

Taro ya tashi lafiya,yara kuma sun tabbatar da sunayensu na ALMUSTAPHA MUHAMMAD JADDA(FAWAD). HAMZA MUHAMMAD JADDA(FAUZAN). da babban aboki amini kuma dan uwa UMAR MUHAMMAD JADDA(FAWWAZ). Yaran sunzo da wani irin yanayi a dangi gaba daya,yan uwa dama wadanda ba 'yan uwa ba kowa ya tafi da fawwaz fauzan da fawad a bakinsa.

Kusan gaban idanunshi aka gama komai,koda ya dawo gidan wajen sha biyun dare yayi mamakin haurowarta samanshi batayi bacci ba.

Daga qofa ta tsaya ta langabe kafada,ya saki murmushi yana cewa.

"Qaraso ciki........kinsa yau duka kishi ya kamani......na kasa sukuni sam". Ido ta zaro,ya sakata sakin murmushin da bata shirya ba.

"Hamma.....kishin me?,duka mata ne fa a wajen,yaran dake wajen under age ne fa?". Idonsa ya lumshe yana duban dukiyar fulaninta da suka tutturo kaman suna tsokanarshi ne ma,lafiyayyar farar fatarta dake samun kulawa tana sake qawata su,uwa uba kuma yanayin rigar da tayi amfani da ita V neck ne da aka shimfidawa lace.

Wani abu ya hadiye a maqoshinsa kawai ya miqa mata hannu,tana mamakin maganarsa ne,don haka sam bata lura da mayataccen kallon da yake watsa mata ba.

Tanata masa surutu na labarin taron suna,har sai da yayi mata wata kyakkyawar runguma sannan hankalinta ya dawo jikinta,dif surutun ya dauke,shuru ya wanzu a dakin,sai sautin bugawar zuciyoyinsu. Duk wani gaba ta jikinsa sai data amsa,ya sake cusa hancinsa cikin jikinta yana jin qamshinta yana birkitashi.

"Sati uku adda na......sati uku da haihuwan su fauxan right?" Kai ta gyada masa,sai shima ya jinjina kansa yana dan zame jikinsa kadan daga nata.

"Naga kaman kinyi sallah daxun da asuba ko?". Qirjinta ya buga tsoro ya saukar mata.

"Hamma.....nayi sallah......amma fa three weeks....." Yadda ya zuba mata jajayen idanunshi ya hanata qarasa magana,ta maida abinda takeson cewa.
163


"Yayi wuri?,nasan haka zakice.....amma bakisan me nakeji bane sabrrrr".

" I know hamma......na sani,ba wani motsinka da zan kasa gane manufarsa.......I will always be ready to accept you.....amma yanzu hamma,dr tace ina buqatar time kafin wannan abun,yana da kyau nayi healing sosai". Zame jikinsa yayi yana lumshe idanunsa ya koma wata kujerar daban ya zauna yana dafe goshinsa. Tausayinsa taji ya kamata,ta tako a hankali zuwa gabansa ta tsugunna tana dora hannuwanta saman cinyarsa.

"May I help you?.bette" Idanunsa da suka sauya launi ya bude a hankali yana kallonta,saita sake gyara tsugunonta

"I will help you to feel better" Idanunsa ya ware a kanta yana dafe hannuwanta.

"No.....ba abinda hakan zai qara bazai magani ba.....komai zai iya faruwa don qishirwa kawai zaki qaramin......dawo nan ki zauna muyi hira" Abinda yace kenan da ita yana ture mata pillows din da suke gefanta.

Hirar kuwa tayi masa sosai,ta dinga bashi labaran abinda ya faru a wajen. Tun yana tsume har ya ware,ya soma dariyan abubuwan da take bashi labarin,qarshe dai a nan suka bingire yana rungume da ita,basu tashi farkawa ba saida kiran wayar tashin triplet ya farkar dasu.

&Sannu a hankali kwanaki suka dinga tafiya,abubuwa da yawa sun lafa kuma sunyi sanyi,kaman darajar haihuwan yaran yazo musu da abubuwa ne masu yawa.

Amna da fannah harma da huda dukkaninsu goyon ciki sukeyi,amma hakan bai rage musu kwadayi ko sha'awar yaran ba. Babu wanda ke iya kwana biyu cikakke ba tare daya kira yaji lafiyar yaran ba. Farouq kuwa da aka jarabceshi da son takwararsa gidan ya zame masa kaman hanyar wucewa,sai aiki yayi mugun cude masa yake kwana uku bai shigo gidan yaga yaran nashi ba,ya kuma kebe takwaransa sunyi ganawa ta daban da sauran.

Ta bangaren maamah kuwa.....tun ranar daya kai mata yaran suka kasa bacewa daga idanu da kunnenta. Cikin awanni ashirin da hudu na yininta kowanne awa bata rufewa ba tare data tunasu ba. Sannu sannu sai takejin kamar tanason ta sake ganin yaran,kaman tana kewarsu,idan tana dakin bata da aiki sai kallon muhallin da ya kwantar dasu a waccan ranar. Wani abu takejin kamar yana shirin kamata me kama da hauka hauka akan yaran,tana yawan jin irin kukan da sukayi a waccar ranar,tana yawan jin muryoyinsu kaman suna wajen.

Daga qarshe dai ta fahimci son ganinsu takeyi,saita ta rasa kuma yadda zata fahimtar dasu saratu tanason ta sake ganin yaran,don iyasu kadai kawai takeson gani banda mahaifiyar tasu.

A hankali sabreen din cikin salo da hikima ta soma gyaran jikinta ta hannun dattijuwar matar nan da tasan jiya tasan yau kuma har gobe ake tafiya da ita wato Bgawos kitchen and aphrodisiac. Ingantattun kayan gyara natural na matan da suka jima a duniya kusan shekaru hamsin.08127084190/08104553105(tasan sirrin gyara sosai,gyara irin na dauri na tsaffin mata bana zamani ba,bana gama garin masu magungunan matan yanzu ba,bama gyaran kadai ba,hadda duk wani nau'in abinciccika,na biki ne suna taron sauka walima da sauransu,ko kuma kawai akwai ranar da zaki tashi bakya sha'awar shiga kitchen?,kinaso kuma abincin gidan ki ya zama ready a tsaftace kaman ke kika shiga kitchen din kikayi da kanki?,karki tsallake wannan).

A jikinta kawai taji canji me matuqar yawa,ta sake jinta tana sake kintsuwa tako ina. Har ta soma gyaran jiki ta watsar,don ta tsorata sosai ranar da fu'ad ya rutsata,da qyar tasha,amma daga qarshe ya gaya mata yana lissafe da satittikan da suka rage.

Tunani ta shiga sosai na yadda zata kubce masa,tanaso ta sake warkewa sosai,uwa uba kuma sunyi hira da fannah,har suka gangaro kan tsarin iyali.

"Muddin period dinki ya dawo to duk sanda kuka kasance tare xaki iya daukan wani cikin" Idanu sabreen ta waro waje.

"Ciki fannah......" Ta danyi dariya.

"Satinsu fauzan nawa?" Dariya fannah tayi.

"Shi ba ruwansa da satin yaranki nawa......indai har period ya dawo daidai shikenan magana ya qare"

"Fannan BB...." Sabreen ta fada tana cin serious.

"Adda sabreen" Ta amsa mata tana dariya qasa qasa.

"Kibar zancan nan tukunna......me zaki bani na gyara tsarabar bare bari" Gyara zama fannah tayi.

"Kamar kuwa kinsan mu bare bari ba wasa bane" Sai suka saki dariya a tare.

"Bari na gutsira miki kadan.....ki samu 'ya'yan habbatussauda da dabino ki dinga ki tsaga dabinon ki cire qwallon ki zuba yayan habba din ki dinga taunawa kullum safe da dare". Da daya da daya ta dinga bata sirrikan da na barebari ne,ita kanta ta qaru ta kuma sallama (sai damu wallahi=??>?q?).

A tsorace take har zuwa sanda suka cika sati shida,ganin sun tsallake ranar baice mata komai ba,don washegari qaramar tafiya ta kamashi zuwa branch dinsa na lagos,don haka kawai tayi amfanin da wannan damar ta tayar da yawon arba'in.

Dabara tayi,ta kira anni tace mata tana son zuwa din,amma bata samu hamman ba,tunda tasan wani lokaci idan tafiya me muhimmanci wadda take ta gaggawa irin haka ta taso masa yakan saka layinsa a flight mode ne

"Yana da kyau ai,ko don a sake ganin 'yan uwa,zan gaya masa da kaina" .

Hankali kwance tahau shirinta,so samu ma ta wuce mali wajen mommanta,to amma mali din tasan tayi nisa ta tsallake zuwa can,don haka kawai saita shirya zuwa abuja gidan yayan ummeenta da bai jima da dawowa Nigeria ba,ta shirya su fauzan duka da masu aikinta,ta siya musu ticket suka wuce abinsu.

Sanda anni ta gaya masa harda 'yar mitarsa,yana tunanin cikin kano ne zasuyi ziyaransu gidan kawu rufai da gidansu da sauran wajen 'yan uwa su dawo gida su kwana.

"Anni kina ganin ba zata debowa yaran nan iska ba?,40 days fa kawai sukayi,nima kwana uku kawai zanyi fa na dawo,meye na fitan?" Ya kasa boyewa sai daya furta.

"Banda abinka fu'ad ai sada zumunci ne,kuma a al'ada ai dama ana yin wannan zagayen,kaman ba gajiya ne da kuma nunawa dangi lafiya kuke ne" Shuru ya danyi,dondai anni ce,yana kuma kunyar jayayya da ita.

"Shikenan,Allah ya kiyaye hanya"

"Ameen ameen" Anni ta amsashi suka dan sake tattaunawa sannan suka shiga wani maganan na daban.

_Yawon arba'in ko?....hmmmm=??=??......._

_get ready muna pages din qarshe ne fa in sha Allah_>?p?>?p?>?p?


&Kwanansa uku a lagos,kwanan sabreen biyu a Abuja ya dawo kano. Har ya iso gidan baiyi wani tunanin abuja ta tafi ba,sai bayan ya shigo ne yadda gidan yayi masa shuru da yawa ya sakashi ya fara kokwanto. Tun a parlor na biyu ya soma da duba kitchen. Ba alamun dazu ko jiya anyi amfani dashi,kai tsaye kawai ya wuce bedroom dinta.

Yadda yaga komai a killace ya bashi amsar cewa ba mutum a


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login